< Zephaniah 1 >

1 The word of the Lord, which came vnto Zephaniah ye sonne of Cushi, the sonne of Gedaliah, the sonne of Amariah, the sonne of Hizkiah, in the dayes of Iosiah, the sonne of Amon King of Iudah.
Domin mai bi da kaɗe-kaɗe. A kan kayan kiɗi masu tsirkiyata. Maganar Ubangiji da ta zo wa Zefaniya ɗan Kushi, ɗan Gedaliya, ɗan Amariya, ɗan Hezekiya, a zamanin Yosiya ɗan Amon sarkin Yahuda.
2 I will surely destroy all things from off the land, saith the Lord.
“Zan hallaka kome a fuskar duniya,” in ji Ubangiji.
3 I will destroy man and beast: I wil destroy the foules of the heauen, and the fishes of the sea, and ruines shalbe to the wicked, and I will cut off man from off the land, saith the Lord.
“Zan hallaka mutane da dabbobi; zan kuma hallaka tsuntsayen sama da kifayen teku, da gumakan da suke sa mugaye su yi tuntuɓe.” “Sa’ad da zan kawar da mutum daga fuskar duniya,” in ji Ubangiji.
4 I will also stretch out mine hand vpon Iudah, and vpon all the inhabitants of Ierusalem, and I wil cut off the remnant of Baal from this place, and the name of the Chemarims with ye Priestes,
“Zan miƙa hannuna gāba da Yahuda da kuma dukan mazaunan Urushalima. Zan datse raguwar Ba’al daga wannan wuri, da sunayen firistocin gumaka da na marasa sanin Allah,
5 And them that worship the hoste of heauen vpon the house tops, and them that worship and sweare by the Lord, and sweare by Malcham,
waɗanda suka rusuna a kan rufin ɗaki don su yi sujada ga rundunar taurari. Waɗanda suka rusuna suka kuma yi rantsuwa da sunan Ubangiji suke kuma rantsuwa da sunan Molek.
6 And them that are turned backe from the Lord, and those that haue not sought the Lord, nor inquired for him.
Waɗanda suka juya daga bin Ubangiji, ba sa kuma neman Ubangiji ko su nemi nufinsa.”
7 Be stil at the presence of the Lord God: for the day of the Lord is at hand: for the Lord hath prepared a sacrifice, and hath sanctified his ghests.
Ku yi shiru a gaban Ubangiji Mai Iko Duka, gama ranar Ubangiji ta yi kusa. Ubangiji ya shirya hadaya; ya kuma tsarkake waɗanda ya gayyato.
8 And it shalbe in the day of the Lords sacrifice, that I will visite the princes and the Kings children, and all such as are clothed with strange apparell.
“A ranar hadayar Ubangiji zan hukunta sarakuna da kuma’ya’yan sarakuna da duk waɗanda suke sanye da rigunan ƙasashen waje.
9 In the same day also will I visite all those that dance vpon the threshold so proudly, which fill their masters houses by crueltie and deceite.
A wannan rana zan hukunta dukan waɗanda suke kauce taka madogarar ƙofa, waɗanda suke cika haikalin allolinsu da rikici da ruɗu.
10 And in that day, saith the Lord, there shall be a noise, and cry from the fishgate, and an howling from the second gate, and a great destruction from the hilles.
“A wannan rana,” in ji Ubangiji, “Za a ji kuka daga Ƙofar Kifi, kururuwa daga Sabon Mazauni, da kuma amo mai ƙarfi daga tuddai.
11 Howle ye inhabitants of the lowe place: for the companie of the marchants is destroyed: all they that beare siluer, are cut off.
Ku yi kururuwa, ku da kuke zaune a yankin kasuwa; za a hallaka dukan’yan kasuwanku, dukan waɗanda suke kasuwanci da azurfa za su lalace.
12 And at that time will I searche Ierusalem with lightes, and visite the men that are frosen in their dregges, and say in their heartes, The Lord will neither doe good nor doe euill.
A wannan lokaci zan bincike Urushalima da fitilu in kuma hukunta waɗanda ba su kula ba, waɗanda suke kamar ruwan inabin da aka bar a ƙasan tukunya, waɗanda suke tsammani, ‘Ubangiji ba zai yi kome ba nagari ko mummuna.’
13 Therefore their goods shall be spoyled, and their houses waste: they shall also build houses, but not inhabite them, and they shall plant vineyards, but not drinke the wine thereof.
Za a washe dukiyarsu, a rurrushe gidajensu. Za su gina gidaje amma ba za su zauna a ciki ba; za su shuka inabi amma ba za su sha ruwansa ba.”
14 The great day of the Lord is neere: it is neere, and hasteth greatly, euen the voyce of the day of the Lord: the strong man shall cry there bitterly.
Babbar ranar Ubangiji ta yi kusa, ta yi kusa kuma tana zuwa da sauri. Ku saurara! Kukan ranar Ubangiji za tă yi zafi, za a ji kururuwan jarumi a can.
15 That day is a day of wrath, a day of trouble and heauinesse, a day of destruction and desolation, a day of obscuritie and darkenesse, a day of cloudes and blackenesse,
Ranan nan za tă zama ranar fushi, rana ce ta baƙin ciki da azaba, rana ce ta tashin hankali da lalacewa, ranar duhu baƙi ƙirin, ranar gizagizai da baƙin duhu,
16 A day of the trumpet and alarme against the strong cities, and against the hie towres.
rana ce ta busa ƙaho da kururuwar yaƙi gāba da birane masu mafaka, da kuma kusurwar hasumiyoyi.
17 And I will bring distresse vpon men, that they shall walke like blind men, because they haue sinned against the Lord, and their blood shall be powred out as dust, and their flesh as the dongue.
“Zan kawo baƙin ciki a kan mutane za su kuma yi tafiya kamar makafi, domin sun yi wa Ubangiji zunubi. Za a zubar da jininsu kamar ƙura kayan cikinsu kuma kamar najasa.
18 Neither their siluer nor their golde shalbe able to deliuer them in ye day of the Lords wrath, but the whole lande shalbe deuoured by the fire of his ielousie: for hee shall make euen a speedie riddance of all them that dwell in the land.
Azurfarsu ko zinariyarsu ba za su iya cetonsu ba a ranar fushin Ubangiji.” A cikin zafin kishinsa za a hallaka dukan duniya gama zai kawo ƙarshen dukan mazaunan duniya nan da nan.

< Zephaniah 1 >