< 2 Timothy 1 >

1 Paul, an apostle of Jesus Christ by the will of God, according to the promise of life which is in Christ Jesus,
Bulus, manzon Almasihu Yesu ta wurin nufin Allah, bisa ga alkawarin rai da ke cikin Almasihu Yesu,
2 To Timothy, my dearly beloved son: Grace, mercy, and peace, from God the Father and Christ Jesus our Lord.
zuwa ga Timoti, kaunataccen da: Alheri, jinkai, da salama daga Allah Uba da Almasihu Yesu Ubangijinmu.
3 I thank God, whom I serve from my forefathers with pure conscience, that without ceasing I have remembrance of you in my prayers night and day;
Na gode wa Allah, wanda na ke bautawa tun daga kakannina, da lamiri mai tsabta, sa'adda na ke tuna wa da kai cikin addu'o'ina koyaushe (dare da rana).
4 Greatly desiring to see you, being mindful of your tears, that I may be filled with joy;
Sa'adda na tuna da hawayenka, na yi marmarin ganinka, saboda in cika da farin ciki.
5 When I call to remembrance the unfeigned faith that is in you, which dwelled first in your grandmother Lois, and your mother Eunice; and I am persuaded that in you also.
An tunashshe ni game da sahihiyar bangaskiyarka, wadda ta samo asali daga kakarka Loyis da mahaifiyarka Afiniki. Na kuma tabbata ta na zaune a cikinka.
6 Why I put you in remembrance that you stir up the gift of God, which is in you by the putting on of my hands.
Wannan shine dalilin da ni ke tunashshe ka cewa ka sake rura baiwar Allah da ke cikinka wadda ka samu sa'adda na dibiya maka hannuwana.
7 For God has not given us the spirit of fear; but of power, and of love, and of a sound mind.
Domin Allah bai ba mu ruhun tsoro ba, amma na iko da kauna da kamun kai.
8 Be not you therefore ashamed of the testimony of our Lord, nor of me his prisoner: but be you partaker of the afflictions of the gospel according to the power of God;
Saboda haka kada ka ji kunyar shaida ga me da Ubangijinmu, ko ni, Bulus, daurarrensa. Maimakon haka, ka zama a shirye ka sha wahala domin bishara bisa ga ikon Allah.
9 Who has saved us, and called us with an holy calling, not according to our works, but according to his own purpose and grace, which was given us in Christ Jesus before the world began, (aiōnios g166)
Allah ne ya cecemu kuma ya kira mu da kira mai tsarki. Ya yi wannan, ba ta wurin ayyukanmu ba, amma ta wurin shirinsa da alherinsa. Ya ba mu wadannan abubuwan a cikin Almasihu Yesu kafin farkon zamanai. (aiōnios g166)
10 But is now made manifest by the appearing of our Savior Jesus Christ, who has abolished death, and has brought life and immortality to light through the gospel:
Amma yanzu an bayyana ceton Allah ta wurin bayyanuwar mai cetonmu Almasihu Yesu. Almasihu ne ya kawo karshen mutuwa ya kuma kawo rai marar karshe da ya bayyana ta wurin bishara.
11 Whereunto I am appointed a preacher, and an apostle, and a teacher of the Gentiles.
Domin wannan, an zabe ni mai wa'azi, manzo da mallami zuwa ga al'ummai.
12 For the which cause I also suffer these things: nevertheless I am not ashamed: for I know whom I have believed, and am persuaded that he is able to keep that which I have committed to him against that day.
Domin wannan dalili na ke shan wahalar wadannan abubuwa. Amma ban ji kunya ba, domin na san shi, wanda na gaskanta. Na sakankance zai iya adana abinda na mika masa har zuwa ranan nan.
13 Hold fast the form of sound words, which you have heard of me, in faith and love which is in Christ Jesus.
Ka adana misalin amintattun sakwanni da ka ji daga gare ni, ta wurin bangaskiya da kauna da ke cikin Almasihu Yesu.
14 That good thing which was committed to you keep by the Holy Ghost which dwells in us.
Abu mai kyau da Allah ya danka maka, ka tsare shi ta wurin Ruhu Mai Tsarki, da ke zaune a cikinmu.
15 This you know, that all they which are in Asia be turned away from me; of whom are Phygellus and Hermogenes.
Ka dai sani, dukkan wadanda su ke zama a Asiya sun juya mani baya. A cikin kungiyar akwai Fijalas da Harmajanas.
16 The Lord give mercy to the house of Onesiphorus; for he oft refreshed me, and was not ashamed of my chain:
Bari Ubangiji ya yi wa iyalin Onisifaras jinkai, domin ya na yawan yi mani hidima, kuma ba ya jin kunyar sarkata.
17 But, when he was in Rome, he sought me out very diligently, and found me.
Maimakon haka, sa'adda ya ke a Roma, ya neme ni da kokarin gaske, ya kuma same ni.
18 The Lord grant to him that he may find mercy of the Lord in that day: and in how many things he ministered to me at Ephesus, you know very well.
Bari Ubangiji ya sa, ya sami jinkai daga gare shi a wannan rana. Dukkan hanyoyin da ya taimake ni a kasar Afisa, kun sani sarai.

< 2 Timothy 1 >