< Psalms 34 >

1 A Psalme of Dauid, when he changed his behauiour before Abimelech, who droue him away, and he departed. I will alway giue thankes vnto the Lord: his praise shalbe in my mouth continually.
Ta Dawuda. Sa’ad da ya yi kamar ya haukace a gaban Abimelek, Wanda ya kore shi, ya kuwa tafi. Zan gode wa Ubangiji kullayaumi; yabonsa kullum za su kasance a leɓunana.
2 My soule shall glory in the Lord: the humble shall heare it, and be glad.
Raina zai yi fariya a cikin Ubangiji; bari waɗanda suke wahala su ji su kuma yi farin ciki.
3 Praise ye the Lord with me, and let vs magnifie his Name together.
Ku ɗaukaka Ubangiji tare da ni; bari mu ɗaukaka sunansa tare.
4 I sought the Lord, and he heard me: yea, he deliuered me out of all my feare.
Na nemi Ubangiji, ya kuwa amsa mini; ya cece ni daga dukan tsoro.
5 They shall looke vnto him, and runne to him: and their faces shall not be ashamed, saying,
Waɗanda suke dubansa sukan haskaka; fuskokinsu ba sa rufuwa da kunya.
6 This poore man cryed, and the Lord heard him, and saued him out of all his troubles.
Wannan matalauci ya yi kira, Ubangiji kuwa ya ji shi; ya cece shi daga dukan wahalarsa.
7 The Angel of the Lord pitcheth round about them, that feare him, and deliuereth them.
Mala’ikan Ubangiji ya kafa sansani kewaye da waɗanda suke tsoronsa, ya kuwa cece su.
8 Taste ye and see, howe gratious the Lord is: blessed is the man that trusteth in him.
Ku gwada ku gani cewa Ubangiji yana da kyau; mai albarka ne mutumin da yake neman mafaka a gare shi.
9 Feare the Lord, ye his Saintes: for nothing wanteth to them that feare him.
Ku ji tsoron Ubangiji, ku tsarkakansa, gama masu tsoronsa ba sa rasa kome.
10 The lyons doe lacke and suffer hunger, but they, which seeke the Lord, shall want nothing that is good.
Zakoki za su iya rasa ƙarfi su kuma ji yunwa, amma waɗanda suke neman Ubangiji ba sa rasa abu mai kyau.
11 Come children, hearken vnto me: I will teache you the feare of the Lord.
Ku zo,’ya’yana, ku saurare ni; zan koya muku tsoron Ubangiji.
12 What man is he, that desireth life, and loueth long dayes for to see good?
Duk waninku da yake ƙaunar rayuwa yana kuma so yă ga kwanaki masu kyau,
13 Keepe thy tongue from euill, and thy lips, that they speake no guile.
ka kiyaye harshenka daga mugunta da kuma leɓunanku daga faɗar ƙarairayi.
14 Eschewe euill and doe good: seeke peace and follow after it.
Juyo daga mugunta ku yi alheri; nemi salama ku kuma yi ƙoƙarin samunta.
15 The eyes of the Lord are vpon the righteous, and his eares are open vnto their crie.
Idanun Ubangiji suna a kan masu adalci kuma kunnuwansa suna sauraran kukansu;
16 But the face of the Lord is against them that doe euill, to cut off their remembrance from the earth.
fuskar Ubangiji yana gāba da waɗanda suke aikata mugunta, don yă sa a manta da su a duniya.
17 The righteous crie, and the Lord heareth them, and deliuereth them out of all their troubles.
Adalai kan yi kuka, Ubangiji kuwa yakan ji su; yakan cece su daga dukan wahalarsu.
18 The Lord is neere vnto them that are of a contrite heart, and will saue such as be afflicted in Spirite.
Ubangiji yana kusa da waɗanda suka karai ya kuma cece waɗanda aka ragargaza a ruhu.
19 Great are the troubles of the righteous: but the Lord deliuereth him out of them all.
Adali zai iya kasance da wahala da yawa, amma Ubangiji yakan cece shi daga dukansu;
20 He keepeth all his bones: not one of them is broken.
yakan tsare dukan ƙasusuwansa, ba ko ɗayansu da zai karye.
21 But malice shall slay the wicked: and they that hate the righteous, shall perish.
Mugunta zai kashe mugu; za a hukunta abokan gāban adalai.
22 The Lord redeemeth the soules of his seruants: and none, that trust in him, shall perish.
Ubangiji yakan cece bayinsa; ba wanda yake neman mafaka a wurinsa da za a hukunta.

< Psalms 34 >