< Psalms 1 >

1 Blessed is the man that walks not in the counsel of the ungodly, nor stands in the way of sinners, nor sits in the seat of the scornful.
Mai farin ciki ne mutumin da ba ya aiki da shawarar mugaye ko yă yi abin da masu zunubi suke yi ko yă zauna tare da masu yin ba’a.
2 But his delight is in the law of the LORD; and in his law does he meditate day and night.
Amma yana jin daɗin bin dokar Ubangiji, kuma yana ta nazarinta dare da rana.
3 And he shall be like a tree planted by the rivers of water, that brings forth his fruit in his season; his leaf also shall not wither; and whatever he does shall prosper.
Yana kama da itacen da aka shuka kusa da maɓulɓulan ruwa, wanda yake ba da amfani a daidai lokaci wanda kuma ganyensa ba sa bushewa. Duk abin da yake yi, yakan yi nasara.
4 The ungodly are not so: but are like the chaff which the wind drives away.
Ba haka yake da mugaye ba! Su kamar yayi ne da iska take kwashewa.
5 Therefore the ungodly shall not stand in the judgment, nor sinners in the congregation of the righteous.
Saboda haka mugaye ba za su iya tsayawa a shari’a ba, balle a sami masu zunubi a taron adalai.
6 For the LORD knows the way of the righteous: but the way of the ungodly shall perish.
Gama Ubangiji yana lura da yadda adalai suke yin abubuwa, amma ayyukan mugaye za su kai su ga hallaka.

< Psalms 1 >