< Exodus 8 >

1 And the Lord said to Moses, Go in to Pharao, and you shall say to him, These things says the Lord: send forth my people, that they may serve me.
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka je wurin Fir’auna, ka ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, ka bar mutanena su tafi domin su yi mini sujada.
2 And if you will not send them forth, behold, I afflict all your borders with frogs:
In ka ƙi barinsu, zan hore ka da annoban kwaɗi a dukan ƙasarka.
3 and the river shall teem with frogs, and they shall go up and enter into your houses, and into your bed-chambers, and upon your beds, and upon the houses of your servants, and of your people and on your dough, and on your ovens.
Nilu zai cika da kwaɗi. Za su haura zuwa cikin fadanka da kan gadonka, cikin gidajen bayinka da kan mutanenka, cikin kwanonin toye-toyenka da na cin abincinka.
4 And upon you, and upon your servants, and upon your people, shall the frogs come up.
Kwaɗin nan za su yi ta tsalle a kanka, da kan mutanenka, da kuma kan dukan bayinka.’”
5 And the Lord said to Moses, Say to Aaron your brother, Stretch forth with the hand your rod over the rivers, and over the canals, and over the pools, and bring up the frogs.
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ce wa Haruna, ‘Ka miƙa hannunka da sandanka bisa koguna da rafuffuka da kuma kududdufai, ka sa kwaɗi su fito su mamaye ƙasar Masar.’”
6 And Aaron stretched forth his hand over the waters of Egypt, and brought up the frogs: and the frog was brought up, and covered the land of Egypt.
Sai Haruna ya miƙa hannunsa bisa ruwan Masar, kwaɗi kuwa suka fito, suka mamaye ƙasar Masar.
7 And the charmers of the Egyptians also did likewise with their sorceries, and brought up the frogs on the land of Egypt.
Amma bokaye ma suka yi abubuwan nan ta wurin sihirinsu; suka sa kwaɗi suka fito suka mamaye ƙasar Masar.
8 And Pharao called Moses and Aaron, and said, Pray for me to the Lord, and let him take away the frogs from me and from my people; and I will send them away, and they shall sacrifice to the Lord.
Fir’auna ya kira Musa da Haruna ya ce, “Yi addu’a ga Ubangiji yă ɗauke kwaɗi daga gare ni da mutanena, zan kuwa bar mutanenku su tafi su yi hadaya ga Ubangiji.”
9 And Moses said to Pharao, Appoint me [a time] when I shall pray for you, and for your servants, and for your people, to cause the frogs to disappear from you, and from your people, and from your houses, only in the river shall they be left behind.
Musa ya ce wa Fir’auna, “Na ba ka dama ka ba da lokacin da zan yi addu’a dominka da kuma bayinka da mutanenka, gidajenku kuwa za su rabu da kwaɗi, amma ban da waɗanda suke cikin Nilu.”
10 And he said, On the morrow: he said therefore, As you has said; that you may know, that there is no other [God] but the Lord.
Fir’auna ya ce, “Gobe.” Musa ya amsa, “Za a yi kamar yadda ka faɗa, domin ka sani babu wani kamar Ubangiji, Allahnmu.
11 And the frogs shall be removed away from you, and from your houses and from the villages, and from your servants, and from your people, only in the river they shall be left.
Kwaɗin za su bar ka da gidajenka, bayinka da mutanenka; za su kasance a Nilu ne kaɗai.”
12 And Moses and Aaron went forth from Pharao, and Moses cried to the Lord concerning the restriction of the frogs, as Pharao appointed him.
Bayan Musa da Haruna sun bar Fir’auna, Sai Musa ya yi kuka ga Ubangiji saboda kwaɗin da ya kawo a bisa Fir’auna.
13 And the Lord did as Moses said, and the frogs died out of the houses, and out of the villages, and out of the fields.
Sai Ubangiji ya yi abin da Musa ya nema. Kwaɗin suka mutu a gidaje, da filaye, da kuma gonaki.
14 And they gathered them together in heaps, and the land stank.
Aka jibga su tsibi-tsibi, ƙasar ta yi ɗoyi saboda su.
15 And when Pharao saw that there was relief, his heart was hardened, and he did not listen to them, as the Lord spoke.
Amma da Fir’auna ya ga an sami sauƙi, sai ya taurare, ya ƙi yă saurari Musa da Haruna kamar dai yadda Ubangiji ya riga ya faɗa.
16 And the Lord said to Moses, Say to Aaron, Stretch forth your rod with your hand and strike the dust of the earth; and there shall be lice both upon man, and upon quadrupeds, and in all the land of Egypt.
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ce wa Haruna, ‘Miƙa hannunka ka bugi ƙurar ƙasa,’ dukan ƙurar ƙasar Masar kuwa za tă zama ƙwari masu cizo.”
17 So Aaron stretched out his rod with his hand, and struck the dust of the earth; and the lice were on men and on quadrupeds, and in all the dust of the earth there were lice.
Suka yi haka, da Haruna ya miƙa hannunsa da sandan, ya bugi ƙurar ƙasa, sai ƙwari masu cizo suka fito a kan mutane da dabbobi. Dukan ƙurar, ko’ina a ƙasar Masar ta zama cinnaku.
