< Judges 4 >

1 And the children of Israel again did that which was evil in the sight of the LORD, when Ehud was dead.
Bayan rasuwar Ehud, Isra’ilawa suka sāke aikata mugayen ayyuka a gaban Ubangiji.
2 And the LORD gave them over into the hand of Jabin king of Canaan, that reigned in Hazor; the captain of whose host was Sisera, who dwelt in Harosheth-goiim.
Saboda haka Ubangiji ya sayar da su ga Yabin sarkin Kan’ana wanda yake mulki a Hazor. Shugaban mayaƙansa shi ne Sisera, wanda yake zaune a Haroshet Haggoyim.
3 And the children of Israel cried unto the LORD; for he had nine hundred chariots of iron; and twenty years he mightily oppressed the children of Israel.
Domin Yabin sarkin Kan’ana yana da kekunan yaƙin ƙarfe ɗari tara, ya ji wa Isra’ilawa ƙwarai har shekara ashirin, sai suka yi kuka ga Ubangiji, don taimako.
4 Now Deborah, a prophetess, the wife of Lappidoth, she judged Israel at that time.
A lokacin Debora annabiya, matar Laffidot ce take bi da Isra’ila.
5 And she sat under the palm-tree of Deborah between Ramah and Beth-el in the hill-country of Ephraim; and the children of Israel came up to her for judgment.
Takan yi zaman shari’a a ƙarƙashin Dabinon Debora tsakanin Rama da Betel, a ƙasar tudu ta Efraim, Isra’ilawa kuwa sukan zo wurinta don tă yi musu shari’a.
6 And she sent and called Barak the son of Abinoam out of Kedesh-naphtali, and said unto him: 'Hath not the LORD, the God of Israel, commanded, saying: Go and draw toward mount Tabor, and take with thee ten thousand men of the children of Naphtali and of the children of Zebulun?
Sai ta aika a kira mata Barak ɗan Abinowam daga Kedesh a Naftali, ta ce masa, “Ubangiji, Allah na Isra’ila ya umarce ka, ‘Je ka, ka ɗauki mutane Naftali da na Zebulun dubu goma tare da kai, ka yi jagoransu zuwa Dutse Tabor.
7 And I will draw unto thee to the brook Kishon Sisera, the captain of Jabin's army, with his chariots and his multitude; and I will deliver him into thy hand.
Zan jawo Sisera, shugaban mayaƙan Yabin, da keken yaƙinsa da mayaƙansa zuwa Kogin Kishon in ba da su a hannunku.’”
8 And Barak said unto her: 'If thou wilt go with me, then I will go; but if thou wilt not go with me, I will not go.'
Barak ya ce, “In kika tafi tare da ni, zan tafi; amma in ba ki zo tare da ni ba, ba zan tafi ba.”
9 And she said: 'I will surely go with thee; notwithstanding the journey that thou takest shall not be for thy honour; for the LORD will give Sisera over into the hand of a woman.' And Deborah arose, and went with Barak to Kedesh.
Debora ta ce, “To, shi ke nan, zan tafi tare da kai. Amma saboda yadda ka ɗauki wannan batun, darajar ba za tă zama taka ba, gama Ubangiji zai ba da Sisera a hannun mace.” Saboda haka Debora ta tafi tare da Barak zuwa Kedesh,
10 And Barak called Zebulun and Naphtali together to Kedesh; and there went up ten thousand men at his feet; and Deborah went up with him.
a can Barak ya kira Zebulun da Naftali. Mutum dubu goma suka kuma bi shi, Debora kuma tana tare da shi.
11 Now Heber the Kenite had severed himself from the Kenites, even from the children of Hobab the father-in-law of Moses, and had pitched his tent as far as Elon-bezaanannim, which is by Kedesh.
To, Heber Bakene ya riga ya bar Keniyawa, zuriyar Hobab, ɗan’uwan matar Musa, ya kafa tentinsa wajen babban itace a Za’anannim kusa da Kedesh.
12 And they told Sisera that Barak the son of Abinoam was gone up to mount Tabor.
Sa’ad da aka gaya wa Sisera cewa Barak ɗan Abinowam ya haura zuwa dutsen Tabor,
13 And Sisera gathered together all his chariots, even nine hundred chariots of iron, and all the people that were with him, from Harosheth-goiim, unto the brook Kishon.
sai Sisera ya tattara keken yaƙinsa na ƙarfe ɗari tara wuri ɗaya da dukan mutanen da suke tare da shi daga Haroshet Haggoyim zuwa Kogin Kishon.
