< Psalms 129 >

1 A Song of Ascents. 'Much have they afflicted me from my youth up', let Israel now say;
Waƙar haurawa. Sun yi mini danniya ƙwarai tun ina ƙarami, bari Isra’ila yă ce,
2 'Much have they afflicted me from my youth up; but they have not prevailed against me.
sun yi mini danniya ƙwarai tun ina ƙarami, amma ba su yi nasara a kaina ba.
3 The plowers plowed upon my back; they made long their furrows.
Manoma sun nome bayana suka yi kunyoyinsu da tsayi.
4 The LORD is righteous; He hath cut asunder the cords of the wicked.'
Amma Ubangiji mai adalci ne; ya’yantar da ni daga igiyoyin mugaye.
5 Let them be ashamed and turned backward, all they that hate Zion.
Bari dukan waɗanda suke ƙin Sihiyona a juye da su baya da kunya.
6 Let them be as the grass upon the housetops, which withereth afore it springeth up;
Bari su zama kamar ciyawa a kan rufi, wadda takan bushe kafin tă yi girma;
7 Wherewith the reaper filleth not his hand, nor he that bindeth sheaves his bosom.
da ita mai girbi ba ya iya cika hannuwansa, balle wanda yake tarawa yă cika hannuwansa.
8 Neither do they that go by say: 'The blessing of the LORD be upon you; we bless you in the name of the LORD.'
Kada masu wuce su ce, “Albarkar Ubangiji ta kasance a kanku; muna sa muku albarka a cikin sunan Ubangiji.”

< Psalms 129 >