< Genesis 35 >

1 And God said to Jacob, Arise, go up to the place, Baethel, and dwell there; and make there an altar to the God that appeared to you, when you fled from the face of Esau your brother.
Sa’an nan Allah ya ce wa Yaƙub, “Haura zuwa Betel ka yi zama a can, ka kuma gina bagade a can wa Allah wanda ya bayyana gare ka sa’ad da kake gudu daga ɗan’uwanka Isuwa.”
2 And Jacob said to his house, and to all that were with him, Remove the strange gods that are with you from the midst of you, and purify yourselves, and change your clothes.
Saboda haka Yaƙub ya ce wa gidansa da kuma dukan waɗanda suke tare da shi, “Ku zubar da baƙin allolin da kuke da su, ku tsarkake kanku, ku kuma canja tufafinku.
3 And let us rise and go up to Baethel, and let us there make an altar to God who listened to me in the day of calamity, who was with me, and preserved me throughout in the journey, by which I went.
Sa’an nan ku zo, mu haura zuwa Betel, inda zan gina bagade wa Allah wanda ya amsa mini a ranar wahalata, wanda kuma ya kasance tare da ni a dukan inda na tafi.”
4 And they gave to Jacob the strange gods, which were in their hands, and the ear-rings which were in their ears, and Jacob hid them under the turpentine tree which is in Secima, and destroyed them to this day.
Saboda haka suka ba Yaƙub dukan baƙin allolin da suke da su, da zoban da suke kunnuwansu, sai Yaƙub ya binne su a ƙarƙashin itacen oak a Shekem.
5 So Israel departed from Secima, and the fear of God was upon the cities round about them, and they did not pursue after the children of Israel.
Sa’an nan suka kama hanya, tsoron Allah kuwa ya kama dukan garuruwan da suke kewayensu har babu wanda ya iya bin su.
6 And Jacob came to Luza, which is in the land of Chanaan, which is Baethel, he and all the people that were with him.
Yaƙub da dukan mutanen da suke tare da shi suka zo Luz (wato, Betel) a ƙasar Kan’ana.
7 And he built there an altar, and called the name of the place Baethel; for there God appeared to him, when he fled from the face of his brother Esau.
A can ya gina bagade, ya kuma kira wurin El Betel, gama a can ne Allah ya bayyana kansa gare shi sa’ad da yake gudu daga ɗan’uwansa.
8 And Deborrha, Rebecca's nurse, died, and was buried below Baethel under the oak; and Jacob called its name, The Oak of Mourning.
To, Debora, ungozomar Rebeka ta rasu aka kuma binne ta a ƙarƙashin itacen oak, ƙasa da Betel. Saboda haka aka kira wurin Allon Bakut.
9 And God appeared to Jacob once more in Luza, when he came out of Mesopotamia of Syria, and God blessed him.
Bayan Yaƙub ya komo daga Faddan Aram, sai Allah ya bayyana gare shi, ya kuma albarkace shi.
10 And God said to him, Your name shall not be called Jacob, but Israel shall be your name; and he called his name Israel.
Allah ya ce masa, “Sunanka Yaƙub ne, amma ba za a ƙara kira ka Yaƙub ba; sunanka zai zama Isra’ila.” Saboda haka ya ba shi suna Isra’ila.
11 And God said to him, I am your God; increase and multiply; for nations and gatherings of nations shall be of you, and kings shall come out of your loins.
Sai Allah ya ce masa, “Ni ne Allah Maɗaukaki, ka yi ta haihuwa, ka kuma riɓaɓɓanya. Al’umma da tarin al’ummai za su fito daga gare ka, sarakuna kuma za su fito daga jikinka.
12 And the land which I gave to Abraam and Isaac, I have given it to you; and it shall come to pass that I will give this land also to your seed after you.
Ƙasar da na ba wa Ibrahim da Ishaku, zan kuma ba ka, zan kuma ba da wannan ƙasa ga zuriyarka a bayanka.”
13 And God went up from him from the place where he spoke with him.
Sa’an nan Allah ya tashi sama daga gare shi a wurin da ya yi magana da shi.
14 And Jacob set up a pillar in the place where God spoke with him, [even] a pillar of stone; and offered a libation upon it, and poured oil upon it.
