< Luke 5 >

1 AND it came to pass, as the multitude were thronging upon him, in order to hear the word of God, that he was standing by the lake of Gennesaret:
Wata rana, Yesu yana tsaye a bakin Tafkin Gennesaret, mutane kuma suna ta matsawa kewaye da shi, domin su ji maganar Allah,
2 and he saw two vessels a-ground near the lake: but the fishermen were gone out of them, and washing their nets.
sai ya hangi jiragen ruwa biyu a bakin tafkin, waɗanda masu kamun kifi suka bari suna wankin abin kamun kifinsu.
3 Then he went on board one of the vessels, which was Simon’s, and desired him to put off a little from the land: and sitting down, he taught the multitudes out of the vessel.
Sai ya shiga ɗaya jirgin ruwan da yake na Siman, ya kuma roƙe shi yă tura shi kaɗan daga gaci. Sai ya zauna a jirgin ruwan, ya koyar da mutane daga ciki.
4 And when he ceased speaking, he said to Simon, Go off into deep water, and shoot your nets for a draught.
Da ya gama magana, sai ya ce wa Siman, “Ka tuƙa jirgin zuwa inda akwai zurfi, ka saukar da abin kamun kifinka ka kama kifi.”
5 And Simon answering, said unto him, Sir, we have been toiling all night, and have taken nothing: but at thy command I will shoot the net.
Siman ya amsa ya ce, “Ranka yă daɗe, duk dare mun yi ta fama ba mu kama kome ba, amma tun da ka ce haka, zan saki abin kamun kifin.”
6 And having done so, they inclosed a prodigious multitude of fishes; and their net was broken.
Da suka yi haka, sai suka kama kifi da yawa, har abin kamun kifinsu suka fara tsintsinkewa.
7 And they made signals to their partners in the other vessels, that they should come to their assistance. And they came, and filled both the vessels, so that they were ready to founder.
Sai suka kira abokansu a ɗaya jirgin, su zo su taimake su, suka kuwa zo. Suka cika jiragen biyu da kifi cif, har jiragen suka fara nutsewa.
8 Then Simon Peter seeing it, fell down on his knees before Jesus, saying, Go from me; for I am a sinful man, O Lord!
Da Siman Bitrus ya ga wannan, sai ya fāɗi a gaban Yesu ya ce, “Rabu da ni, Ubangiji. Ni mai zunubi ne!”
9 For amazement had seized on him, and on all who were with him, at the draught of fishes which they had taken:
Gama mamaki ya kama shi da abokansa duka, saboda yawan kifin da suka kama.
10 as also on James and John the sons of Zebedee, who were partners with Simon. And Jesus said to Simon, Fear not: henceforward thou shalt catch men.
Yaƙub da Yohanna,’ya’yan Zebedi, abokan aikin Siman su ma suka yi mamaki. Sai Yesu ya ce wa Siman, “Kada ka ji tsoro, daga yanzu za ka riƙa kama mutane ne.”
11 And when they had brought their vessels on shore, they left all, and followed him.
Sai suka jawo jiragen ruwansu zuwa gaci, suka bar kome da kome, suka bi shi.
12 And it came to pass as he was just at one of the cities, behold, a man full of leprosy! and seeing Jesus, he fell on his face, and besought him, saying, Lord, if thou wilt, thou canst make me clean.
Yayinda Yesu yake ɗaya daga cikin garuruwan nan, sai ga wani mutum wanda kuturta ta ci ƙarfinsa. Da ganin Yesu, sai ya fāɗi da fuskarsa a ƙasa, ya roƙe shi ya ce, “Ubangiji, in ka yarda, kana iya ka tsabtacce ni.”
13 And he stretching out his hand touched him, saying, I will: be thou cleansed. And instantly the leprosy departed from him.
Yesu ya miƙa hannunsa ya taɓa mutumin ya ce, “Na yarda, ka zama da tsabta!” Nan da nan, sai kuturtar ta rabu da shi.
14 And he commanded him to tell no man: but go shew thyself to the priest, and offer for thy purification, as Moses enjoined, for a testimony unto them.
Sai Yesu ya umarce shi ya ce, “Kada ka gaya wa kowa, amma ka tafi ka nuna kanka ga firist, ka kuma miƙa hadayu da Musa ya umarta, saboda tsarkakewarka ta zama shaida a gare su.”
15 Now the discourse concerning him more and more spread through the country: and vast multitudes came together to hear him, and to be cured by him of their disorders.
Duk da haka, labarinsa ya ƙara bazuwa sosai, har taron mutane suka dinga zuwa don jinsa, da kuma neman warkarwa daga cututtukansu.
16 But he himself was in the desert for retirement and prayer.
Amma Yesu sau da yawa, yakan keɓe kansa zuwa wuraren da ba kowa, yă yi addu’a.
17 And on a certain day it happened that he was teaching, and there were sitting Pharisees, and doctors of the law, who had come from every town of Galilee, and Judea, and Jerusalem: and the power of the Lord for healing them was exercised.
Wata rana, da yake cikin koyarwa, waɗansu Farisiyawa da malaman dokoki waɗanda suka zo daga kowane ƙauye a Galili, Yahudiya da Urushalima kuwa suna zaune. Ikon Ubangiji yana nan don yă warkar da masu ciwo.
18 And behold, men carried on a couch a man who was a paralytic; and sought to bring him into the house, and to place him before him.
Sai ga waɗansu mutane suka kawo wani shanyayye a kan tabarma. Suka yi ƙoƙari su shigar da shi cikin gidan, domin su kwantar da shi a gaban Yesu.
19 And not discovering by what means they could introduce him, because of the crowd, they went up to the roof, and through the tiling let him down with his little couch into the midst, before Jesus.
