< Genesis 16 >

1 And Sara the wife of Abram bore him no children; and she had an Egyptian maid, whose name was Agar.
To, Saira, matar Abram, ba tă haifa masa’ya’ya ba. Amma tana da wata baiwa mutuniyar Masar mai suna Hagar,
2 And Sara said to Abram, Behold, the Lord has restrained me from bearing, go therefore in to my maid, that I may get children for myself through her. And Abram listened to the voice of Sara.
saboda haka sai ta ce wa Abram, “Ubangiji ya hana mini haihuwar’ya’ya. Tafi ka kwana da baiwata; wataƙila in sami iyali ta wurinta.” Abram kuwa ya yarda da abin da Saira ta faɗa.
3 So Sara the wife of Abram having taken Agar the Egyptian her handmaid, after Abram had lived ten years in the land of Chanaan, gave her to Abram her husband as a wife to him.
Saboda haka bayan Abram ya yi zama a Kan’ana shekaru goma, Saira matarsa ta ɗauki Hagar baiwarta ta ba wa mijinta tă zama matarsa.
4 And he went in to Agar, and she conceived, and saw that she was with child, and her mistress was dishonored before her.
Abram kuwa ya kwana da Hagar, ta kuma yi ciki. Sa’ad da Hagar ta gane tana da ciki, sai ta fara rena uwargijiyarta.
5 And Sara said to Abram, I am injured by you; I gave my handmaid into your bosom, and when I saw that she was with child, I was dishonored before her. The Lord judge between me and you.
Sai Saira ta ce wa Abram, “Kai ne da alhakin wahalan nan da nake sha. Na sa baiwata a hannunka, yanzu da ta sani tana da ciki, sai ta fara rena ni. Bari Ubangiji yă shari’anta tsakanina da kai.”
6 And Abram said to Sara, Behold your handmaid is in your hands, use her as it may seem good to you. And Sara afflicted her, and she fled from her face.
Abram ya ce, “Baiwarki tana a hannunki? Ki yi da ita yadda kika ga ya fi kyau.” Sai Saira ta wulaƙanta Hagar; saboda haka ta gudu daga gare ta.
7 And an angel of the Lord found her by the fountain of water in the wilderness, by the fountain in the way to Sur.
Mala’ikan Ubangiji ya sami Hagar kusa da maɓulɓula a jeji, ita ce maɓulɓular da take gefen hanya zuwa Shur.
8 And the angel of the Lord said to her, Agar, Sara's maid, whence come you, and wither go you? and she said, I am fleeing from the face of my mistress Sara.
Ya kuma ce mata, “Hagar, baiwar Saira, daga ina kika fito, kuma ina za ki?” Ta amsa ta ce, “Ina gudu ne daga wurin uwargijiyata Saira.”
9 And the angel of the Lord said to her, Return to your mistress, and submit yourself under her hands.
Sai mala’ikan Ubangiji ya ce mata, “Koma wurin uwargijiyarki Saira, ki yi mata biyayya.”
10 And the angel of the Lord said to her, I will surely multiply your seed, and it shall not be numbered for multitude.
Mala’ikan ya ƙara da cewa, “Zan ƙara zuriyarki har su yi yawan da ba wanda zai iya lasafta su.”
11 And the angel of the Lord said to her, Behold you are with child, and shall bear a son, and shall call his name Ismael, for the Lord has listened to your humiliation.
Mala’ikan Ubangiji ya kuma ce mata, “Ga shi kina da ciki za ki kuwa haifi ɗa. Za ki ba shi suna Ishmayel, gama Ubangiji ya ga wahalarki.
12 He shall be a wild man, his hands against all, and the hands of all against him, and he shall dwell in the presence of all his brethren.
Zai zama mutum mai halin jakin jeji. Hannunsa zai yi gāba da kowa, hannun kowa kuma zai yi gāba da shi. Zai yi zama gāba ga dukan’yan’uwansa.”
13 And she called the name of the Lord God who spoke to her, You are God who see me; for she said, For I have openly seen him that appeared to me.
Sai ta ba wa Ubangiji wanda ya yi magana da ita, wannan suna. “Kai Allah ne wanda yake ganina,” gama ta ce, “Yanzu na ga wanda yake ganina.”
14 Therefore she called the well, The well of him whom I have openly seen; behold it is between Cades and Barad.
Shi ya sa ake kira rijiyar Beyer-Lahai-Royi tana nan har yanzu, tsakanin Kadesh da Bered.
15 And Agar bore a son to Abram; and Abram called the name of his son which Agar bore to him, Ismael.
Haka fa Hagar ta haifa wa Abram ɗa, Abram kuwa ya ba da suna Ishmayel ga ɗan da ta haifa.
16 And Abram was eighty-six years old, when Agar bore Ismael to Abram.
Abram yana da shekaru 86 sa’ad da Hagar ta haifa masa Ishmayel.

< Genesis 16 >