< Job 17 >

1 I perish, carried away by the wind, and I seek for burial, and obtain [it] not.
Na karaya, kwanakina sun kusa ƙarewa, kabari yana jirana.
2 Weary I entreat; and what have I done? and strangers have stolen my goods.
Ba shakka masu yi mini ba’a suna kewaye da ni; idanuna suna ganin tsokanar da suke yi mini.
3 Who is this? let him join hands with me.
“Ya Allah, ka ba ni abin da ka yi mini alkawari. Wane ne zai kāre ni?
4 For you have hid their heart from wisdom; therefore you shall not exalt them.
Ka rufe zuciyarsu yadda ba za su iya ganewa ba, saboda haka ba za ka bari su yi nasara ba.
5 He shall promise mischief to [his] companions: but [their] eyes have failed for [their] children.
In mutum ya juya wa abokansa baya don a ba shi wata lada’ya’yansa za su makance.
6 But you has made me a byword amount the nations, and I am become a scorn to them.
“Allah ya sa na zama abin da kowa yake magana a kai wanda kowa yake tofa wa miyau a fuska.
7 For my eyes are dimmed through pain; I have been grievously beset by all.
Idanuna ba sa gani sosai don baƙin ciki; jikina ya zama kamar inuwa kawai
8 Wonder has seized true men upon this; and let the just rise up against the transgressor.
Mutanen da suke masu adalci wannan abu ya ba su tsoro; marasa laifi sun tayar wa marasa tsoron Allah.
9 But let the faithful hold on his own way, and let him that is pure of hands take courage.
Duk da haka, masu adalci za su ci gaba da tafiya a kan hanyarsu, waɗanda hannuwansu suke da tsabta kuma za su ƙara ƙarfi.
10 Howbeit, do you all strengthen [yourselves] and come now, for I do not find truth in you.
“Amma ku zo dukanku, ku sāke gwadawa! Ba zan sami mutum ɗaya mai hikima ba a cikinku.
11 My days have passed in groaning, and my heart-strings are broken.
Kwanakina sun wuce, shirye-shiryena sun ɓaci haka kuma abubuwan da zuciyata take so.
12 I have turned the night into day: the light is short because of darkness.
Mutanen nan sun juya rana ta zama dare. A tsakiyar duhu suka ce, ‘Haske yana kusa.’
13 For if I remain, Hades is my habitation: and my bed has been made in darkness. (Sheol h7585)
In kabari ne begen da nake da shi kaɗai, in na shimfiɗa gadona a cikin duhu, (Sheol h7585)
14 I have called upon death to be my father, and corruption [to be] my mother and sister.
In na ce wa kabari, ‘Kai ne mahaifina,’ tsutsa kuma ke ce, ‘Mahaifiyata’ ko ‘’yar’uwata,’
15 Where then is yet my hope? or [where] shall I see my good?
To, ina begena yake? Wane ne zai iya ganin wani bege domina?
16 Will they go down with me to Hades, or shall we go down together to the tomb? (Sheol h7585)
Ko begena zai tafi tare da ni zuwa kabari ne? Ko tare za a bizne mu cikin ƙura?” (Sheol h7585)

< Job 17 >