14 And Deborah said unto Barak: 'Up; for this is the day in which the LORD hath delivered Sisera into thy hand; is not the LORD gone out before thee?' So Barak went down from mount Tabor, and ten thousand men after him.
Sa’an nan Debora ta ce wa Barak, “Je ka! Wannan ita ce ranar da Ubangiji ya ba da Sisera a hannunka. Ba Ubangiji ya riga ya sha gabanka?” Saboda haka Barak ya gangara zuwa Dutsen Tabor, da mutum dubu goma biye da shi.
15 And the LORD discomfited Sisera, and all his chariots, and all his host, with the edge of the sword before Barak; and Sisera alighted from his chariot, and fled away on his feet.
Da matsowar Barak, Ubangiji ya murƙushe Sisera da dukan sarakunansa da mayaƙansa da takobi, Sisera kuwa ya gudu da ƙafa ya bar keken yaƙinsa.
16 But Barak pursued after the chariots, and after the host, unto Harosheth-goiim; and all the host of Sisera fell by the edge of the sword; there was not a man left.
Amma Barak ya bi keken yaƙin da mayaƙan har Haroshet Haggoyim. Aka karkashe dukan mayaƙan Sisera ba ko ɗayan da ya tsira.
17 Howbeit Sisera fled away on his feet to the tent of Jael the wife of Heber the Kenite; for there was peace between Jabin the king of Hazor and the house of Heber the Kenite.
Amma Sisera, ya tsere da ƙafa zuwa tentin Yayel, matar Heber Bakene, domin suna da abokantaka da Yabin sarkin Hazor da kuma kabilar Heber Bakene.
18 And Jael went out to meet Sisera, and said unto him: 'Turn in, my lord, turn in to me; fear not.' And he turned in unto her into the tent, and she covered him with a rug.
Yayel ta fito ta taryi Sisera ta ce masa, “Ranka yă daɗe, ka shigo, ka shigo ciki. Kada ka ji tsoro.” Saboda haka ya shiga cikin tentinta, sai ta rufe shi da bargo.
19 And he said unto her: 'Give me, I pray thee, a little water to drink; for I am thirsty.' And she opened a bottle of milk, and gave him drink, and covered him.
Sai ya ce, “Ina roƙonki, ki ba ni ruwa in sha, ina jin ƙishirwa.” Sai ta buɗe salkar madara, ta ba shi ya sha, sai ta kuma rufe shi.
20 And he said unto her: 'Stand in the door of the tent, and it shall be, when any man doth come and inquire of thee, and say: Is there any man here? that thou shalt say: No.'
Ya ce mata, “Ki tsaya a ƙofar tenti, in wani ya zo ya tambaye ki, ‘Akwai wani a nan?’ Ki ce masa ‘a’a.’”
21 Then Jael Heber's wife took a tent-pin, and took a hammer in her hand, and went softly unto him, and smote the pin into his temples, and it pierced through into the ground; for he was in a deep sleep; so he swooned and died.
Amma Yayel, matar Heber, ta ɗauki turken tenti da guduma ta tafi wurinsa da sauri sa’ad da yake barci saboda gajiya. Ta kafa masa turken a gindin kunnensa ta haɗa shi da ƙasa, har ya mutu.
22 And, behold, as Barak pursued Sisera, Jael came out to meet him, and said unto him: 'Come, and I will show thee the man whom thou seekest.' And he came unto her; and, behold, Sisera lay dead, and the tent-pin was in his temples.
Sai ga Barak mai bin sawun Sisera, Yayel kuwa ta fito don marabtarsa, ta ce, “Shigo, zan nuna maka mutumin da kake nema.” Saboda haka ya shiga ciki tare da ita, sai ga Sisera kwance da turken a gindin kunnensa, matacce.
23 So God subdued on that day Jabin the king of Canaan before the children of Israel.
A ranar Allah ya yi kaca-kaca da Yabin, sarkin Kan’ana a gaban Isra’ila.
24 And the hand of the children of Israel prevailed more and more against Jabin the king of Canaan, until they had destroyed Jabin king of Canaan.
Isra’ilawa kuwa suka ƙara ƙarfi gāba da Yabin, sarkin Kan’aniyawa, har suka hallaka shi.

< Judges 4 >