< Luke 1 >

1 SINCE many have attempted to compose a narrative of facts, confirmed to us by the fullest evidence:
Mutane da yawa sun ɗau niyyar rubuta labarin abubuwan da aka cika a cikinmu,
2 exactly as they delivered them to us, who were eve witnesses from the first, and ministers of the word;
kamar yadda muka karɓe su daga waɗanda tun farko shaidu ne da kuma masu hidimar bishara.
3 it seemed right to me also, having obtained accurate knowledge of all things from above, to write to thee in regular order, most excellent Theophilus,
Saboda haka, da yake ni da kaina na binciko kome a hankali daga farko, na ga ya yi kyau in rubuta maka labarin dalla-dalla, ya mafifici Tiyofilus,
4 to the intent that thou mayest clearly know the certainty of those matters, concerning which thou hast been instructed.
don ka san tabbacin abubuwan da aka koyar da kai.
5 There was in the days of Herod, the king of Judea, a certain priest named Zacharias, of the course of Abiah: and his wife of the daughters of Aaron, and her name Elisabeth.
A lokacin da Hiridus ne yake sarautar Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na sashin firistoci gidan Abiya. Matarsa Elizabet ma’yar zuriyar Haruna ce.
6 And they were both righteous before God, walking in all the commandments and ordinances of the Lord blameless.
Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna kuma bin umarnan Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi.
7 And they had no child, because Elizabeth was barren, and both were far advanced in years.
Sai dai ba su da’ya’ya, domin Elizabet bakararriya ce; kuma dukansu biyu sun tsufa.
8 And it came to pass, as he discharged his priestly office in the order of his periodical ministration before God,
Wata rana da lokacin aikin firistoci na sashen Zakariya na yin hidima ya kewayo, yana kuma cikin hidimarsa ta firist a gaban Allah,
9 according to the custom of the priesthood, it fell to his lot to burn the incense when he went into the temple of the Lord.
sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare.
10 And all the multitude of people was praying without, at the time of the burning the incense.
Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.
11 And an angel of the Lord appeared to him standing on the right side of the altar of incense.
Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare.
12 And Zacharias was agitated greatly at the sight, and fear fell upon him.
Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi.
13 But the angel said unto him, Fear not, Zacharias: for thy prayer is heard; and thy wife Elisabeth shall bring thee a son, and thou shalt call his name John.
Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna.
14 And it shall give thee joy and exultation; and many shall rejoice at his birth:
Zai zama abin murna da farin ciki a gare ka, mutane da yawa kuwa za su yi murna don haihuwarsa,
15 for he shall be great in the sight of the Lord; and he shall never drink wine, nor any intoxicating liquor; and he shall be filled with the Holy Ghost, even from his mother’s womb.
gama zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba kuwa zai taɓa shan ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun haihuwa.
16 And many of the children of Israel shall he turn unto the Lord, their God.
Shi ne zai juye mutanen Isra’ila da yawa zuwa wurin Ubangiji Allahnsu.
17 And he shall go forth before him in the spirit and power of Elias, to convert the hearts of fathers with their children, and the disobedient to the wisdom of the just; to prepare a people ready for the Lord.
Zai sha gaban Ubangiji, a ruhu da kuma iko irin na Iliya, domin yă juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, marasa biyayya kuma ga zama masu biyayya don yă kintsa mutane su zama shiryayyu domin Ubangiji.”
18 And Zacharias said to the angel, By what shall I know this? for I am old, and my wife far advanced in her age.
Sai Zakariya ya tambayi mala’ikan ya ce, “Yaya zan tabbatar da wannan? Ga ni tsoho, matana kuma ta kwana biyu.”
19 And the angel answering said to him, I am Gabriel, that stand in the presence of God; and I have been sent to speak to thee, and to proclaim these glad tidings to thee.
Mala’ikan ya ce, “Ni ne Jibra’ilu. Ina tsaya a gaban Allah, an kuma aiko ni in yi maka magana, in kuma faɗa maka wannan labari mai daɗi.
