< Ruth 4 >

1 Then went Boaz vp to the gate, and sate there, and beholde, the kinsman, of whome Boaz had spoken, came by: and he sayd, Ho, snch one, come, sit downe here. And he turned, and sate downe.
Ana cikin haka Bowaz ya haura zuwa ƙofar gari ya tafi ya zauna a can. Sa’ad da dangi mai fansan da ya yi zance ya iso, Bowaz ya ce, “Zo nan abokina ka zauna.” Saboda haka ya ratso ya zauna.
2 Then he tooke ten men of the Elders of the citie, and sayd, Sit ye downe here. And they sate downe.
Bowaz kuwa ya kira dattawa guda goma na garin ya ce, “Ku zauna a nan,” suka kuwa zauna.
3 And he said vnto ye kinsman, Naomi, that is come againe out of ye countrey of Moab, wil sell a parcel of land, which was our brother Elimelechs.
Sa’an nan ya ce wa dangin nan mai fansa, “Na’omi, wadda ta dawo daga Mowab, tana so ta sayar da filin da yake na ɗan’uwanmu Elimelek.
4 And I thought to aduertise thee, saying, Buy it before the assistants, and before the Elders of my people. If thou wilt redeeme it, redeeme it: but if thou wilt not redeeme it, tel me: for I know that there is none besides thee to redeeme it, and I am after thee. Then he answered, I wil redeeme it.
Na ga ya kamata in jawo hankalinka ga batun in kuma ba da shawara ka saye shi a gaban waɗannan da suke zazzaune a nan da kuma a gaban dattawan jama’a. In kana so ka fanshe shi, to, sai ka yi. Amma in ba za ka yi ba, sai ka faɗa mini, don in sani. Gama babu wani mai izinin yin haka sai kai, ni ne kuwa na biye.” Sai ya ce, “Zan fansa.”
5 Then said Boaz, What day thou buyest the field of the hand of Naomi, thou mnst also buy it of Ruth the Moabitesse the wife of the dead, to stirre vp the name of the dead, vpon his inheritance.
Sa’an nan Bowaz ya ce, “A ranar da ka saya filin daga Na’omi da kuma daga Rut mutuniyar Mowab, ka sayi gwauruwar marigayin nan, domin ka riƙe sunan marigayin da kuma kayansa.”
6 And the kinsman answered, I can not redeeme it, lest I destroy mine owne inheritance: redeeme my right to thee, for I can not redeeme it.
Da jin haka, sai dangin nan mai fansa ya ce, “To, ba zan iya fanshe shi ba don kada in yi wa nawa mallakar rauni. Za ka iya fanshe shi wa kanka. Ni dai ba zan iya ba.”
7 Now this was the maner beforetime in Israel, concerning redeeming and changing, for to stablish all things: a man did plucke off his shooe, and gaue it his neighbour, and this was a sure witnes in Israel.
(To, a kwanakin can a Isra’ila, domin a tabbatar da fansa da kuma musayar da mallaka, mutum zai cire takalminsa ya ba wa ɗayan. Wannan ita ce hanyar tabbatar da al’amarin a hukumance a cikin Isra’ila.)
8 Therefore the kinsman sayd to Boas, Buy it for thee: and he drew off his shooe.
Saboda haka dangin nan mai fansa ya ce wa Bowaz, “Saye shi wa kanka.” Sai ya cire takalminsa.
9 And Boaz sayd vnto the Elders and vnto all the people, Ye are witnesses this day, that I haue bought all that was Elimelechs, and all that was Chilions and Mahlons, of the hand of Naomi.
Sa’an nan Bowaz ya yi shela wa dattawa da kuma dukan mutane, “A yau ku ne shaidu cewa na saya daga Na’omi dukan mallakar Elimelek, Kiliyon da kuma Malon.
10 And moreouer, Ruth the Moabitesse the wife of Mahlon, haue I bought to be my wife, to stirre vp the name of the dead vpon his inheritance, and that the name of the dead be not put out from among his brethren, and from the gate of his place: ye are witnesses this day.
Na kuma ɗauki Rut mutuniyar Mowab, gwauruwar Malon a matsayin matata domin sunan mamaci da kuma mallakarsa yă ci gaba, domin kada sunansa yă ɓace daga cikin iyali ko daga tarihin gari. A yau ku ne shaidu!”
11 And all the people that were in the gate, and the Elders sayd, We are witnesses: the Lord make the wife that commeth into thine house, like Rahel and like Leah, which twaine did build the house of Israel: and that thou mayest doe worthily in Ephrathah, and be famous in Beth-lehem,
Sai dattawan da kuma dukan waɗanda suke a ƙofar suka ce, “Mu shaidu ne. Bari Ubangiji yă sa macen da take zuwa cikin gidanka ta zama kamar Rahila da Liyatu, waɗanda tare suka gina gidan Isra’ila. Bari ka sami martaba a cikin Efrata ka kuma zama sananne cikin Betlehem.
12 And that thine house be like the house of Pharez (whom Thamar bare vnto Iudah) of the seede which the Lord shall giue thee of this yong woman.
Ta wurin’ya’yan da Ubangiji zai ba ka ta wurin wannan mace, bari iyalinka yă zama kamar na Ferez, wanda Tamar ta haifa wa Yahuda.”
13 So Boaz tooke Ruth, and she was his wife: and when he went in vnto her, the Lord gaue that she conceiued, and bare a sonne.
Sai Bowaz ya ɗauki Rut ta kuwa zama matarsa. Sa’an nan ya kwana da ita, Ubangiji kuma ya sa ta yi ciki, ta haifi ɗa.
14 And the women sayd vnto Naomi, Blessed be the Lord, which hath not left thee this day without a kinsman, and his name shalbe continued in Israel.
Mata suka ce wa Na’omi, “Yabo ya tabbata ga Ubangiji, wanda a wannan rana bai bar ki ba tare da dangi mai fansa ba. Allah yă sa yă zama sananne a dukan Isra’ila!
15 And this shall bring thy life againe, and cherish thine olde age: for thy daughter in lawe which loueth thee, hath borne vnto him, and she is better to thee then seuen sonnes.
Zai sabunta rayuwarki yă adana ki a tsufanki. Gama surukarki wadda take ƙaunarki wadda kuma take mafi kyau gare ki fiye da’ya’ya maza bakwai, ta haife shi.”
16 And Naomi tooke the childe, and layde it in her lap, and became nource vnto it.
Sai Na’omi ta ɗauki yaron, ta kwantar da shi a cinyarta ta kuma kula da shi.
17 And the women her neighbours gaue it a name, saying, There is a childe borne to Naomi, and called the name thereof Obed: the same was the father of Ishai, the father of Dauid.
Matan da suke zama a wurin suka ce, “Na’omi ta sami yaro.” Suka kuwa ba shi suna Obed. Shi ne ya haifi Yesse, mahaifin Dawuda.
18 These now are ye generations of Pharez: Pharez begate Hezron,
Ga asalin zuriyar Ferez. Ferez shi ne mahaifin Hezron,
19 And Hezron begate Ram, and Ram begate Amminadab,
Hezron ya haifi Ram, Ram ya haifi Amminadab,
20 And Amminadab begate Nahshon, and Nahshon begate Salmah,
Amminadab ya haifi Nashon, Nashon ya haifi Salmon,
21 And Salmon begate Boaz, and Boaz begat Obed,
Salmon ya haifi Bowaz, Bowaz ya haifi Obed,
22 And Obed begate Ishai, and Ishai begate Dauid.
Obed ya haifi Yesse, Yesse kuwa ya haifi Dawuda.

< Ruth 4 >