18 And the charmers also did so with their sorceries, to bring forth the louse, and they could not. And the lice were both on the men and on the quadrupeds.
Sa’ad da bokayen Fir’auna suka yi ƙoƙari yin sihiri iri na rufe ido domin su fito da kwari, sai suka kāsa. Ƙwari masu cizo kuwa suka rufe mutane da dabbobi.
19 So the charmers said to Pharao, This is the finger of God. But the heart of Pharao was hardened, and he listened not to them, as the Lord said.
Sai bokaye suka ce wa Fir’auna, “Wannan fa da hannun Allah a ciki.” Amma zuciyar Fir’auna ta taurare, bai kuwa saurara ba, kamar dai yadda Ubangiji ya riga ya faɗa.
20 And the Lord said to Moses, Rise up early in the morning, and stand before Pharao: and behold, he will go forth to the water, and you shall say to him, These things says the Lord: Send away my people, that they may serve me in the wilderness.
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka tashi da sassafe ka sadu da Fir’auna a lokacin da za shi kogi, ka ce masa, ‘Ga abin da Ubangiji yana cewa, bari mutanena su tafi, don su yi mini sujada.
21 And if you will not let my people go, behold, I send upon you, and upon your servants, and upon your people, and upon your houses, the dog-fly; and the houses of the Egyptians shall be filled with the dog-fly, even throughout the land upon which they are.
In ba ka bar mutanena suka tafi ba, zan turo da tarin ƙuda a kanka da bayinka, a kan mutanenka da cikin gidajenka. Gidajen Masarawa za su cika da ƙudaje, har ma da ƙasa inda za su taka.
22 and I will distinguish marvelously in that day the land of Gesem, on which my people dwell, in which the dog-fly shall not be: that you may know that I am the Lord the God of all the earth.
“‘Amma zan keɓe yankin Goshen, inda mutanena suke don kada ƙudaje su taɓa wurin, domin ka sani cewa Ni, Ubangiji, ina cikin wannan ƙasa.
23 And I will put a difference between my people and your people, and on the morrow shall this be on the land. And the Lord did thus.
Zan sa iyaka tsakanin jama’ata da jama’arka. Gobe ne wannan mu’ujiza za tă auku.’”
24 And the dog-fly came in abundance into the houses of Pharao, and into the houses of his servants, and into all the land of Egypt; and the land was destroyed by the dog-fly.
Ubangiji kuwa ya yi haka. Tarin ƙuda suka zubo a fadar Fir’auna da cikin gidajen bayinsa, da ko’ina a Masar, ƙasar kuwa ta lalace saboda ƙudaje.
25 And Pharao called Moses and Aaron, saying, Go and sacrifice to the Lord your God in the land.
Sai Fir’auna ya kira Musa da Haruna ya ce, “Ku tafi, ku miƙa hadaya ga Allahnku, a nan a cikin ƙasar.”
26 And Moses said, It can’t be so, for we shall sacrifice to the Lord our God the abominations of the Egyptians; for if we sacrifice the abominations of the Egyptians before them, we shall be stoned.
Amma Musa ya ce, “Wannan ba zai yiwu ba. Hadayun da mukan miƙa wa Ubangiji, Allahnmu haram ne ga Masarawa. In kuwa muka miƙa hadayun da suke haram a idanunsu, ba za su jajjefe mu ba?
27 We will go a journey of three days into the wilderness, and we will sacrifice to the Lord our God, as the Lord said to us.
Dole mu yi tafiya kwana uku cikin hamada domin miƙa hadayu ga Ubangiji Allahnmu, yadda ya umarce mu.”
28 And Pharao said, I [will] let you go, and do you sacrifice to your God in the wilderness, but do not go very far away: pray then for me to the Lord.
Fir’auna ya ce, “Zan bar ku ku tafi, don ku miƙa hadayu ga Ubangiji Allahnku, a cikin hamada, amma ba za ku tafi da nisa ba. Yanzu ku yi mini addu’a.”
29 And Moses said, I then will go forth from you and pray to God, and the dog-fly shall depart both from your servants, and from your people to-morrow. Do not you, Pharao, deceive again, so as not to send the people away to do sacrifice to the Lord.
Musa ya amsa, “Da zarar na bar ka, zan yi addu’a ga Ubangiji, gobe kuwa ƙudaje za su bar Fir’auna da fadawansa da kuma mutanensa. Sai dai a tabbata Fir’auna bai sāke yin ruɗi ta wurin ƙin barin mutane su tafi su miƙa hadayu ga Ubangiji ba.”
30 And Moses went out from Pharao, and prayed to God.
Sa’an nan Musa ya rabu da Fir’auna, ya kuma yi addu’a ga Ubangiji,
31 And the Lord did as Moses said, and removed the dog-fly from Pharao, and from his servants, and from his people, and there was not one left.
Ubangiji kuwa ya yi abin da Musa ya roƙa. Ƙudaje suka rabu da Fir’auna da fadawansa da kuma mutanensa; ba ƙudan da ya rage.
32 And Pharao hardened his heart, even on this occasion, and he would not send the people away.
Amma a wannan lokaci ma, Fir’auna ya taurare zuciyarsa, bai kuma bar mutanen suka tafi ba.

< Exodus 8 >