< Revelation 15 >

1 And I sawe another signe in heauen, great and marueilous, seuen Angels, hauing the seuen last plagues: for by them is fulfilled the wrath of God.
Na ga wata babbar alama mai banmamaki a sama, mala’iku bakwai da annobai bakwai na ƙarshe, na ƙarshe, domin da su ne fushin Allah ya cika.
2 And I sawe as it were a glassie sea, mingled with fire, and them that had gotten victorie of the beast, and of his image, and of his marke, and of the number of his name, stand at the glassie sea, hauing the harpes of God,
Sai na ga abin da ya yi kamar tekun gilashi gauraye da wuta kuma tsaye kusa da teku, waɗanda suka ci nasara bisan dabbar da siffarta da bisan lambar sunanta. Suna riƙe da garayu waɗanda Allah ya ba su
3 And they sung the song of Moses the seruant of God, and the song of the Lambe, saying, Great and marueilous are thy workes, Lord God almightie: iust and true are thy wayes, King of Saints.
suka rera waƙar Musa bawan Allah da kuma waƙar Ɗan Ragon suna cewa, “Ayyukanka suna da girma da kuma banmamaki, ya Ubangiji Maɗaukaki. Al’amuranka suna da aminci da kuma gaskiya, ya Sarkin zamanai.
4 Who shall not feare thee, O Lord, and glorifie thy Name! for thou onely art holy, and all nations shall come and worship before thee: for thy iudgements are made manifest.
Wane ne ba zai ji tsoronka, yă kuma kawo ɗaukaka ga sunanka ba, ya Ubangiji? Gama kai kaɗai ne mai tsarki. Dukan al’ummai za su zo su yi sujada a gabanka, gama an bayyana ayyukan adalcinka.”
5 And after that, I looked, and beholde, the Temple of the tabernacle of testimonie was open in heauen.
Bayan wannan sai na duba, a cikin sama kuwa sai ga haikali, wato, tabanakul na Shaida, a buɗe.
6 And the seuen Angels came out of the Temple, which had the seuen plagues, clothed in pure and bright linnen, and hauing their breasts girded with golden girdles.
Daga cikin haikalin mala’iku bakwai tare da annobai bakwai suka fito. Suna saye da tufafin lilin masu tsabta masu walƙiya, suna kuma saye da ɗamarar zinariya a ƙirjinsu.
7 And one of the foure beastes gaue vnto the seuen Angels seuen golden vials full of the wrath of God, which liueth for euermore. (aiōn g165)
Sai ɗaya daga cikin halittu huɗun nan masu rai, ya ba wa mala’iku bakwai nan kwanonin zinariya bakwai cike da fushin Allah, wanda yake raye har abada abadin. (aiōn g165)
8 And the Temple was full of the smoke of the glory of God and of his power, and no man was able to enter into the Temple, till the seuen plagues of the seuen Angels were fulfilled.
Aka kuma cika haikalin da hayaƙi daga ɗaukakar Allah da kuma daga ikonsa, kuma ba wanda ya iya shiga haikalin sai da aka cika annobai bakwai nan na mala’iku bakwai.

< Revelation 15 >