< Psalms 142 >

1 Maschil of David, when he was in the cave; a Prayer. With my voice I cry unto the LORD; with my voice I make supplication unto the LORD.
Maskil ne ta Dawuda. Sa’ad da yake cikin kogo. Addu’a ce. Na yi kuka mai ƙarfi ga Ubangiji; na tā da muryata ga Ubangiji neman jinƙai.
2 I pour out my complaint before Him, I declare before Him my trouble;
Na kawo gunagunina a gabansa; a gabansa na faɗa wahalata.
3 When my spirit fainteth within me — Thou knowest my path — in the way wherein I walk have they hidden a snare for me.
Sa’ad da ƙarfina ya kāre a cikina, kai ne wanda ya san hanyata. A hanyar da nake tafiya mutane sun kafa mini tarko.
4 Look on my right hand, and see, for there is no man that knoweth me; I have no way to flee; no man careth for my soul.
Duba ta damata ka gani; babu wanda ya kula da ni. Ba ni da mafaka; babu wanda ya kula da raina.
5 I have cried unto Thee, O LORD; I have said: 'Thou art my refuge, my portion in the land of the living.'
Na yi kuka gare ka, ya Ubangiji; Na ce, “Kai ne mafakata, rabona a ƙasar masu rai.”
6 Attend unto my cry; for I am brought very low; deliver me from my persecutors; for they are too strong for me.
Ka saurari kukata, gama ina cikin matsananciyar bukata; ka cece ni daga waɗanda suke fafarata, gama sun fi ni ƙarfi sosai.
7 Bring my soul out of prison, that I may give thanks unto Thy name; the righteous shall crown themselves because of me; for Thou wilt deal bountifully with me.
Ka’yantar da ni daga kurkuku, don in yabi sunanka. Ta haka masu adalci za su taru kewaye da ni saboda alherinka gare ni.

< Psalms 142 >