< Esias 46 >

1 Bel has fallen, Nabo is broken to pieces, their graven images are gone to the wild beasts and the cattle: you take them packed up as a burden to the weary, exhausted, hungry, and [at the same time] helpless man;
Bel ya rusuna, Nebo ya durƙusa ƙasa; ana ɗaukan gumakansu a kan dabbobi ne. Siffofin da ake yawo da su nawaya ne, kayan nauyi masu gajiyarwa.
2 who will not be able to save themselves from war, but they themselves are led [away] captive.
Sun durƙusa suka kuma rusuna tare; ba su iya kuɓutar da nauyin kaya su kansu sukan tafi bauta.
3 Hear me, O house of Jacob, and all the remnant of Israel, who are borne [by me] from the womb, and taught [by me] from infancy, [even] to old age:
“Ku kasa kunne gare ni, ya ku gidan Yaƙub, dukanku waɗanda kuka rage na gidan Isra’ila, ku da na lura da ku tun da aka yi cikinku, na kuma riƙe ku tun haihuwarku.
4 I am [he]; and until you shall have grown old, I am [he]: I bear you, I have made, and I will relieve, I will take up and save you.
Har lokacin da kuka tsufa kuka yi furfura ni ne shi, ni ne shi wanda zai lura da ku. Na yi ku zan kuma riƙe ku; zan lura da ku in kuma kuɓutar da ku.
5 To whom have you compared me? see, consider, you that go astray.
“Da wa za ku kwatanta ni ko ku ɗauka daidai da ni? Da wa nake kama da har da za ku kwatanta ni?
6 They that furnish gold out of a purse, and silver by weight, will weigh it in a scale, and they hire a goldsmith and make idols, and bow down, and worship them.
Waɗansu sukan zubar da zinariya daga jaka su kuma auna azurfa a ma’auni; sukan yi haya maƙerin zinariya don yă ƙera allah, su kuma rusuna su yi masa sujada.
7 They bear it upon the shoulder, and go; and if they put it upon its place, it remains, it can’t move: and whoever shall cry to it, it can’t hear; it can’t save him from trouble.
Sukan daga shi a kafaɗunsu su kuma ɗauke shi; sukan kafa shi a tsaye a wurinsa, a can kuwa zai tsaya. Daga wannan wuri ba zai iya gusawa ba. Ko da wani ya nemi taimakonsa, ba ya amsawa; ba zai iya cetonsa daga wahala ba.
8 Remember you these things, and groan: repent, you that have gone astray, return in your heart;
“Ku tuna da wannan, ku sa shi a zuciya, ku riƙe shi a zuciya, ku’yan tawaye.
9 and remember the former things [that were] of old: for I am God, and there is none other beside me,
Ku tuna da abubuwan da suka riga suka faru, waɗannan na tun dā; ni ne Allah, kuma babu wani; ni ne Allah kuma babu wani kamar ni.
10 telling beforehand the latter events before they come to pass, and they are accomplished together: and I said, all my counsel shall stand, and I will do all things that I have planned:
Nakan sanar da ƙarshe tun daga farko, daga fil azal, abin da yake zuwa nan gaba. Na ce nufina zai tabbata, kuma zan aikata dukan abin da na gan dama.
11 calling a bird from the east, and from a land afar off, for the things which I have planned: I have spoken, and brought [him]; I have created and made [him]; I have brought him, and prospered his way.
Daga gabas na kira tsuntsun da yake farauta; daga can ƙasa mai nesa, wani mutumin da zai cika nufina. Abin da na riga na faɗa, shi zan sa ya faru; abin da na shirya, shi zan aikata.
12 Listen to me, you senseless ones, that are far from righteousness:
Ku kasa kunne, ku masu taurinkai, ku da kuke nesa da adalci.
13 I have brought near my righteousness, and I will not be slow with the salvation that is from me: I have given salvation in Sion to Israel for glory.
Ina kawo adalcina kusa, ba shi da nisa; kuma cetona ba zai jinkirta ba. Zan yi wa Sihiyona ceto, darajata ga Isra’ila.

< Esias 46 >