< Luke 24 >

1 Now upon the first day of the week, very early in the morning, they came unto the tomb, bringing the spices which they had prepared, and certain others with them.
Da sassafe a ranar farko ta mako, matan suka je kabarin, da kayan ƙanshin da suka shirya.
2 And they found the stone rolled away from the tomb.
Suka iske an riga an gungurar da dutsen daga bakin kabarin.
3 And they entered in, and found not the body of the Lord Jesus.
Amma da suka shiga ciki, ba su iske jikin Ubangiji Yesu ba.
4 And it came to pass, as they were much perplexed thereabout, behold, two men stood by them in shining garments:
Yayinda suna cikin tunani a kan wannan, nan take, ga waɗansu mutum biyu tsaye kusa da su, sanye da kaya masu ƙyalli, kamar walƙiya.
5 And as they were afraid, and bowed down their faces to the earth, they said unto them, Why seek all of you the living among the dead?
A cikin tsoro, matan suka fāɗi da fuskokinsu a ƙasa, amma mutanen suka ce musu, “Me ya sa kuke neman mai rai a cikin matattu?
6 He is not here, but has risen: remember how he spoke unto you when he was yet in Galilee,
Ba ya nan, ya tashi! Ku tuna yadda ya gaya muku tun yana tare da ku a Galili cewa,
7 Saying, The Son of man must be delivered into the hands of sinful men, and be crucified, and the third day rise again.
‘Dole a ba da Ɗan Mutum ga hannun masu zunubi, a kuma gicciye shi, a rana ta uku kuma a tashe shi.’”
8 And they remembered his words, (rhema)
Sai suka tuna da maganarsa.
9 And returned from the tomb, and told all these things unto the eleven, and to all the rest.
Da suka dawo daga kabarin, sai suka faɗa wa Sha Ɗayan nan da sauransu, dukan waɗannan abubuwa.
10 It was Mary Magdalene and Joanna, and Mary the mother of James, and other women that were with them, which told these things unto the apostles.
Matan da suka gaya wa manzannin waɗannan abubuwa su ne, Maryamu Magdalin, da Yowanna, da Maryamu uwar Yaƙub, da waɗansu da suke tare da su.
11 And their words (rhema) seemed to them as idle tales, and they believed them not.
Amma ba su gaskata matan ba, domin sun ɗauki kalmominsu wani zancen banza ne.
12 Then arose Peter, and ran unto the tomb; and stooping down, he beheld the linen clothes laid by themselves, and departed, wondering in himself at that which was come to pass.
Duk da haka, Bitrus ya tashi a guje zuwa kabarin. Da ya sunkuya, sai ya ga ƙyallayen lilin kaɗai a kwance. Sai ya koma yana tunani a ransa, a kan abin da ya faru.
13 And, behold, two of them went that same day to a village called Emmaus, which was from Jerusalem about threescore furlongs.
A wannan rana kuma, biyu daga cikinsu suna tafiya zuwa wani ƙauye, da ake kira Emmawus, da suke kusan mil bakwai daga Urushalima.
14 And they talked together of all these things which had happened.
Suna magana da juna a kan dukan abubuwan da suka faru.
15 And it came to pass, that, while they communed together and reasoned, Jesus himself drew near, and went with them.
Da suna magana, kuma suna tattauna waɗannan abubuwa da junansu, sai Yesu da kansa ya zo yana tafiya tare da su.
16 But their eyes were held that they should not know him.
Amma ba a ba su ikon gane shi ba.
17 And he said unto them, What manner of communications (logos) are these that all of you have one to another, as all of you walk, and are sad?
Sai ya tambaye, su ya ce, “Mene ne kuke tattaunawa da juna a cikin tafiyarku?” Suka tsaya shiru, da damuwa a fuskarsu.
18 And the one of them, whose name was Cleopas, answering said unto him, Are you only a stranger in Jerusalem, and have not known the things which are come to pass there in these days?
