< Esias 8 >

1 And the Lord said to me, Take to yourself a volume of a great new [book], and write in it with a man's pen concerning the making a rapid plunder of spoils; for it is near at hand.
Ubangiji ya ce mini, “Ka ɗauki naɗaɗɗen littafi mai girma ka yi rubutu a kai da alƙalami kurum, Maher-Shalal-Hash-Baz.
2 And make me witnesses [of] faithful men, Urias, and Zacharias the son of Barachias.
Zan kuma kira Uriya firist da Zakariya ɗan Yeberekiya su zama mini amintattun shaidu.”
3 And I went in to the prophetess; and she conceived, and bore a son. And the Lord said to me, Call his name, Spoil quickly, plunder speedily.
Sa’an nan na tafi na yi jima’i da annabiya, ta kuwa yi ciki ta haifi ɗa. Ubangiji kuma ya ce mini, “Raɗa masa suna, Maher-Shalal-Hash-Baz.
4 For before the child shall know [how] to call [his] father or [his] mother, [one] shall take the power of Damascus and the spoils of Samaria before the king of the Assyrians.
Kafin yaron yă san yadda zai ce ‘Babana’ ko ‘Mamana,’ sarkin Assuriya zai kwashe arzikin Damaskus da ganimar Samariya.”
5 And the Lord spoke to me yet again, [saying],
Ubangiji ya sāke yi mini magana ya ce,
6 Because this people chooses not the water of Siloam that goes softly, but wills to have Rassin, and the son of Romelias [to be] king over you;
“Domin wannan jama’a ta ƙi natsattsen ruwan rafin Shilowa suka yi ta farin ciki a kan Rezin ɗan Remaliya,
7 therefore, behold, the Lord brings up upon you the water of the river, strong and abundant, [even] the king of the Assyrians, and his glory: and he shall come up over every valley of yours, and shall walk over every wall of yours:
saboda haka Ubangiji yana shirin yă kawo musu rigyawar ruwan Kogi, wato, sarkin Assuriya da dukan sojojinsa. Zai cika dukan gaɓoɓinsa, yă kuma malala har zuwa bakin kogi.
8 and he shall take away from Juda [every] man who shall be able to lift up his head, [and every one] able to accomplish anything; and his camp shall fill the breadth of your land, [O] God with us.
Yă yi ta malala har zuwa cikin Yahuda, yă shafe ta, yana ratsa ta ciki har yă kai kafaɗa. Fikafikansa da ya buɗe za su rufe fāɗin ƙasarka, Ya Immanuwel!”
9 Know, you Gentiles, and be conquered; listen you, even to the extremity of the earth: be conquered, after you strengthened yourselves; for even if you should again strengthen yourselves, you shall again be conquered.
Ku yi kururuwar yaƙi, ku ƙasashe, ku kuma ji tsoro! Ku saurara, dukanku manisantan ƙasashe. Ku shirya don yaƙi, ku kuma ji tsoro!
10 And whatever counsel you shall take, the Lord shall bring it to nothing; and whatever word you shall speak, it shall not stand among you: for God is with us.
Ku ƙirƙiro dabarunku, amma ba za su yi nasara ba; ku ƙulla shirye-shiryenku, amma ba za su yi amfani ba, gama Allah yana tare da mu.
11 Thus says the Lord, With a strong hand they revolt from the course of the way of this people, saying,
Ubangiji ya yi mini magana da hannunsa mai ƙarfi a kaina, yana yi mini gargaɗi kada in bi hanyar waɗannan mutane. Ya ce,
12 Let them not say, [It is] hard, for whatever this people says, is hard: but fear not you their fear, neither be dismayed.
“Kada ka kira wani abu makirci game da kome da waɗannan mutane suke kira makirci; kada ji tsoron abin da suke tsoro, kada kuma ka firgita game da shi.
13 Sanctify you the Lord himself; and he shall be your fear.
Ubangiji Maɗaukaki shi ne za ka ɗauka a matsayi mai tsarki, shi ne wanda za ka ji tsoro, shi ne za ka yi rawar jiki a gabansa,
14 And if you shall trust in him, he shall be to you for a sanctuary; and you shall not come against [him] as against a stumbling-stone, neither as against the falling of a rock: but the houses of Jacob are in a snare, and the dwellers in Jerusalem in a pit.
zai kuwa kasance a wuri mai tsarki; amma ga dukan gidajen Isra’ila zai zama dutsen da zai sa mutane su yi tuntuɓe dutse kuma da zai sa su fāɗi. Ga dukan mutanen Urushalima kuma zai zama tarko da raga.
15 Therefore many among them shall be weak, and fall, and be crushed; and they shall draw near, and men shall be taken securely.
Yawancinsu za su yi tuntuɓe; za su fāɗi a kuwa ragargaza su, za a sa musu tarko a kuma kama su.”
16 Then shall those who seal themselves that they may not learn the law be made manifest.
Ɗaura shaidar nan ta gargadi ka kuma yimƙe umarnin Allah a cikin almajiraina.
17 And [one] shall say, I will wait for God, who has turned away his face from the house of Jacob, and I will trust in him.
Zan saurari Ubangiji, wanda ya ɓoye fuskarsa daga gidan Yaƙub. Zan dogara gare shi.
18 Behold I and the children which God has given me: and they shall be [for] signs and wonders in the house of Israel from the Lord of hosts, who dwells in mount Sion.
Ga ni, da yaran da Ubangiji ya ba ni. Mu alamu ne da shaidu a cikin Isra’ila daga Ubangiji Maɗaukaki, wanda yake zama a Dutsen Sihiyona.
19 And if they should say to you, Seek those who have in them a divining spirit, and them that speak out of the earth, them that speak vain words, who speak out of their belly: shall not a nation diligently seek to their God? why do they seek to the dead concerning the living?
Sa’ad da mutane suka ce muku ku nemi shawarar’yan bori da masu sihiri, waɗanda suke shaƙe murya har ba a jin abin da suke faɗi, bai kamata mutane su nemi shawara daga Allahnsu ba? Me zai sa ku nemi shawara daga matattu a madadin masu rai?
20 For he has given the law for a help, that they should not speak according to this word, concerning which there are no gifts to give for it.
Nemi umarnin Allah da kuma shaidar jan kunne. Duk wanda bai yi magana bisa ga wannan kalma ba, ba su da amfani.
21 And famine shall come sorely upon you, and it shall come to pass, [that] when you shall be hungry, you shall be grieved, and you shall speak ill of the prince and your fathers' ordinances: and they shall look up to heaven above,
Cikin matsuwa da yunwa, za su yi ta kai komo ko’ina a ƙasar; sa’ad da suka ji yunwa, za su yi fushi su tā da idanu sama, su zagi sarkinsu da Allahnsu.
22 and they shall look on the earth below, and behold severe distress, and darkness, affliction, and anguish, and darkness so that [one can’t] see; and he that is in anguish shall not be distressed only for a time.
Sa’an nan za su zura wa ƙasa idanu, abin da za su gani kawai shi ne matsuwa da duhu da kuma abin banrazana, za a kuma jefa su cikin baƙin duhu.

< Esias 8 >