< Psalms 72 >

1 A Psalme of Salomon. Give thy iudgements to the King, O God, and thy righteousnesse to the Kings sonne.
Ta Solomon. Ka tanada sarki da shari’arka ta gaskiya, ya Allah, ɗan sarki da adalcinka.
2 Then shall he iudge thy people in righteousnesse, and thy poore with equitie.
Zai shari’anta mutanenka da adalci, marasa ƙarfinka da shari’ar gaskiya.
3 The mountaines and the hilles shall bring peace to the people by iustice.
Duwatsu za su kawo wadata ga mutane, tuddai kuma su ba da amfani na adalci.
4 He shall iudge the poore of the people: he shall saue the children of the needie, and shall subdue the oppressor.
Zai kāre marasa ƙarfi a cikin mutane yă kuma cece’ya’yan masu bukata; zai murƙushe masu danniya.
5 They shall feare thee as long as the sunne and moone endureth, from generatio to generation.
Zai jimre muddin rana tana nan, muddin akwai wata, har dukan zamanai.
6 He shall come downe like the rayne vpon the mowen grasse, and as the showres that water the earth.
Zai zama kamar ruwan sama mai fāɗuwa a filin ciyayin da aka yanka, kamar yayyafi mai ba wa duniya ruwa.
7 In his dayes shall the righteous florish, and abundance of peace shalbe so long as the moone endureth.
A kwanakinsa adalai za su haɓaka wadata za tă yalwata har sai babu sauran wata.
8 His dominion shall be also from sea to sea, and from the Riuer vnto the endes of the land.
Zai yi mulki daga teku zuwa teku kuma daga Kogi zuwa iyakar duniya.
9 They that dwell in ye wildernes, shall kneele before him, and his enemies shall licke the dust.
Kabilun hamada za su rusuna a gabansa abokan gābansa kuwa za su lashe ƙura.
10 The Kings of Tarshish and of the yles shall bring presents: the Kings of Sheba and Seba shall bring giftes.
Sarakunan Tarshish da na bakin kogi masu nisa za su ba da gandu gare shi; sarakunan Sheba da Seba za su ba shi kyautai.
11 Yea, all Kings shall worship him: all nations shall serue him.
Dukan sarakuna za su rusuna masa kuma dukan al’ummai za su bauta masa.
12 For he shall deliuer the poore when he cryeth: the needie also, and him that hath no helper.
Gama zai ceci masu bukatan da suka yi kuka, marasa ƙarfin da ba su da mai taimako.
13 He shalbe mercifull to the poore and needie, and shall preserue the soules of the poore.
Zai ji tausayin gajiyayyu da masu bukata yă ceci masu bukata daga mutuwa.
14 He shall redeeme their soules from deceite and violence, and deare shall their blood be in his sight.
Zai kuɓutar da su daga danniya da rikici, gama jininsu yake a gabansa.
15 Yea, he shall liue, and vnto him shall they giue of the golde of Sheba: they shall also pray for him continually, and dayly blesse him.
Bari yă yi doguwar rayuwa! Bari a ba shi zinariya daga Sheba. Bari mutane su riƙa yin addu’a dominsa su kuma albarkace shi dukan yini.
16 An handfull of corne shall be sowen in the earth, euen in the toppe of the mountaines, and the fruite thereof shall shake like the trees of Lebanon: and the children shall florish out of the citie like the grasse of the earth.
Bari hatsi yă yalwata a duk fāɗin ƙasar; bari yă cika bisan tuddai. Bari’ya’yan itatuwansa su haɓaka kamar Lebanon; bari yă bazu kamar ciyayi a gona.
17 His name shall be for euer: his name shall indure as long as the sunne: all nations shall blesse him, and be blessed in him.
Bari sunansa yă dawwama har abada; bari yă ci gaba muddin rana tana nan. Dukan al’ummai za su sami albarka ta wurinsa, za su kuma ce da shi mai albarka.
18 Blessed be the Lord God, euen the God of Israel, which onely doeth wonderous things.
Yabo ya tabbata ga Ubangiji Allah, Allah na Isra’ila, wanda shi kaɗai ya aikata abubuwa masu banmamaki.
19 And blessed be his glorious Name for euer: and let all the earth be filled with his glorie. So be it, euen so be it.
Yabo ya tabbata ga sunansa mai ɗaukaka har abada; bari dukan duniya ta cika da ɗaukakarsa.
20 HERE END THE prayers of Dauid, the sonne of Ishai.
Wannan ya kammala addu’o’in Dawuda ɗan Yesse.

< Psalms 72 >