Yaƙub kuwa ya kafa al’amudin dutse a inda Allah ya yi magana da shi, ya zuba hadaya ta sha a kansa; ya kuma zuba mai a kansa.
15 And Jacob called the name of the place in which God spoke with him, Baethel.
Yaƙub ya kira inda Allah ya yi magana da shi, Betel.
16 [[And Jacob removed from Baethel, and pitched his tent beyond the tower of Gader, ]] and it came to pass when he drew near to Chabratha, to enter into Ephratha, Rachel travailed; and in her travail she was in hard labor.
Sa’an nan suka tashi daga Betel. Yayinda suna da ɗan nisa da Efrat, sai Rahila ta fara naƙuda ta kuwa sha wahala sosai.
17 And it came to pass in her hard labor, that the midwife said to her, Be of good courage, for you shall also have this son.
Sa’ad da take cikin zafin haihuwa, sai macen da ta karɓi haihuwar ta ce mata, “Kada ki ji tsoro, gama yanzu kin sami wani ɗa.”
18 And it came to pass in her giving up the ghost (for she was dying), that she called his name, The son of my pain; but his father called his name Benjamin.
Yayinda take jan numfashinta na ƙarshe, sai ta ba wa ɗanta suna Ben-Oni. Amma mahaifinsa ya kira shi Benyamin.
19 So Rachel died, and was buried in the way of the course of Ephratha, this is Bethleem.
Ta haka Rahila ta rasu, aka kuma binne ta a hanya zuwa Efrata (wato, Betlehem).
20 And Jacob set up a pillar on her tomb; this is the pillar on the tomb of Rachel, until this day.
Yaƙub ya kafa al’amudi bisa kabarinta, al’amudin kabarin Rahila ke nan, wanda yake can har wa yau.
21 And it came to pass when Israel lived in that land, that Ruben went and lay with Balla, the concubine of his father Jacob; and Israel heard, and the thing appeared grievous before him.
Isra’ila ya yi gaba, ya kafa tentinsa gaba da Migdal Eder.
22 And the sons of Jacob were twelve.
Yayinda Isra’ila yana zama a wancan yanki, Ruben ya shiga ya kwana da Bilha ƙwarƙwarar mahaifinsa, Isra’ila kuwa ya ji labari. Yaƙub ya haifi’ya’ya maza goma sha biyu.
23 The sons of Lea, the firstborn of Jacob; Ruben, Symeon, Levi, Judas, Issachar, Zabulon.
’Ya’yan Liyatu maza, Ruben shi ne ɗan fari na Yaƙub. Sauran su ne, Simeyon, Lawi, Yahuda, Issakar da Zebulun.
24 And the sons of Rachel; Joseph and Benjamin.
’Ya’yan Rahila maza su ne, Yusuf da Benyamin.
25 And the sons of Balla, the handmaid of Rachel; Dan and Nephthalim.
’Ya’yan Bilha maza, mai hidimar Rahila su ne, Dan da Naftali.
26 And the sons of Zelpha, the handmaid of Lea; Gad and Aser. These [are] the sons of Jacob, which were born to him in Mesopotamia of Syria.
’Ya’yan Zilfa maza, mai hidimar Liyatu su ne, Gad da Asher. Waɗannan su ne’ya’yan Yaƙub maza, waɗanda aka haifa masa a Faddan Aram.
27 And Jacob came to Isaac his father to Mambre, to a city of the plain; this is Chebron in the land of Chanaan, where Abraam and Isaac sojourned.
Yaƙub ya dawo gida wurin mahaifinsa Ishaku a Mamre, kusa da Kiriyat Arba (wato, Hebron), inda Ibrahim da Ishaku suka zauna.
28 And the days of Isaac which he lived were an hundred and eighty years.
Ishaku ya rayu shekaru ɗari da tamanin,
29 And Isaac gave up the ghost and died, and was laid to his family, old and full of days; and Esau and Jacob his sons buried him.
sa’an nan ya ja numfashinsa na ƙarshe, ya kuwa mutu, aka kuma tara shi ga mutanensa da kyakkyawan tsufa da kuma cikakken shekaru.’Ya’yansa maza, Isuwa da Yaƙub suka binne shi.

< Genesis 35 >