< Job 19 >

1 Then Job answered and said,
Sai Ayuba ya amsa,
2 How long will you vex my soul, and destroy me with words? only know that the Lord has dealt with me thus.
“Har yaushe za ku yi ta ba ni azaba ku kuma murƙushe ni da maganganunku?
3 You speak against me; you do not feel for me, but bear hard upon me.
Yanzu sau goma ke nan kuna wulaƙanta ni, kuna kai mini hari na rashin kunya.
4 Yes verily, I have erred in truth, (but the error abides with myself) in having spoken words which it was not right [to speak]; and my words err, and are unreasonable.
In gaskiya ne na yi laifi, kuskurena ya rage nawa.
5 But alas! for you magnify yourselves against me, and insult me with reproach.
In kuwa za ku ɗaukaka kanku a kaina kuna ɗauka wahalar da nake sha domin na yi laifi ne,
6 Know then that it is the Lord that has troubled [me], and has raised his bulwark against me.
sai ku san cewa Allah ya yi mini ba daidai ba ya kewaye ni da ragarsa.
7 Behold, I laugh at reproach; I will not speak: [or] I will cry out, but [there is] nowhere judgment.
“Ko da yake na yi kuka cewa, ‘An yi mini ba daidai ba!’ Ba a amsa mini ba; ko da yake na nemi taimako, ba a yi adalci ba.
8 I am fenced round about, and can by no means escape: he has set darkness before my face.
Ya tare mini hanya yadda ba zan iya wucewa ba; ya rufe hanyata da duhu.
9 And he has stripped me of my glory, and has taken the crown from my head.
Ya cire darajar da nake da ita, ya kuma cire rawani daga kaina.
10 He has torn me around about, and I am gone: and he has cut off my hope like a tree.
Ya yi kaca-kaca da ni har sai da na ƙare; ya tuge begen da nake da shi kamar itace.
11 And he has dreadfully handled me in anger, and has counted me for an enemy.
Yana jin haushina ya lissafta ni cikin maƙiyansa.
12 His troops also came upon me with one accord, liars in wait compassed my ways.
Rundunarsa ta zo da ƙarfi; suka kafa sansani kewaye da ni, suka zagaye tentina.
13 My brethren have stood aloof from me; they have recognized strangers [rather] than me: and my friends have become pitiless.
“Ya raba ni da’yan’uwana maza; abokaina sun zama baƙi gare ni.
14 My nearest of kin have not acknowledged me, and they that knew my name, have forgotten me.
Dangina sun tafi; abokaina na kurkusa sun manta da ni.
15 [As for] my household, and my maidservants, I was a stranger before them.
Waɗanda sukan ziyarce ni, da masu yi mini aiki mata sun ɗauke ni baƙo.
16 I called my servant, and he listened not; and my mouth entreated [him].
Na kira bawana, amma bai amsa ba, ko da yake na roƙe shi da bakina.
17 And I implored my wife, and earnestly entreated the sons of my concubines.
Numfashina yana ɓata wa matata rai;’yan’uwana sun ƙi ni.
18 But they rejected me for ever; whenever I rise up, they speak against me.
Har’yan yara suna rena ni; in sun gan ni sai su fara yi mini riyar reni.
19 They that saw me abhorred me: the very persons whom I had loved, rose up against me.
Duk abokaina sun yashe ni; waɗanda nake ƙauna sun zama ba sa ƙaunata.
20 My flesh is corrupt under my skin, and my bones are held in [my] teeth.
Ni ba kome ba ne sai dai fata da ƙashi, da ƙyar na tsira.
21 Pity me, pity me, O friends; for it is the hand of the Lord that has touched me.
“Ku tausaya mini, abokaina, ku ji tausayina, gama hannun Allah ya sauko a kaina.
22 Therefore do you persecute me as also the Lord [does], and are not satisfied with my flesh?
Don me kuke fafarata kamar yadda Allah yake yi? Ba ku gaji da yagar fatata ba?
23 For oh that my words were written, and that they were recorded in a book forever,
“Kash, da ma a ce ana rubuta maganganuna, da an rubuta su a littafi,
24 with an iron pen and lead, or graven in the rocks!
a rubuta su da ƙarfe a kan dutse don su dawwama har abada!
25 For I know that he is eternal who is about to deliver me,
Na san wanda zai fanshe ni yana nan da rai, kuma a ƙarshe zai tsaya a kan duniya.
26 [and] to raise up upon the earth my skin that endures these [sufferings]: for these things have been accomplished to me of the Lord;
Kuma bayan an hallaka fatata, duk da haka a cikin jiki zan ga Allah.
27 which I am conscious of in myself, which mine eye has seen, and not another, but all have been fulfilled to me in [my] bosom.
Zan gan shi da kaina da idanuna, Ni, ba wani ba ne. Zuciyata ta cika da wannan tunani!
28 But if you shall also say, What shall we say before him, and [so] find the root of the matter in him?
“In kuka ce, ‘Za ku ci gaba da matsa mini, tun da shi ne tushen damuwa,’
29 Do you also beware of deceit: for wrath will come upon transgressors; and then shall they know where their substance is.
sai ku ma ku ji tsoron takobin; gama fushi yakan kawo hukunci ta wurin takobi, sa’an nan za ku san cewa akwai shari’a.”

< Job 19 >