20 And behold, thou shalt be dumb, and unable to speak, until that day when these things shall come to pass, because thou hast not believed my words, which shall be fulfilled at their exact time.
Yanzu za ka zama bebe, ba za ka ƙara iya magana ba sai ranar da wannan magana ta cika, saboda ba ka gaskata da kalmomina waɗanda za su zama gaskiya a daidai lokacinsu ba.”
21 And the people were waiting for Zacharias, and marvelled that he tarried so long in the temple.
Ana cikin haka, mutane suna jiran Zakariya, suna kuma mamaki me ya sa ya daɗe haka a cikin haikali.
22 And when he came out, he could not speak to them: and they perceived that he had seen a vision in the temple: for he himself made signs to them, and continued deaf and dumb.
Da ya fito, bai iya yin musu magana ba. Sai suka gane, ya ga wahayi ne a haikali, domin ya dinga yin musu alamu, amma ya kāsa yin magana.
23 And it came to pass, when the days of his ministry were fulfilled, he went to his own house.
Da lokacin hidimarsa ya cika, sai ya koma gida.
24 And after those days Elisabeth his wife conceived, and kept herself in retirement five months, saying,
Bayan wannan, matarsa Elizabet ta yi ciki, ta kuma riƙa ɓuya har wata biyar.
25 Thus hath the Lord dealt with me in the days in which he looked upon me to take away my reproach among men.
Sai ta ce, “Ubangiji ne ya yi mini wannan. A waɗannan kwanaki ya nuna tagomashinsa ya kuma kawar mini da kunya a cikin mutane.”
26 Now in the sixth month the angel Gabriel was sent from God into a city of Galilee, the name of which was Nazareth,
A wata na shida, sai Allah ya aiki mala’ika Jibra’ilu zuwa Nazaret, wani gari a Galili,
27 to a virgin of the house of David, betrothed to a man whose name was Joseph; and the virgin’s name was Mary.
gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu.
28 And the angel coming in to her said, All hail! O thou highly favoured one! the Lord is with thee: blessed art thou among women.
Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”
29 And when she saw him, she was greatly agitated at his address: and reasoned in herself what kind of salutation this could be.
Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka?
30 And the angel said unto her, Fear not, Mary, for thou hast found favour with God.
Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.
31 And, behold, thou shalt conceive in thy womb, and bring forth a son, and thou shalt call his name JESUS.
Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu.
32 He shall be great, and shall be called the Son of the Highest: and the Lord God will give him the throne of David his father;
Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda,
33 and he shall reign over the house of Jacob for ever, and of his kingdom there shall be no end. (aiōn g165)
zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.” (aiōn g165)
34 And Mary said, How shall this be, seeing I know not man?
Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”
35 And the angel answering said unto her, The Holy Ghost shall come upon thee, and the power of the Most High shall overshadow thee; wherefore also the Holy One that shall be born of thee, shall be called the Son of God.
Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.
36 And, behold, Elisabeth thy cousin, she also hath conceived in her old age: and this is the fifth month of pregnancy with her who was called barren.
’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida.
37 For there is nothing impossible with God.
Gama ba abin da zai gagari Allah.”
38 Then said Mary, Behold a servant of the Lord, be it to me according to thy declaration. And the angel departed from her.
Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.
39 Then Mary arose in those days, and went with haste into the hill country, to a city of Judah,
A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya,
40 and entered into the house of Zachariah, and saluted Elisabeth.
inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet.
41 And it came to pass, when Elisabeth heard the salutation of Mary, the babe leaped for joy in her womb; and Elisabeth was filled with the Holy Ghost:
Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki.
42 and she exclaimed with a loud voice, and said, Blessed art thou among women, and blessed is the fruit of thy womb.
Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa!
43 And whence is this favour shewn me, that the mother of my Lord should come to me?
Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina?
44 For, lo! as the voice of thy salutation reached my ears, the babe leaped for joy in my womb.
Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna.