Da suka ga babu hanyar da za su bi saboda taron, sai suka haura rufin, suka saukar da shi a kan tabarmarsa, ta bakin ramin da suka huda a rufin, suka ajiye shi a tsakiyar taron, a gaban Yesu.
20 And seeing their faith, he saith to him, Man, thy sins are forgiven thee.
Da Yesu ya ga bangaskiyarsu, sai ya ce, “Saurayi, an gafarta maka zunubanka.”
21 And the scribes and Pharisees began to reason, saying, Who is this that speaketh blasphemies? Who can forgive sins but God alone?
Farisiyawa da malaman dokoki suka fara yin tunani a zukatansu, “Wane ne wannan mutum da yake saɓo haka? Wa zai iya gafarta zunubai, in ba Allah kaɗai ba?”
22 And Jesus knowing their reasoning, in reply said to them, Why do ye reason in your hearts?
Yesu ya san abin da suke tunani, sai ya yi tambaya ya ce, “Don me kuke tunanin waɗannan abubuwa a zukatanku?
23 for which is the easier? to say, Thy sins are forgiven; or to say, Arise and walk?
Wanne ya fi sauƙi, a ce, ‘An gafarta maka zunubanka,’ ko kuma a ce, ‘Tashi, ka yi tafiya’?
24 But that ye may know that the Son of man hath authority upon earth to forgive sins, (he saith to the paralytic, ) I say to thee, Arise, and take up thy couch, and go into thy house.
Amma domin ku san cewa Ɗan Mutum yana da iko a duniya ya gafarta zunubai.” Sai ya ce wa shanyayyen, “Na ce maka, tashi, ɗauki tabarmarka ka tafi gida.”
25 And instantly he rose up before them, took up that on which he had lain, and went away to his house, giving glory to God.
Nan da nan, ya tashi tsaye a gabansu, ya ɗauki tabarmar da yake kwance a kai, ya tafi gida, yana yabon Allah.
26 And an extacy of admiration seized upon them all, and they glorified God; and they were filled with awe, saying, We have seen wondrously strange things to-day.
Kowa ya yi mamaki, ya kuma yabi Allah. Suka cika da tsoro, suna cewa, “Mun ga abubuwan banmamaki yau.”
27 And after these things he went out, and saw a farmer of the taxes, named Levi, sitting at the custom-house: and he said unto him, Follow me.
Bayan wannan, sai Yesu ya fita, ya ga wani mai karɓar haraji, mai suna Lawi, yana zaune a wurin da ake karɓar haraji. Yesu ya ce masa, “Bi ni.”
28 And leaving all behind, he rose, and followed him.
Sai Lawi ya tashi, ya bar kome da kome, ya bi shi.
29 And Levi made him a great entertainment at his house and there was a great number of publicans and others, sitting at table with them.
Sai Lawi ya shirya wa Yesu wani babban liyafa a gidansa. Wani babban taron na masu karɓar haraji, tare da waɗansu suna cin abinci tare da su.
30 And their scribes and Pharisees murmured against his disciples, saying, Why do ye eat and drink with publicans and sinners?
Amma Farisiyawa da malaman dokokin da suke a ƙungiyarsu, suka yi wa almajiransa gunaguni, suna cewa, “Don me kuke ci, kuke sha tare da masu karɓar haraji da masu zunubi?”
31 And Jesus answering said unto them, They who are well, have no need of a physician: but they who have illness.
Yesu ya amsa musu ya ce, “Ai, masu lafiya ba sa bukatar likita, sai dai marasa lafiya.
32 I came not to call righteous men, but sinners, to repentance.
Ban zo don in kira masu adalci ba, sai dai masu zunubi zuwa ga tuba.”
33 Then said they unto him, Why do the disciples of John observe frequent fasts, and make prayers; but thine are eating and drinking?
Suka ce masa, “Almajiran Yohanna sukan yi azumi da addu’a, haka ma almajiran Farisiyawa, amma naka sai ci da sha.”
34 And he said unto them, Can you make the children of the bridechamber fast, as long as the bridegroom is with them?
Yesu ya amsa ya ce, “Za ku iya sa abokan ango yin azumi yayinda yake tare da su?
35 But the days will come, when the bridegroom shall be taken away from them, then shall they fast in those days.
Amma lokaci yana zuwa, da za a ɗauke ango daga gare su. A waɗancan kwanakin ne za su yi azumi.”
36 Then he spake a parable unto them, No man putteth a patch of new cloth on an old garment; but if otherwise, both the new makes a rent, and the patch from the new is not of a piece with the old.
Sai ya faɗa musu wannan misali ya ce, “Ba wanda yakan yage ƙyalle daga sabuwar riga ya yi wa tsohuwar riga faci. In ya yi haka, zai yage sabuwar rigar, kuma facin daga sabuwar ba zai dace da tsohuwar rigar ba.
37 And no man putteth new wine into old bottles; for if he doth, the new wine will burst the bottles, and it will itself be spilled, and the bottles be destroyed.
Kuma ba wanda yakan zuba sabon ruwan inabi a cikin tsofaffin salkuna. In ya yi haka, sabon ruwan inabi zai farfashe salkunan, ruwan inabin yă zube, salkunan kuma su lalace.
38 But new wine should be put into new bottles; then both are preserved.
A’a, sai dai a zuba sabon ruwan inabi a sababbin salkuna.
39 And no man drinking old wine, immediately desires new: for he saith, The old is better.
Kuma ba wanda yakan so shan sabon ruwan inabi bayan ya sha tsohon, don yakan ce, ‘Ai, tsohon ya fi kyau.’”

< Luke 5 >