< Daniel 11 >

1 And I in the first year of Cyrus stood to strengthen and confirm [him].
A shekara ta fari ta Dariyus mutumin Mede, na ɗauki matsayina domin in goyi baya in kuma kāre shi.)
2 And now I will tell you the truth. Behold, there shall yet rise up three kings in Persia: and the fourth shall be very far richer than all: and after that he is master of his wealth, he shall rise up against all the kingdoms of the Greeks.
“Yanzu dai, zan faɗa maka gaskiya. Sarakuna uku za su taso a Farisa, sa’an nan kuma na huɗu, wanda zai fi dukansu dukiya. Sa’ad da zai sami iko saboda dukiyarsa, zai zuga dukan kowane mutum yă yi gāba da masarautar Girka.
3 An there shall rise up a mighty king, and he shall be lord of a great empire, and shall do according to his will.
Sa’an nan wani babban sarki zai bayyana, wanda zai yi mulki da babban iko yă kuma yi abin da ya ga dama.
4 And when his kingdom shall stand up, it shall be broken, and shall be divided to the four winds of heaven; but not to his posterity, nor according to his dominion which he ruled over: for his kingdom shall be plucked up, and [given] to others beside these.
Bayan da ya bayyana, daularsa za tă wargaje za a rarraba ta zuwa kusurwoyi huɗu na duniya, a ba waɗansu waɗanda ba zuriyarsa ba, ba kuwa za su yi mulki da iko kamar yadda ya yi ba, gama za a tumɓuki daularsa a kuma ba wa waɗansu.
5 And the king of the south shall be strong; and one of their princes shall prevail against him, and shall obtain a great dominion.
“Sai sarki Kudu zai yi ƙarfi ƙwarai, amma ɗaya daga cikin komandodinsa zai yi ƙarfi fiye da shi, zai kuma yi mulki masarautarsa da iko mai girma.
6 And after his years they shall associate; and the daughter of the king of the south shall come to the king of the north, to make agreements with him: but she shall not retain power of arm; neither shall his seed stand: and she shall be delivered up, and they that brought her, and the maiden, and he that strengthened her in these times.
Bayan’yan shekaru, za su haɗa kai. Diyar sarkin Kudu za tă je wurin sarkin Arewa ta sada zumunci, amma ba za tă riƙe iko ba, shi kuwa da ikonsa ba za su daɗe ba. A waɗannan kwanaki za a bashe ta, da ita da masu rakiyarta da kuma mahaifinta da kuma wanda ya goyi bayanta.
7 [But] out of the flower of her root there shall arise [one on] his place, and shall come against the host, and shall enter into the strongholds of the king of the north, and shall fight against them, and prevail.
“Wani daga cikin zuriyarta zai taso yă ɗauki matsayinta. Zai kai wa sojojin sarkin Arewa hari yă kuma shiga kagararsa; zai yi yaƙi da su yă kuma yi nasara.
8 Yes, he shall carry with a body of captives into Egypt their gods with their molten [images, and] all their precious vessels of silver and gold; and he shall last longer than the king of the north.
Zai ƙwace allolinsu, siffofinsu na ƙarfe da kuma kaya masu daraja na azurfa da na zinariya a kuma kai su Masar. Zai yi’yan shekaru bai kai wa sarkin Arewa yaƙi ba.
9 And he shall enter into the kingdom of the king of the south, and shall return to his own land.
Sa’an nan sarkin Arewa zai kai wa sarkin Kudu hari, amma zai janye, yă koma ƙasarsa.
10 And his sons shall gather a multitude among many: and one shall certainly come, and overflow, and pass through, and he shall rest, and collect his strength.
’Ya’yansa maza za su yi shirin yaƙi za su kuma tattara babbar rundunar sojoji, waɗanda za su yi ta mamayewa kamar rigyawar da ba iya tarewa, kuma za su kai yaƙin har kagararsa.
11 And the king of the south shall be greatly enraged, and shall come forth, and shall war with the king of the north: and he shall raise a great multitude; but the multitude shall be delivered into his hand.
“Sa’an nan sai sarkin Kudu zai kama hanya da fushi zuwa yaƙi da sarkin Arewa, wanda zai tattara babbar rundunar yaƙi, amma za a ci shi da yaƙi.
