< Psalms 2 >

1 Why doe the heathen rage, and the people murmure in vaine?
Me ya sa ƙasashe suke haɗa baki mutane kuma suke ƙulla shawarwarin banza?
2 The Kings of the earth band themselues, and the princes are assembled together against the Lord, and against his Christ.
Sarakunan duniya sun ɗauki matsayi masu mulki sun taru gaba ɗaya suna gāba da Ubangiji da kuma Shafaffensa.
3 Let vs breake their bands, and cast their cordes from vs.
Suna cewa, “Bari mu tsittsinke sarƙoƙinsu, mu kuma’yantar da kamammu daga kangin bautar Allah.”
4 But he that dwelleth in the heauen, shall laugh: the Lord shall haue them in derision.
Mai zama a kursiyi a sama yana dariya; Ubangiji yana musu ba’a.
5 Then shall hee speake vnto them in his wrath, and vexe them in his sore displeasure, saying,
Sa’an nan ya tsawata musu cikin fushinsa ya kuma razanar da su cikin hasalarsa, yana cewa,
6 Euen I haue set my King vpon Zion mine holy mountaine.
“Na kafa Sarkina a kan kursiyi a kan Sihiyona, dutsena mai tsarki.”
7 I will declare the decree: that is, the Lord hath said vnto me, Thou art my Sonne: this day haue I begotten thee.
Sarki ya yi shelar umarnin Ubangiji. Ubangiji ya ce mini, “Kai Ɗana ne; yau na zama Mahaifinka.
8 Aske of me, and I shall giue thee the heathen for thine inheritance, and the endes of the earth for thy possession.
Ka tambaye ni zan kuwa sa al’ummai su zama gādonka, iyakokin duniya su zama mallakarka.
9 Thou shalt krush them with a scepter of yron, and breake them in pieces like a potters vessell.
Za ka yi mulkinsu da sandan ƙarfe; za ka farfashe su kucu-kucu kamar tukunyar laka.”
10 Be wise nowe therefore, ye Kings: be learned ye Iudges of the earth.
Saboda haka, ku sarakuna, ku yi wayo; ku shiga hankalinku, ku masu mulkin duniya.
11 Serue the Lord in feare, and reioyce in trembling.
Ku bauta wa Ubangiji da tsoro ku kuma yi farin ciki kuna rawar jiki.
12 Kisse the sonne, least he be angry, and ye perish in the way, when his wrath shall suddenly burne. blessed are all that trust in him.
Ku sumbaci Ɗan, don kada yă yi fushi ku hallaka a abubuwan da kuke yi, gama fushinsa zai iya kuna farat ɗaya. Masu farin ciki ne dukan waɗanda suke neman mafaka daga gare shi.

< Psalms 2 >