< Exodus 31 >

1 And the Lord spoke to Moses, saying,
Sai Ubangiji ya ce wa Musa,
2 Behold, I have called by name Beseleel the son of Urias the son of Or, of the tribe of Juda.
“Duba, na zaɓi Bezalel ɗan Uri, ɗan Hur, na kabilar Yahuda,
3 And I have filled him [with] a divine spirit of wisdom, and understanding, and knowledge, to invent in every work,
na kuma cika shi da Ruhun Allah, fasaha, azanci, da kuma sani cikin kowace irin sana’a,
4 and to frame works, to labor in gold, and silver, and brass, and blue, and purple, and spun scarlet,
don yin zāne-zāne na aikin zinariya, azurfa da tagulla,
5 and works in stone, and for artificers' work in wood, to work at all works.
don yanka da shirya duwatsu, yin aikin katako, da kuma yin kowane irin aikin sana’ar hannu.
6 And I have appointed him and Eliab the [son] of Achisamach of the tribe of Dan, and to every one understanding in heart I have given understanding; and they shall make all things as many as I have appointed you, —
Ban da haka, na zaɓi Oholiyab ɗan Ahisamak, na kabilar Dan, don yă taimake shi. Na kuma ba da fasaha ga dukan masu aikin sana’ar hannu, don yin duk abin da na umarce ka.
7 the tabernacle of witness, and the ark of the covenant, and the propitiatory that is upon it, and the furniture of the tabernacle,
Tentin Sujada, akwatin Alkawari tare da murfin kafara a bisansa, da dukan kayan aiki na tentin,
8 and the altars, and the table and all its furniture,
tebur da kayansa, wurin ajiye fitila na zinariya zalla, da dukan kayansa, bagaden ƙona turare,
9 and the pure candlestick and all its furniture, and the laver and its base,
bagaden hadaya ta ƙonawa da dukan kayansa, daro tare da mazauninsa,
10 and Aaron's robes of ministry, and the robes of his sons to minister to me as priests,
da kuma saƙaƙƙun riguna, tsarkakan riguna don Haruna firist da rigunan’ya’yansa maza, sa’ad da suke hidima a matsayin firistoci,
11 and the anointing oil and the compound incense of the sanctuary; according to all that I have commanded you shall they make them.
da man shafewa, da turare mai ƙanshi don Wuri Mai Tsarki. Za a yi su kamar yadda na umarce ka.”
12 And the Lord spoke to Moses, saying,
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa,
13 Do you also charge the children of Israel, saying, Take heed and keep my sabbaths; [for] they are a sign with me and among you throughout your generations, that you may know that I am the Lord that sanctifies you.
“Ka faɗa wa Isra’ilawa, ‘Dole ku kiyaye Asabbataina. Wannan zai zama alama tsakanina da ku daga tsara zuwa tsara, saboda ku sani ni ne Ubangiji, wanda ya mai da ku masu tsarki.
14 And you shall keep the sabbaths, because this is holy to the Lord for you; he that profanes it shall surely be put to death: every one who shall do a work on it, that soul shall be destroyed from the midst of his people.
“‘Ku kiyaye Asabbaci, domin yă zama mai tsarki a gare ku. Duk wanda ya ƙazantar da shi, za a kashe shi; duk wanda ya yi wani aiki a ranar, za a ware shi daga mutane.
15 Six days you shall do works, but the seventh day is the sabbath, a holy rest to the Lord; every one who shall do a work on the seventh day shall be put to death.
Kwana shida, za a yi aiki, amma a rana ta bakwai, Asabbaci ne na hutu, mai tsarki ga Ubangiji. Duk wanda ya yi wani aiki a Asabbaci, za a kashe shi.
16 And the children of Israel shall keep the sabbaths, to observe them throughout their generations.
Isra’ilawa za su kiyaye Asabbaci, suna bikinsa daga tsara zuwa tsara a matsayin madawwamin alkawari.
17 It is a perpetual covenant with me and the children of Israel, it is a perpetual sign with me; for in six days the Lord made the heaven and the earth, and on the seventh day he ceased, and rested.
Zai zama alama tsakanina da Isra’ilawa har abada, gama cikin kwana shida Ubangiji ya yi sama da ƙasa, a rana ta bakwai kuma ya daina aiki, ya kuma huta.’”
18 And he gave to Moses when he left off speaking to him in mount Sina the two tables of testimony, tables of stone written [upon] with the finger of God.
Sa’ad da Ubangiji ya gama yin wa Musa magana a kan Dutsen Sinai, sai ya ba shi alluna biyu na Alkawari, allunan duwatsu rubutattu da yatsan Allah.

< Exodus 31 >