< Kings I 29 >

1 And the Philistines gather all their armies to Aphec, and Israel encamped in Aendor, which is in Jezrael.
Filistiyawa suka tattara dukan rundunoninsu a Afek. Isra’ila kuwa suka yi sansani kusa da maɓulɓular da take Yezireyel.
2 And the lords of the Philistines went on by hundreds and thousands, and David and his men went on in the rear with Anchus.
Sa’ad da sarakuna Filistiyawa suke wucewa da rundunarsu na mutum ɗari-ɗari da na dubu-dubu. Dawuda da mutanensa suna biye a baya tare da Akish.
3 And the lords of the Philistines said, Who [are] these that pass by? And Anchus said to the captains of the Philistines, [Is] not this David the servant of Saul king of Israel? He has been with us some time, even this second year, and I have not found any fault in him from the day that he attached himself to me even until this day.
Komandodin Filistiyawa suka ce, “Waɗannan Ibraniyawa kuma fa?” Akish ya ce, “Wannan shi ne Dawuda hafsan Shawulu, sarkin Isra’ila. Yana nan tare da ni shekara guda ke nan. Ban kuwa taɓa samunsa da wani lahani ba tun daga ranar da ya bar Shawulu.”
4 And the captains of the Philistines were displeased at him, and they say to him, Send the man away, and let him return to his place, where you did set him; and let him not come with us to the war, and let him not be a traitor in the camp: and wherewith will he be reconciled to his master? Will it not be with the heads of those men?
Amma komandodin Filistiyawa suka yi fushi, suka ce, “Ka sa mutumin nan yă koma zuwa wurin da ka ba shi yă zauna. Ba zai bi mu zuwa wurin yaƙi ba. Yana iya juya a kanmu lokacin yaƙin. Zai iya yin amfani da wannan zarafi yă ciccire kawunanmu don yă faranta wa maigidansa rai?
5 [Is] not this David whom they celebrated in dances, saying, Saul has struck his thousands, and David his ten thousands?
Tuna fa, ba shi ne Dawuda ɗin da ake girmama da rawa da waƙoƙi ana cewa, “‘Shawulu ya kashe dubbai, Dawuda kuwa dubbun dubbai ba’?”
6 And Anchus called David, and said to him, [As] the Lord lives, you [are] right and approved in my eyes, and [so is] your going out and your coming in with me in the army, and I have not found [any] evil to charge against you from the day that you came to me until this day: but you are not approved in the eyes of the lords.
Saboda haka Akish ya kira Dawuda ya ce masa, “Muddin Ubangiji yana a raye, na amince da kai tun daga ranar da ka zo wurina har yă zuwa yau, ban same ka da wani laifi ba, na kuma yi farin ciki in sa ka a cikin sojojina don ka yi mini aiki. Amma masu mulki nawa ba su yarda da kai ba.
7 Now then return and go in peace, thus you shall not do evil in the sight of the lords of the Philistines.
Sai ka juya ka koma ka isa lafiya ba tare da ɓata wa masu mulkin Filistiyawa rai ba.”
8 And David said to Anchus, What have I done to you? and what have you found in your servant from the [first] day that I was before you even until this day, that I should not come and war against the enemies of the lord my king?
Dawuda ya ce wa Akish, “Me na yi? Ka taɓa samun bawanka da laifi tun daga ranar da na zo har zuwa yanzu? Ina dalilin da ba zan tafi tare da kai in yaƙi maƙiyin ranka yă daɗe, sarki ba?”
9 And Anchus answered David, I know that you [are] good in my eyes, but the lords of the Philistines say, He shall not come with us to the war.
Akish ya ce, “A ganina kai marar laifi ne kamar mala’ikan Allah, duk da haka shugabannin sojojin Filistiyawa sun ce, ‘Ba zai tafi yaƙi tare da mu ba.’
10 Now then rise up early in the morning, you and the servants of your lord that are come with you, and go to the place where I appointed you, and entertain no evil thought in your heart, for you [are] good in my sight: and rise early for your journey when it is light, and depart.
Ka tashi da sassafe, kai da bayin shugabanka da suka zo tare da kai. Da gari ya waye sai ku kama hanya.”
11 So David arose early, he and his men, to depart and guard the land of the Philistines: and the Philistines went up to Jezrael to battle.
Gari na wayewa tun da sassafe Dawuda da mutanensa suka tashi suka kama hanyar komawa ƙasar Filistiyawa. Filistiyawa kuwa suka haura zuwa Yezireyel.

< Kings I 29 >