< Zechariah 3 >

1 And he shewed mee Iehoshua the hie Priest, standing before the Angel of the Lord, and Satan stoode at his right hand to resist him.
Sa’an nan ya nuna mini Yoshuwa babban firist a tsaye a gaban mala’ikan Ubangiji, Shaiɗan kuma yana tsaye a damansa don yă tuhume shi.
2 And the Lord said vnto Satan, The Lord reprooue thee, O Satan: euen the Lord that hath chosen Ierusalem, reprooue thee. Is not this a brand taken out of the fire?
Ubangiji ya ce wa Shaiɗan, “Ubangiji ya tsawata maka, Shaiɗan! Ubangiji wanda ya zaɓi Urushalima, ya tsawata maka! Ashe, mutumin nan ba shi ne sandar da take ƙonewa da aka ciro daga cikin wuta ba?”
3 Nowe Iehoshua was clothed with filthie garments, and stoode before the Angel.
Yanzu an sa wa Yoshuwa tufafi masu dauda sa’ad da yake tsaye a gaban mala’ikan.
4 And he answered and spake vnto those that stoode before him, saying, Take away the filthie garments from him. And vnto him hee saide, Behold, I haue caused thine iniquitie to depart from thee, and I wil clothe thee with change of raiment.
Mala’ikan ya ce wa waɗanda suke tsaye a gabansa, “Ku cire masa tufafinsa masu dauda.” Sai ya ce wa Yoshuwa, “Duba, na ɗauke zunubanka, zan sa maka tufafi masu tsada.”
5 And I saide, Let them set a faire diademe vpon his head. So they set a faire diademe vpon his head, and clothed him with garments, and the Angel of the Lord stoode by.
Sai na ce, “Sa masa rawani mai tsabta a kansa.” Aka sa masa rawani mai tsabta a kansa aka kuma sa masa tufafi yayinda mala’ikan Ubangiji yake tsaye a wurin.
6 And the Angel of the Lord testified vnto Iehoshua, saying,
Mala’ikan Ubangiji ya yi wa Yoshuwa wannan gargaɗi.
7 Thus saith the Lord of hostes, If thou wilt walke in my wayes, and keepe my watch, thou shalt also iudge mine House, and shalt also keepe my courtes, and I will giue thee place among these that stand by.
“Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki ya ce, ‘In za ka yi tafiya a hanyoyina ka kuma kiyaye abubuwan da nake so, za ka zama shugaban haikalina, ka kuma lura da ɗakunan shari’ata, zan kuma ba ka wuri cikin waɗannan da suke tsaye a nan.
8 Heare now, O Iehoshua the hie Priest, thou and thy fellowes that sit before thee: for they are monstruous persons: but behold, I wil bring forth the Branche my seruant.
“‘Ka saurara, ya babban firist Yoshuwa, kai da abokanka da suke zaune a gabanka, ku da kuke alamun abubuwan da za su zo. Zan kawo bawana, wanda yake Reshe.
9 For loe, the stone that I haue layd before Iehoshua: vpon one stone shalbe seuen eyes: beholde, I will cut out the grauing thereof, saith the Lord of hostes, and I will take away the iniquitie of this land in one day.
Dubi dutsen da na ajiye a gaban Yoshuwa! Akwai idanu bakwai a kan wannan dutse guda, zan kuma yi rubutu a kansa,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki, ‘zan kuma kawar da zunubin ƙasan nan a rana ɗaya.
10 In that day, saith the Lord of hostes, shall ye call euery man his neighbour vnder the vine, and vnder the figge tree.
“‘A wannan rana kowannenku zai gayyaci maƙwabcinsa yă zauna a ƙarƙashin itacen inabi da kuma na ɓaure,’ in ji Ubangiji Maɗaukaki.”

< Zechariah 3 >