< Joel 1 >

1 The word of the Lord which came to Joel the son of Bathuel.
Maganar Ubangiji wadda ta zo wurin Yowel ɗan Fetuwel.
2 Hear these [words], you elders, and listen all you that inhabit the land. Have such things happen in your days, or in the days of your fathers?
Ku ji wannan, ku dattawa, ku kasa kunne, dukan waɗanda suke zaune a ƙasar. Ko wani abu makamancin haka ya taɓa faruwa a kwanakinku ko a kwanakin kakanninku?
3 Tell your children concerning them, and [let] your children [tell] their children, and their children another generation.
Ku faɗa wa’ya’yanku, bari kuma’ya’yanku su faɗa wa’ya’yansu,’ya’yansu kuma su faɗa wa tsara ta gaba.
4 The leavings of the caterpillar has the locust eaten, and the leavings of the locust has the palmerworm eaten, and the leavings of the palmerworm has the cankerworm eaten.
Abin da ɗango ya bari fāri masu girma sun cinye; abin da fāri masu girma suka bari, burduduwa ta cinye; abin da burduduwa ta bari sauran kwari sun cinye.
5 Awake, you drunkards, from your wine, and weep: mourn, all you that drink wine to drunkenness: for joy and gladness and removed are from your mouth.
Ku farka, ku bugaggu, ku yi kuka! Ku yi kuka da ƙarfi, ku dukan mashayan ruwan inabi; ku yi kuka mai ƙarfi saboda sabon ruwan inabi, gama an riga an ƙwace ta daga leɓunanku.
6 For a strong and innumerable nation is come up against my land, their teeth are lion's teeth, and their back teeth those of a [lion's] whelp.
Wata al’umma ta mamaye ƙasata, tana da ƙarfi ba ta kuma ƙidayuwa; tana da haƙoran zaki, da zagar zakanya.
7 He has ruined my vine, and utterly broken my fig-trees: he has utterly searched [my vine], and cast it down; he has peeled its branches.
Ta mayar da kuringar inabina kango ta kuma lalatar da itatuwan ɓaurena. Ta ɓamɓare bayansu duka ta kuma jefar da su ta bar rassansu fari fat.
8 Lament to me more than a virgin girded with sackcloth for the husband of her youth.
Ku yi makoki kamar budurwa a cikin tsummoki tana baƙin ciki domin mijinta na ƙuruciyarta.
9 The meat-offering and drink-offering are removed from the house of the Lord: mourn, you priests that serve at the altar of the Lord.
Hadayun hatsi da hadayun sha an yanke su daga gidan Ubangiji. Firistoci suna makoki, su waɗanda suke yi wa Ubangiji hidima.
10 For the plains languish: let the land mourn, for the corn languishes; the wine is dried up, the oil becomes scarce;
Filaye sun zama marasa amfani, ƙasa ta bushe; an lalatar da hatsi, sabon ruwan inabin ya bushe, mai kuma ba amfani.
11 the husbandmen are consumed: mourn your property on account of the wheat and barley; for the harvest has perished from off the field.
Ku fid da zuciya, ku manoma, ku yi ihu, ku masu noma inabi; ku yi baƙin ciki saboda alkama da sha’ir, saboda an lalata girbin filaye.
12 The vine is dried up, and the fig-trees are become few; the pomegranate, and palm tree, and apple, and all trees of the field are dried up: for the sons of men have have abolished joy.
Kuringar inabin ta bushe itacen ɓaure kuma ya yi yaushi,’ya’yan rumman, itacen dabino da itacen gawasa, dukan itatuwan filaye, sun bushe. Tabbatacce farin cikin’yan adam ya bushe.
13 Gird yourselves [with sackcloth], and lament, you priests: mourn, you that serve at the altar: go in, sleep in sackcloths, you that minister to God: for the meat-offering and drink-offering are withheld from the house of your God.
Ku sa tsummoki, ya firistoci, ku yi makoki; ku yi ihu, ku da kuke yin hidima a gaban bagade. Zo, ku kwana saye da tsummoki, ku waɗanda kuke yi wa Allahna hidima, gama an yanke hadayun hatsi da hadayun sha daga gidan Allahnku.
14 Sanctify a fast, proclaim a [solemn] service, gather the elders [and] all the inhabitants of the land into the house of your God, and cry earnestly to the Lord,
Ku yi shelar azumi mai tsarki; ku kira tsarkakan taro. Ku kira dattawa da kuma dukan mazaunan ƙasar zuwa gidan Ubangiji Allahnku, ku kuma yi kuka ga Ubangiji.
15 Alas, Alas, Alas for the day! for the day of the Lord is near, and it will come as trouble upon trouble.
Kaito saboda wannan rana! Gama ranar Ubangiji ta kusa, za tă zo kamar hallaka daga wurin Maɗaukaki.
16 [Your] meat has been destroyed before your eyes, joy and gladness from out of the house of your God.
Ba a yanke abinci a idanunmu, farin ciki da kuma murna daga gidan Allahnmu ba?
17 The heifers have started at their mangers, the treasures are abolished, the wine presses are broken down; for the corn is withered.
Iri suna ta yanƙwanewa a busasshiyar ƙasa Ɗakunan ajiya sun lalace, an rurrushe rumbunan hatsin, gama hatsi ya ƙare.
18 What shall we store up for ourselves? the herds of cattle have mourned, because they had no pasture; and the flocks of sheep have been utterly destroyed.
Ji yadda dabbobi suke nishi! Garkunan shanu sun ruɗe saboda ba su da ciyawa, har garkunan tumaki ma suna shan wahala.
19 To you, O Lord, will I cry: for fire has devoured the fair places of the wilderness, and a flame has burnt up all the trees of the field.
A gare ka, ya Ubangiji, nake kira, gama wuta ta cinye wurin kiwo harshen wuta kuma ya ƙone dukan itatuwan jeji.
20 And the cattle of the field have looked up to you: for the fountains of waters have been dried up, and fire has devoured the fair places of the wilderness.
Har ma namun jeji suna haki gare ka; rafuffuka sun bushe wuta kuma ta cinye wurin kiwo a jeji.

< Joel 1 >