45 And blessed is she that hath believed; for there shall be a fulfilment of the things told her from the Lord.
Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”
46 And Mary said, My soul doth magnify the Lord,
Sai Maryamu ta ce, “Raina yana ɗaukaka Ubangiji
47 and my spirit hath exulted in God my Saviour:
ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,
48 for he hath looked upon the lowly state of his maid-servant: for, lo! henceforth shall all generations pronounce me blessed.
gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa. Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,
49 For the Mighty One hath done great things for me; and holy is his name.
gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa, sunansa labudda Mai Tsarki ne.
50 And his mercy is upon those who fear him, from generation to generation.
Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa, daga zamani zuwa zamani.
51 He hath displayed strength from his arm; he hath scattered the proud in the imagination of their hearts.
Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa; ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.
52 He hath cast down potentates from the throne, and hath exalted the lowly.
Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.
53 He hath filled the hungry with good things; and the rich he hath sent empty away.
Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa amma ya sallami mawadata hannu wofi.
54 He hath succoured Israel his servant, that he might be mindful of mercy for ever; (aiōn g165)
Ya taimaki bawansa Isra’ila, yana tunawa yă nuna jinƙai
55 as he had spoken to our fathers, to Abraham, and to his seed.
ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.” (aiōn g165)
56 And Mary abode with her about three months, and returned unto her home.
Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.
57 Now Elisabeth’s time was up that she should be delivered; and she brought a son.
Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa.
58 And her neighbours and her relations heard, that the Lord had magnified his mercy upon her; and they congratulated her.
Maƙwabtanta da’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.
59 And it came to pass, on the eighth day they came to circumcise the child; and they called him after the name of his father, Zacharias.
A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,
60 And his mother spake and said, No; but he shall be called John.
amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”
61 And they said to her, There is not one among thy relations, who is called by this name.
Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”
62 And they made signs to his father, what he would have him called.
Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.
63 And desiring a writing tablet, he wrote, saying, John is his name. And they were all surprised.
Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
64 Instantly then his mouth was opened, and his tongue loosed, and he burst out in praises to God.
Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.
65 And great awe fell on all those who dwelt around them: and in all the mountainous country of Judea, all these circumstances were the subject of conversation.
Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.
66 And all who heard them laid them up in their hearts, saying, Well! what a child will this be! And the hand of the Lord was with him.
Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.
67 And Zacharias his father was filled with the Holy Ghost, and prophesied, saying,
Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,
68 Blessed be the Lord the God of Israel; for he hath visited and wrought redemption for his people;
“Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.
69 and hath raised up a horn of salvation for us in the house of his servant David:
Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda
70 as he spake by the mouth of his holy prophets, which have been from the beginning: (aiōn g165)
(yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki), (aiōn g165)
71 even preservation from our enemies, and from the hand of all that hate us;
cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu
72 to perform mercy towards our fathers, and to remember his own holy covenant:
don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
73 the oath which he sware to Abraham our father,
rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,
74 to give us, that we, secure from fear, rescued from the hands of our enemies, should serve him,
don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,
75 in righteousness and holiness before him, all the days of our life.
cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.
76 And thou, child, shalt be called the prophet of the Most High; for thou shalt go before the face of the Lord to prepare his ways;
“Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki; gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,
77 to give the knowledge of salvation to his people, by the remission of their sins,
don ka sanar da mutanensa ceto, ta wurin gafarar zunubansu,
78 through the bowels of mercy of our God; with which he hath visited us, as the dawn of the morning from on high,
saboda jinƙai na Allahnmu mai ƙauna, hasken nan na ceto zai ɓullo mana daga sama,
79 to illumine those who sat in darkness, and in the shadow of death, to direct our feet into the way of peace.
don yă haskaka a kan waɗanda suke zama cikin duhu, da kuma cikin inuwar mutuwa, don yă bi da ƙafafunmu a hanyar salama.”
80 And the child grew, and became mighty in spirit, and was in the deserts until the days of his public exhibition to Israel.
Yaron kuwa ya yi girma ya kuma ƙarfafa a ruhu; ya zauna a hamada sai lokacin da ya fito a fili ga mutanen Isra’ila.

< Luke 1 >