< Psalms 114 >

1 When Israel went out of Egypt, the house of Jacob from a people of strange language;
Sa’ad da Isra’ila ya fito daga Masar, gidan Yaƙub daga mutane masu baƙon harshe,
2 Judah was his sanctuary, [and] Israel his dominion.
Yahuda ya zama wuri mai tsarki na Allah, Isra’ila mallakarsa.
3 The sea saw [it], and fled: Jordan was driven back.
Teku ya kalla ya kuma gudu, Urdun ya juye da baya;
4 The mountains skipped like rams, [and] the little hills like lambs.
duwatsu suka yi tsalle kamar raguna, tuddai kamar tumaki.
5 What [ailed] thee, O thou sea, that thou fleddest? thou Jordan, [that] thou wast driven back?
Me ya sa, ya teku, kika gudu, Ya Urdun, ka juya baya,
6 Ye mountains, [that] ye skipped like rams; [and] ye little hills, like lambs?
ku duwatsu, kuka yi tsalle kamar raguna, ku tuddai, kamar tumaki?
7 Tremble, thou earth, at the presence of the Lord, at the presence of the God of Jacob;
Ki yi rawar jiki, ya duniya, a gaban Ubangiji, a gaban Allah na Yaƙub,
8 Which turned the rock [into] a standing water, the flint into a fountain of waters.
wanda ya juye dutse ya zama tafki, dutse mai ƙarfi zuwa maɓulɓulan ruwa.

< Psalms 114 >