Ɗaya daga cikinsu, mai suna Kiliyobas, ya tambaye shi ya ce, “Ashe, kai baƙo ne a Urushalima, da ba ka san abubuwan da suka faru a can, a cikin kwanakin nan ba?”
19 And he said unto them, What things? And they said unto him, Concerning Jesus of Nazareth, which was a prophet mighty in deed and word (logos) before God and all the people:
Sai ya yi tambaya, “Waɗanne abubuwa?” Suka amsa suka ce, “Game da Yesu Banazare. Shi annabi ne, mai iko ne kuma cikin ayyukansa da maganarsa, a gaban Allah da kuma dukan mutane.
20 And how the chief priests and our rulers delivered him to be condemned to death, and have crucified him.
Manyan firistoci da masu mulkinmu sun ba da shi a yi masa hukuncin mutuwa, suka kuwa gicciye shi.
21 But we trusted that it had been he which should have redeemed Israel: and beside all this, to day is the third day since these things were done.
Amma da, muna sa zuciya cewa, shi ne wanda zai fanshi Isra’ila. Bugu da ƙari kuma yau kwana uku ke nan tun da wannan abin ya faru.
22 Yea, and certain women also of our company made us astonished, which were early at the tomb;
Har wa yau, waɗansu daga cikin matanmu sun ba mu mamaki. Sun je kabarin da sassafen nan,
23 And when they found not his body, they came, saying, that they had also seen a vision of angels, which said that he was alive.
amma ba su sami jikinsa ba. Sun dawo sun faɗa mana cewa, sun ga wahayi na mala’iku, da suka ce yana da rai.
24 And certain of them which were with us went to the tomb, and found it even so as the women had said: but him they saw not.
Sa’an nan, waɗansu abokanmu suka je kabarin, suka kuma tarar da kome kamar yadda matan suka faɗa, amma shi, ba su gan shi ba.”
25 Then he said unto them, O fools, and slow of heart to believe all that the prophets have spoken:
Sai ya ce musu, “Ashe, ku marasa azanci ne, masu nauyin zuciyar gaskata, da dukan abin da annabawa suka faɗa!
26 Ought not Christ to have suffered these things, and to enter into his glory?
Ai, dole Kiristi yă sha waɗannan wahalolin, kafin yă shiga ɗaukakarsa.
27 And beginning at Moses and all the prophets, he expounded unto them in all the scriptures the things concerning himself.
Sai ya fara bayyana musu daga Musa da dukan Annabawa, abin da dukan Nassi ya faɗa a kansa.”
28 And they drew nigh unto the village, where they went: and he made as though he would have gone further.
Da suka yi kusa da ƙauyen da za su, sai Yesu ya yi kamar zai ci gaba.
29 But they constrained him, saying, Abide with us: for it is toward evening, and the day is far spent. And he went in to tarry with them.
Amma suka matsa masa suka ce, “Sauka wurinmu, don dare ya kusa, rana ta kusa fāɗuwa.” Sai ya sauka wurinsu.
30 And it came to pass, as he sat at food with them, he took bread, and blessed it, and brake, and gave to them.
Da ya zauna a tebur tare da su, sai ya ɗauki burodi, ya yi godiya, ya kakkarya ya fara ba su.
31 And their eyes were opened, and they knew him; and he vanished out of their sight.
Sa’an nan idanunsu suka buɗe, suka gane shi. Sai ya ɓace musu.
32 And they said one to another, Did not our heart burn within us, while he talked with us by the way, and while he opened to us the scriptures?
Suka tambayi juna, “Ashe, shi ya sa zukatanmu suka kuna a cikinmu, sa’ad da yake magana da mu a hanya, yana bayyana mana Nassi.”
33 And they rose up the same hour, and returned to Jerusalem, and found the eleven gathered together, and them that were with them,
Suka tashi nan da nan suka koma Urushalima. A can suka sami Sha Ɗayan nan da waɗanda suke tare da su a wuri ɗaya,
34 Saying, The Lord has risen indeed, and has appeared to Simon.
suna cewa, “Gaskiya ne! Ubangiji ya tashi, ya kuma bayyana ga Siman”
35 And they told what things were done in the way, and how he was known of them in breaking of bread.
Sai su biyun nan suka ba da labarin abin da ya faru a hanya, da kuma yadda suka gane Yesu yayinda ya kakkarya burodin.
