< Jezekiel 39 >

1 And you, son of man, prophesy against Gog, and say, Thus says the Lord; Behold, I am against you, O Gog, Rhos prince of Mesoch and Thobel:
“Ɗan mutum, ka yi annabci a kan Gog ka ce, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da kai, ya Gog, babban sarkin Meshek da Tubal.
2 and I will assemble you, and guide you, and raise you up on the extremity of the north, and I will bring you up upon the mountains of Israel.
Zan juya ka in kuma ja ka. Zan kawo ka daga can arewa in aike ka don ka fāɗa wa duwatsun Isra’ila.
3 And I will destroy the bow out of your left hand, and your arrows out of your right hand, and I will cast you down on the mountains of Israel;
Sa’an nan zan karya bakan da take a hannun hagunka, in sa kibiyoyin da suke a hannun damanka su fāɗi.
4 and you and all that belong to you shall fall, and the nations that are with you shall be given to multitudes of birds, [even] to every fowl, and I have given you to all the wild beasts of the field to be devoured.
A kan duwatsun Isra’ila za ka fāɗi, kai da sojojinka da kuma al’ummai da suke tare da kai. Zan bayar da kai ka zama abinci ga tsuntsaye da namun jeji masu cin nama.
5 You shall fall on the face of the field: for I have spoken [it], says the Lord.
Za ka mutu a fili, gama haka ni na faɗa, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
6 And I will send a fire upon Gog, and the islands shall be securely inhabited: and they shall know that I am the Lord.
Zan aika da wuta a kan Magog da kuma a kan waɗanda suke zama lafiya a bakin teku, za su kuwa san cewa ni ne Ubangiji.
7 And my holy name shall be known in the midst of my people Israel; and my holy name shall no more be profaned: and the nations shall know that I am the Lord, the Holy [One] in Israel.
“‘Zan sanar da sunana mai tsarki a cikin mutanena Isra’ila. Ba zan ƙara bari a ɓata sunana mai tsarki ba, kuma al’ummai za su san cewa Ni Ubangiji Mai Tsarki ne a cikin Isra’ila.
8 Behold it is come, and you shall know that it shall be, says the Lord God; this is the day concerning which I have spoken.
Yana zuwa! Tabbatacce zai faru, in ji Ubangiji Mai Iko Duka. Ranar da na yi magana ke nan.
9 And they that inhabit the cities of Israel shall come forth, and make a fire with the arms, the shields and the spears, and bows and arrows, and hand-staves, and lances, and they shall keep fire burning with them for seven years:
“‘Sa’an nan waɗanda suke zama a garuruwan Isra’ila za su fita su tattara makamai su hura wuta da su su kuma ƙone su, manya da ƙanana garkuwoyi, bakkuna da kibiyoyi, kulake da māsu. Shekara bakwai za su yi amfani da su don hura wuta.
10 and they shall not take any wood out of the field, neither shall they cut any out of the forests, but they shall burn the weapons with fire: and they shall plunder those that plundered them, and spoil those that spoiled them, says the Lord.
Ba za su yi wahalar zuwa jeji don neman itacen hura wuta ba, domin za su yi amfani da makamai don hura wuta. Za su kuma washe waɗanda suka washe su ganima, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
11 And it shall come to pass [that] in that day I will give to Gog a place of renown, a tomb in Israel, the burial-place of them that approach the sea: and they shall build round about the outlet of the valley, and there they shall bury Gog and all his multitude: and [the place] shall then be called the burial-place of Gog.
“‘A ranar zan yi wa Gog makabarta a cikin Isra’ila, a kwarin waɗanda suke tafiya wajen gabashin Teku. Za tă tare hanyar matafiya, domin za a binne Gog da dukan mutanensa a can. Ta haka za a kira wurin Kwarin Haman Gog.
12 And the house of Israel shall bury them, that the land may be cleansed in the space of seven months.
“‘Watanni bakwai gidan Isra’ila zai yi ta binne su don a tsarkake ƙasar.
13 Yes, all the people of the land shall bury them; and it shall be to them a [place] of renown in the day wherein it was glorified, says the Lord.
Dukan mutanen ƙasar za su binne su, kuma ranar da za a ɗaukaka ni za tă zama ranar tuni a gare su, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
14 And they shall appoint men continually to go over the land, to bury them that have been left on the face of the earth, to cleanse it after the space of seven months, and they shall seek [them] out.
“‘Za a ɗauki mutane kullum don tsabtacce ƙasar. Waɗansu za su ratsa ƙasar, ƙari da waɗannan, waɗansu za su binne gawawwakin da suka ragu a ƙasar. A ƙarshen watanni bakwai ɗin za su fara bincikensu.