12 And he shall take the multitude, and his heart shall be exalted; and he shall cast down many thousands; but he shall not prevail.
Sa’ad da zai kawar da rundunar, sarkin Kudu zai cika da girman kai zai kuma kashe mutane dubbai, duk da haka ba zai kasance mai nasara ba.
13 For the king of the north shall return, and bring a multitude greater than the former, and at the end of the times of years an invading army shall come with a great force, and with much substance.
Sarki Arewa kuma zai ƙara tara babbar rundunar soja, wadda ta fi ta dā girma; bayan waɗansu shekaru kuma, zai tafi yaƙi da babbar rundunar mayaƙa cike da kayan yaƙi.
14 And in those times many shall rise up against the king of the south; and the children of the spoilers of your people shall exalt themselves to establish the vision; and they shall fail.
“A waɗannan lokutan mutane da yawa za su tashi gāba da sarkin Kudu. Amma waɗansu’yan kama-karya za su taso daga jama’arka da niyya su cika abin da wahayin ya ce, amma za a fatattake su.
15 And the king of the north shall come in, and cast up a mound, and take strong cities: and the arms of the king of the south shall withstand, and his chosen ones shall rise up, but there shall be no strength to stand.
Sa’an nan sarkin arewa zai zo ya gina mahaurai a jikin katagar birni don yă ci birnin da yaƙi. Sojojin nan na Kudu kuwa ba za su iya tsayawa ba, ko zaɓaɓɓun jarumawansu ma, gama za su rasa ƙarfin tsayawa.
16 And he that comes in against him shall do according to his will, and there is no one to stand before him: and he shall stand in the land of beauty, and it shall be consumed by his hand.
Wanda ya kai harin zai yi yadda ya ga dama, ba wanda zai iya ja da shi. Zai kafa kansa a Kyakkyawar Ƙasa zai kuma sami ikon da zai hallaka ta.
17 And he shall set his face to come in with the force of his whole kingdom, and shall cause everything to prosper with him: and he shall give him the daughter of women to corrupt her: but she shall not continue, neither be on his side.
Zai yunƙura yă zo da ƙarfin dukan masarautarsa zai kuma nemi haɗinkan sarkin Kudu. Zai kuma ba shi diyarsa yă aura don yă lalatar da mulkin, amma shirinsa ba zai yi nasara ba ko yă taimake shi ba.
18 And he shall turn his face to the islands, and shall take many, and cause princes to cease from their reproach: nevertheless his own reproach shall return to him.
Sa’an nan zai mai da hankalinsa zuwa ƙasashe a bakin kogi, zai kuma kama da yawansu, amma wani komanda zai kawo ƙarshen faɗin ransa, zai kuma sa faɗin ransa yă koma masa.
19 Then he shall turn back his face to the strength of his own land: but he shall become weak, and fall, and not be found.
Bayan wannan, zai juya ga kagarar ƙasarsa, amma zai yi tuntuɓe yă fāɗi, ba kuwa za a ƙara ganinsa ba.
20 And there shall arise out of his root one that shall cause a plant of the kingdom to pass over his place, earning kingly glory: and yet in those days shall he be broken, yet not openly, nor in war.
“Magājinsa zai aiki mai karɓar haraji don darajar masarautarsa. Amma ba da daɗewa ba za a hallaka shi, duk da haka ba da fushi ko cikin yaƙi ba.
21 [One] shall stand on his place, [who] has been set a nothing, and they have not put upon him the honor of the kingdom: but he shall come in prosperously, and obtain the kingdom by deceitful ways.
“Magājin wannan sarki zai zama wani mutumin banza wanda ma bai fito daga gidan sarauta ba. Zai taso ba zato ba tsammani, yă ƙwace sarautar ta hanyar zamba.
22 And the arms of him that overflows shall be washed away as with a flood from before him, and shall be broken, and [so shall be] the head of the covenant.
Sa’an nan zai shafe mayaƙa masu yawa a gabansa; zai hallaka har da waɗanda suke mulki na alkawari.
23 And because of the leagues made with him he shall work deceit: and he shall come up, and overpower them with a small nation.
