< Jeremias 1 >

1 The word of God which came to Jeremias the [son] of Chelcias, of the priests, who lived in Anathoth in the land of Benjamin:
Kalmomin Irmiya ɗan Hilkiya, ɗaya daga cikin firistoci a Anatot a yankin Benyamin.
2 [accordingly] as the word of God came to him in the days of Josias son of Amos king of Juda, in the thirteenth year of his reign.
Maganar Ubangiji ta zo gare shi a shekara ta goma sha uku ta sarautar Yosiya ɗan Amon sarkin Yahuda,
3 And it was in the days of Joakim, son of Josias king of Juda, until the eleventh year of Sedekias king of Juda, [even] until the captivity of Jerusalem in the fifth month.
da kuma a zamanin Yehohiyakim ɗan Yosiya sarkin Yahuda, har zuwa watan biyar na shekara goma sha ɗaya na Zedekiya ɗan Yosiya sarkin Yahuda, sa’ad da aka kai mutanen Urushalima zaman bauta.
4 And the word of the Lord came to him, [saying],
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
5 Before I formed you in the belly, I knew you; and before you came forth from the womb, I sanctified you; I appointed you a prophet to the nations.
“Kafin in siffanta ka a cikin ciki na san ka, kafin a haife ka, na keɓe ka; na naɗa ka ka zama annabi ga al’ummai.”
6 And I said, O Lord, you that are supreme Lord, behold, I know not [how] to speak, for I am a child.
Sai na ce, “Kayya, Ubangiji Mai Iko Duka, ban iya magana ba; ni ɗan yaro ne kawai.”
7 And the Lord said to me, Say not, I am a child: for you shall go to all to whoever I shall send you, and according to all [the words] that I shall command you, you shall speak.
Amma Ubangiji ya ce mini, “Kada ka ce, ‘Ni ɗan yaro ne kawai.’ Dole ka je wurin kowane mutumin da na aike ka ka kuma faɗa abin da na umarce ka.
8 Be not afraid before them: for I am with you to deliver you, says the Lord.
Kada ka ji tsoronsu, gama ina tare da kai kuma zan kiyaye ka,” in ji Ubangiji.
9 And the Lord stretched forth his hand to me, and touched my mouth: and the Lord said to me, Behold, I have put my words into your mouth.
Sai Ubangiji ya miƙa hannunsa ya taɓa bakina ya ce mini, “Yanzu na sa kalmomina a bakinka.
10 Behold, I have appointed you this day over nations and over kingdoms, to root out, and to pull down, and to destroy, and to rebuild, and to plant.
Duba, yau na naɗa ka a kan al’ummai da mulkoki don ka tumɓuke ka kuma rusar, ka hallaka ka kuma kakkaɓe, ka gina ka kuma shuka.”
11 And the word of the Lord came to me, saying, What see you? And I said, A rod of an almond tree.
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa, “Me ka gani, Irmiya?” Sai na amsa na ce, “Na ga reshen itacen almon.”
12 And the Lord said to me, You have well seen: for I have watched over my words to perform them.
Ubangiji ya ce mini, “Daidai ne ka gani, gama ina lura in ga cewa maganata ta cika.”
13 And the word of the Lord came to me a second time, saying, What see you? And I said, A caldron on the fire; and the face of it is toward the north.
Maganar Ubangiji ta sāke zo mini cewa, “Me ka gani?” Na amsa na ce, “Na ga tukunya tana tafasa, tana juyewa daga arewa.”
14 And the Lord said to me, From the north shall flame forth evils upon all the inhabitants of the land.
Ubangiji ya ce mini, “Daga arewa za a zubo masifa a kan dukan mazaunan ƙasar.
15 For, behold, I call together all the kingdoms of the earth from the north, says the Lord; and they shall come, and shall set each one his throne at the entrance of the gates of Jerusalem, and against all the walls round about her, and against all the cities of Juda.
Ina shirin kiran dukan mutanen masarautar arewanci,” in ji Ubangiji. “Sarakunansu za su zo su kafa kursiyoyinsu a mashigin ƙofofin Urushalima; za su zo su kewaye dukan katangarta su kewaye dukan garuruwan Yahuda.
16 And I will speak to them in judgment, concerning all their iniquity, [forasmuch] as they have forsaken me, and sacrificed to strange gods, and worshipped the works of their own hands.
Zan furta hukunci a kan mutanena saboda muguntarsu na yashe ni, suna ƙona turare ga waɗansu alloli suna kuma bauta wa abin da hannuwansu suka yi.
17 And do you gird up your loins, and stand up, and speak all [the words] that I shall command you: be not afraid of their face, neither be you alarmed before them; for I am with you to deliver you, says the Lord.
“Ka kintsa kanka! Ka tashi tsaye ka faɗa musu abin da na umarce ka. Kada su firgita ka, in ba haka ba zan firgita ka a gabansu.
18 Behold, I have made you this day as a strong city, and as a brazen wall, strong [against] all the kings of Juda, and the princes thereof, and the people of the land.
Yau na mai da kai birni mai katanga, ginshiƙin ƙarfe da bangon tagulla don ka tsaya gāba da dukan ƙasar, ya kuma yi gāba da sarakunan Yahuda da fadawan, da firistoci da kuma mutanenta.
19 And they shall fight against you; but they shall by no means prevail against you; because I am with you, to deliver you, says the Lord.
Za su yi yaƙi da kai amma ba za su ci nasara a kanka ba, gama ina tare da kai, zan kuma kiyaye ka,” in ji Ubangiji.

< Jeremias 1 >