15 And every one that goes through the land, and sees a man's bone, shall set up a mark by it, until the buriers shall have buried it in the valley, the burial place of Gog.
Yayinda suke ratsa ƙasar, in waninsu ya ga ƙashin mutum, zai kafa shi kamar alama a gefe sai masu haƙa kabari sun binne shi a Kwarin Haman Gog.
16 For the name of the city [shall be] Burial-place: so shall the land be cleansed.
Akwai wani garin da ake kira Hamona zai kasance a can. Ta haka za su tsabtacce ƙasar.’
17 And you, son of man, say, Thus says the Lord; Say to every winged bird, and to all the wild beasts of the field, Gather yourselves, and come; gather yourselves from all [places] round about to my sacrifice, which I have made for you, [even] a great sacrifice on the mountains of Israel, and you shall eat flesh, and drink blood.
“Ɗan mutum, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa, ka gayyato kowane irin tsuntsu da dukan namun jeji, ‘Ku taru ku kuma zo wuri ɗaya daga ko’ina don hadayar da nake shirya muku, babbar hadaya a kan duwatsun Isra’ila. A can za ku ci nama ku kuma sha jini.
18 You shall eat the flesh of mighty men, and you shall drink the blood of princes of the earth, rams, and calves and goats, and they are all fatted calves.
Za ku ci naman manyan mutane ku kuma sha jinin sarakunan duniya sai ka ce an yanka raguna da’yan tumaki, awaki da bijimai, dukansu turkakkun dabbobi daga Bashan.
19 And you shall eat fat till you are full, and shall drink wine till you are drunken, of my sacrifice which I have prepared for you.
A hadayar da nake shirya muku, za ku ci kitse sai kun ƙoshi ku kuma sha jini sai kun bugu.
20 And you shall be filled at my table, [eating] horse, and rider, and mighty man, and every warrior, says the Lord.
A teburina za ku ci iya ƙoshiyarku da naman jama’a da kuma mahaya, manyan mutane da sojoji na kowane iri,’ in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
21 And I will set my glory among you, and all the nations shall see my judgment which I have wrought, and my hand which I have brought upon them.
“Zan nuna ɗaukakata a cikin al’ummai, kuma dukan al’ummai za su ga hukuncin da zan yi da kuma hannu mai nauyin da zan ɗora a kansu.
22 And the house of Israel shall know that I am the Lord their God, from this day and onwards.
Daga wannan rana zuwa gaba gidan Isra’ila zai san cewa ni ne Ubangiji Allahnsu.
23 And all the nations shall know that the house of Israel were led captive because of their sins, because they rebelled against me, and I turned away my face from them, and delivered them into the hands of their enemies, and they all fell by the sword.
Al’ummai kuma za su san cewa mutanen Isra’ila sun tafi zaman bauta saboda zunubinsu, domin sun yi rashin aminci gare ni. Saboda haka na kawar da fuskata daga gare su na miƙa su ga abokan gābansu, suka kuwa mutu ta takobi.
24 According to their uncleannesses and according to their transgressions did I deal with them, and I turned away my face from them.
Na yi da su gwargwadon rashin tsabtarsu da laifofinsu, na kuma kawar da fuskata daga gare su.
25 Therefore thus says the Lord God, Now will I turn back captivity in Jacob, and will have mercy on the house of Israel, and will be jealous for the sake of my holy name.
“Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan komo da Yaƙub daga zaman bauta zan kuma yi wa dukan Isra’ila jinƙai, zan kuma yi kishi saboda sunana mai tsarki.
26 And they shall bear their reproach, and the iniquity which they committed when they lived upon their land in peace. Yet there shall be none to terrify [them]
Za su manta da kunyar da suka sha da dukan rashin amincin da suka nuna mini sa’ad da suke zama lafiya a ƙasarsu inda ba wanda zai tsorata su.
27 when I have brought them back from the nations, and gathered them out of the countries of the nations: and I will be sanctified among them in the presence of the nations.
Sa’ad da na komo da su daga al’ummai na kuma tattara su daga ƙasashen abokan gābansu, zan nuna kaina mai tsarki ta wurinsu a gaban al’ummai masu yawa.
28 And they shall know that I am the Lord their God, when I have been manifested to them among the nations.
Sa’an nan za su san cewa ni ne Ubangiji Allahnsu, gama ko da yake na tura su zaman bauta a cikin al’ummai, zan tattara su zuwa ƙasarsu, ba tare da barin wani a baya ba.
29 And I will no more turn away my face from them, because I have poured out my wrath upon the house of Israel, says the Lord God.
Ba zan ƙara kawar da fuskata daga gare su, gama zan zuba Ruhuna a kan gidan Isra’ila, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.”

< Jezekiel 39 >