Bayan ƙulla yarjejjeniya da shi, zai yi zamba cikin aminci, kuma zai sami damar hawan mulki da goyon baya mutane kaɗan.
24 And he shall enter with prosperity, and [that] into fertile districts; and he shall do what his fathers and his fathers' fathers have not done; he shall scatter among them plunder, and spoils, and wealth; and he shall devise plans against Egypt, even for a time.
Sa’ad da yankuna mafi arziki suke ji kome lafiya yake, zai kai musu hari kuma Zai aikata abin da kakanninsa ba su taɓa yi ba. Zai rarraba abin da aka kwaso daga yaƙi, da ganima, da dukiya ga dukan mabiyansa. Zai kuma yi shiri yă kai wa mafaka hari, amma na ɗan lokaci ne kawai.
25 And his strength and his heart shall be stirred up against the king of the south with a great force; and the king of the south shall engage in war with a great and very strong force; but [his forces] shall not stand, for they shall devise plans against him:
“Tare da babbar rundunar mayaƙa zai yi ƙarfin hali yă far wa sarkin Kudu da yaƙi. Sarkin kudu zai haɗa babbar rundunar soja mai ƙarfi don yaƙin, amma ba zai iya karo da shi ba, domin za a shirya masa maƙarƙashiya.
26 and they shall eat his provisions, and shall crush him, and he shall carry away armies as with a flood, and many shall fall down slain.
Waɗanda suke ci daga tanadin sarki za su yi ƙoƙari su hallaka shi; za a share mayaƙansa, kuma za a kashe mutane masu yawa a yaƙin.
27 And [as for] both the kings, their hearts [are set] upon mischief, and they shall speak lies at one table; but it shall not prosper; for yet the end is for a [fixed] time.
Sarakunan nan biyu sun sa mugunta a ransu. Za su zauna a tebur guda su yi ta shara wa juna ƙarya, amma a banza, gama lokacin da aka ƙayyade bai yi ba tukuna.
28 And he shall return to his land with much substance; and his heart [shall be] against the holy covenant; and he shall perform [great deeds], and return to his own land.
“Sarkin Arewa zai koma ƙasarsa da dukiya mai girma, amma zuciyarsa za tă yi gāba da tsattsarkan alkawari. Zai ɗauki mataki a kan wannan abu sa’an nan yă koma ƙasarsa.
29 At the [set] time he shall return, and shall come into the south, but the last [expedition] shall [not] be as the first.
“A ƙayyadadden lokaci zai sāke kai wa Kudu hari, amma a wannan karo abin da zai faru zai sha bamban daga abin da ya faru can baya.
30 For the Citians issuing forth shall come against him, and he shall be brought low, and shall return, and shall be incensed against the holy covenant: and he shall do [thus], and shall return, and have intelligence with them that have forsaken the holy covenant.
Jiragen ruwa yammancin bakin teku za su yi gāba da shi, zuciyarsa kuwa za tă yi sanyi. Sa’an nan zai juya ya huce haushinsa a kan tsattsarkan alkawari. Zai komo yă nuna jinƙai ga waɗanda suka juya wa tsattsarkan alkawari baya.
31 And seeds shall spring up out of him, and they shall profane the sanctuary of strength, and they shall remove the perpetual [sacrifice], and make the abomination desolate.
“Mayaƙansa za su taso su ƙazantar da kagarar haikali za su kuma kawar da hadaya ta kullum. Sa’an nan za su kafa abin banƙyama da yake lalatarwa.
32 And the transgressors shall bring about a covenant by deceitful ways: but a people knowing their God shall prevail, and do [valiantly].
Ta wurin daɗin baki zai gurɓata waɗannan da suka karya alkawari, amma mutanen da suka san Allahnsu za su yi tsayin daka su yi jayayya da shi.
33 And the intelligent of the people shall understand much: yet they shall fall by the sword, and by flame, and by captivity, and by spoil of [many] days.
“Waɗanda suke da hikima za su wayar da kan mutane da yawa, duk da haka za a kashe su da takobi, waɗansu da wuta, a washe waɗansu a kai su bauta.
34 And when they are weak they shall be helped with a little help: but many shall attach themselves to them with treachery.
