< Psalms 66 >

1 To him that excelleth. A song or Psalme. Rejoice in God, all ye inhabitants of the earth.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Waƙa. Zabura. Ku yi sowa ta farin ciki ga Allah, dukan duniya!
2 Sing forth the glory of his name: make his praise glorious.
Ku rera ɗaukaka ga sunansa; ku sa yabonsa yă zama da ɗaukaka!
3 Say vnto God, Howe terrible art thou in thy workes! through the greatnesse of thy power shall thine enemies be in subiection vnto thee.
Ku ce wa Allah, “Ayyukanka da banmamaki suke! Ikonka da girma yake har abokan gābanka suna durƙusa a gabanka.
4 All the worlde shall worship thee, and sing vnto thee, euen sing of thy Name. (Selah)
Dukan duniya sun rusuna a gabanka suna rera yabo gare ka, suna rera yabo ga sunanka.” (Sela)
5 Come and beholde the workes of God: he is terrible in his doing towarde the sonnes of men.
Ku zo ku ga abin da Allah ya yi, ayyukansa masu banmamaki a madadin mutum!
6 He hath turned the Sea into drie land: they passe through the riuer on foote: there did we reioyce in him.
Ya juya teku zuwa busasshiyar ƙasa, sun wuce cikin ruwaye da ƙafa, ku zo, mu yi farin ciki a cikinsa.
7 He ruleth the worlde with his power: his eyes beholde the nations: the rebellious shall not exalt them selues. (Selah)
Yana mulki har abada ta wurin ikonsa, idanunsa suna duban al’ummai, kada’yan tawaye su tayar masa. (Sela)
8 Prayse our God, ye people, and make the voyce of his prayse to be heard.
Ku yabi Allahnku, ya mutane, bari a ji ƙarar yabonsa;
9 Which holdeth our soules in life, and suffereth not our feete to slippe.
ya adana rayukanmu ya kuma kiyaye ƙafafunmu daga santsi.
10 For thou, O God, hast proued vs, thou hast tryed vs as siluer is tryed.
Gama kai, ya Allah, ka gwada mu; ka tace mu kamar azurfa.
11 Thou hast brought vs into the snare, and layed a strait chaine vpon our loynes.
Ka kawo mu cikin kurkuku ka kuma jibga kaya masu nauyi a bayanmu.
12 Thou hast caused men to ryde ouer our heads: we went into fire and into water, but thou broughtest vs out into a welthie place.
Ka bar mutane suka hau a kawunanmu; mun bi ta wuta da ruwa, amma ka kawo mu zuwa wurin yalwa.
13 I will go into thine House with burnt offrings, and will pay thee my vowes,
Zan zo haikalinka da hadayun ƙonawa zan kuwa cika alkawurana gare ka,
14 Which my lippes haue promised, and my mouth hath spoken in mine affliction.
alkawuran da leɓunana suka yi alkawari bakina kuma ya faɗa sa’ad da nake cikin wahala.
15 I will offer vnto thee the burnt offerings of fat rammes with incense: I will prepare bullocks and goates. (Selah)
Zan miƙa kitsen dabbobi gare ka da kuma baye-baye na raguna; zan miƙa bijimai da awaki. (Sela)
16 Come and hearken, all ye that feare God, and I will tell you what he hath done to my soule.
Ku zo ku saurara, dukanku waɗanda suke tsoron Allah; bari in faɗa muku abin da ya yi mini.
17 I called vnto him with my mouth, and he was exalted with my tongue.
Na yi kuka gare shi da bakina; yabonsa yana a harshena.
18 If I regard wickednesse in mine heart, the Lord will not heare me.
Da a ce na ji daɗin zunubi a zuciyata, da Ubangiji ba zai saurara ba;
19 But God hath heard me, and considered the voyce of my prayer.
amma tabbatacce Allah ya saurara ya kuma ji muryata a cikin addu’a.
20 Praysed be God, which hath not put backe my prayer, nor his mercie from me.
Yabo ga Allah, wanda bai ƙi addu’ata ba ko yă janye ƙaunarsa daga gare ni!

< Psalms 66 >