36 And as they thus spoke, Jesus himself stood in the midst of them, and says unto them, Peace be unto you.
Suna cikin wannan zance, sai ga Yesu da kansa tsaye a tsakiyarsu. Sai ya ce musu, “Salama a gare ku!”
37 But they were terrified and affrighted, and supposed that they had seen a spirit. (pneuma)
Suka firgita, suka tsorota, suna tsammani fatalwa ce suka gani.
38 And he said unto them, Why are all of you troubled? and why do thoughts arise in your hearts?
Sai ya ce musu, “Don me kuke damuwa, kuke kuma shakka a zuciyarku?
39 Behold my hands and my feet, that it is I myself: handle me, and see; for a spirit (pneuma) has not flesh and bones, as all of you see me have.
Ku duba hannuwana da ƙafafuna. Ai, ni ne da kaina! Ku taɓa ni ku ji, ai, fatalwa ba ta da nama da ƙashi, yadda kuke gani nake da su.”
40 And when he had thus spoken, he showed them his hands and his feet.
Da ya faɗi haka, sai ya nuna musu hannuwansa da ƙafafunsa.
41 And while they yet believed not for joy, and wondered, he said unto them, Have all of you here any food?
Kuma har yanzu, suna cikin rashin gaskatawa, saboda murna da mamaki, sai ya tambaye su, “Kuna da abinci a nan?”
42 And they gave him a piece of a broiled fish, and of an honeycomb.
Suka ba shi ɗan gasasshen kifi,
43 And he took it, and did eat before them.
ya karɓa ya ci a gabansu.
44 And he said unto them, These are the words (logos) which I spoke unto you, while I was yet with you, that all things must be fulfilled, which were written in the law of Moses, and in the prophets, and in the psalms, concerning me.
Ya ce musu, “Wannan shi ne abin da na gaya muku tun ina tare da ku cewa, dole a cika kome da aka rubuta game da ni, a cikin Dokar Musa, da Annabawa, da kuma Zabura.”
45 Then opened he their understanding, that they might understand the scriptures,
Sai ya wayar da tunaninsu don su fahimci Nassi.
46 And said unto them, Thus it is written, and thus it was essential for Christ to suffer, and to rise from the dead the third day:
Ya ce musu, “Wannan shi ne abin da aka rubuta, cewa dole Kiristi yă sha wahala, a rana ta uku kuma yă tashi daga matattu.
47 And that repentance and remission of sins should be preached in his name among all nations, beginning at Jerusalem.
Kuma a cikin sunansa za a yi wa’azin tuba da gafarar zunubai, ga dukan ƙasashe. Za a kuwa fara daga Urushalima.
48 And all of you are witnesses of these things.
Ku ne shaidun waɗannan abubuwa.
49 And, behold, I send the promise of my Father upon you: but tarry all of you in the city of Jerusalem, until all of you be imbued with power from on high.
Zan aika muku da abin da Ubana ya yi alkawari. Amma ku dakata a birnin tukuna, sai an rufe ku da iko daga sama.”
50 And he led them out as far as to Bethany, and he lifted up his hands, and blessed them.
Bayan ya kai su waje kusa da Betani, sai ya ɗaga hannuwansa ya sa musu albarka.
51 And it came to pass, while he blessed them, he was parted from them, and carried up into heaven.
Yana cikin sa musu albarka, sai ya rabu da su. Aka ɗauke shi zuwa cikin sama.
52 And they worshipped him, and returned to Jerusalem with great joy:
Sai suka yi masa sujada, suka koma Urushalima cike da murna sosai.
53 And were continually in the temple, praising and blessing God. Amen.
Sai suka ci gaba da zama a cikin haikalin, suna yabon Allah.

< Luke 24 >