Sa’ad da suka fāɗi, za su sami ɗan taimako, mutane da yawa za su haɗa kai da su, amma da munafunci.
35 And [some] of them that understand shall fall, to try them as with fire, and to test [them], and that they may be manifested at the time of the end, for the matter [is] yet for a [set] time.
Waɗansu masu hikima za su yi tuntuɓe, don a tsabtacce su, a tsarkake su, su yi tsab, har matuƙar da aka ƙayyade ta yi.
36 And he shall do according to his will, and the king shall exalt and magnify himself against every god, and shall speak great swelling words, and shall prosper until the indignation shall be accomplished: for it is coming to an end.
“Sarkin zai yi abin da ya ga dama. Zai ɗaukaka yă kuma girmama kansa gaba da kowane allah zai kuma faɗa munanan abubuwa a kan Allahn alloli. Zai yi nasara har sai lokacin hukunci ya cika, gama abin da aka ƙaddara zai cika.
37 And he shall not regard any gods of his fathers, nor the desire of women, neither shall he regard any deity: for he shall magnify himself above all.
Ba zai kula da alloli iyayensa ba ko wanda mata suke sha’awa, balle ma yă ga darajar wani allah, amma zai ɗaukaka kansa gaba da su duka.
38 And he shall honor the god of forces on his place: and a god whom his fathers knew not he shall honor with gold, and silver, and precious stones, and desirable things.
A maimakonsu, zai ɗaukaka allahn kagarai; allahn da kakanninsa ba su ko sani ba, shi ne zai miƙa masa zinariya, da azurfa, da duwatsu masu daraja, da abubuwa masu tsada.
39 And he shall do [thus] in the strong places of refuge with a strange god, and shall increase his glory: and he shall subject many to them, and shall distribute the land in gifts.
Zai kai wa kagarai mafi ƙarfi hari da taimakon baƙon allah zai kuma girmama waɗanda suka yarda da shi zai ba su girma, ya kuma shugabantar da su a kan mutane da yawa, zai raba musu ƙasa ta zama ladansu.
40 And at the end of the time he shall conflict with the king of the south: and the king of the north shall come against him with chariots, and with horsemen, and with many ships; and they shall enter into the land: and he shall break in pieces, and pass on:
“A lokaci ƙarshe sarkin Kudu zai tasar masa da yaƙi, sarkin Arewa kuwa zai tunzura, yă tasar masa da kekunan yaƙi da mahayan dawakai, da jiragen ruwa da yawa. Zai ratsa ƙasashe, yă ci su da yaƙi, yă wuce.
41 and he shall enter into the land of beauty, and many shall fail: but these shall escape out of his hand, Edom, and Moab, and the chief of the children of Ammon.
Zai kuma mamaye Kyakkyawa Ƙasa. Ƙasashe masu yawa za su fāɗi, amma Edom, Mowab da kuma shugabannin Ammon za su kuɓuta daga hannunsa.
42 And he shall stretch forth [his] hand over the land; and the land of Egypt shall not escape.
Zai fadada mulkinsa har zuwa ƙasashe masu yawa; Masar ma ba za tă tsira ba.
43 And he shall have the mastery over the secret [treasures] of gold and silver, and over all the desirable [possessions] of Egypt, and of the Libyans and Ethiopians in their strongholds.
Zai mallaki dukiyoyi na zinariya, da na azurfa, da dukan abubuwa masu tsada na Masar. Zai kuma ci Libiyawa da Kush da yaƙi.
44 But rumors and anxieties out of the east and from the north shall trouble him; and he shall come with great wrath to destroy many.
Amma labari daga gabas da arewa za su firgita shi, shi kuwa zai ci gaba da yin yaƙi da zafi, yă karkashe mutane da yawa, yă shafe su.
45 And he shall pitch the tabernacle of his palace between the seas in the holy mountain of beauty: [but] he shall come to his portion, and there is none to deliver him.
Zai kafa tentin mulkinsa tsakanin tekunan da suke a kyakkyawan tsauni mai tsarki. Duk da haka zai zo ga ƙarshensa, kuma babu wanda zai taimake shi.

< Daniel 11 >