< Psalms 140 >

1 To him that excelleth. A Psalme of David. Deliuer me, O Lord, from the euill man: preserue me from the cruel man:
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Ka cece ni, ya Ubangiji, daga mugaye; ka tsare ni daga mutane masu rikici,
2 Which imagine euill things in their heart, and make warre continually.
masu shirya maƙarƙashiya a zukatansu suna kuma kawo yaƙi kullum.
3 They haue sharpened their tongues like a serpent: adders poyson is vnder their lips. (Selah)
Suna sa harsunansu su yi kaifi kamar na maciji; dafin gamsheƙa yana a leɓunansu. (Sela)
4 Keepe mee, O Lord, from the handes of the wicked: preserue mee from the cruell man, which purposeth to cause my steppes to slide.
Ka kiyaye ni, ya Ubangiji, daga hannuwan mugaye; ka tsare ni daga mutane masu rikici waɗanda suke shirin kwashe ni a ƙafafu.
5 The proude haue layde a snare for me, and spred a nette with cordes in my pathway, and set grennes for me. (Selah)
Masu girman kai sun sa mini tarko; sun shimfiɗa igiyoyin ragarsu sun kuma shirya mini tarko a hanyata. (Sela)
6 Therefore I saide vnto the Lord, Thou art my God: heare, O Lord, the voyce of my prayers.
Ya Ubangiji, na ce maka, “Kai ne Allahna.” Ka ji kukata ta neman jinƙai, ya Ubangiji.
7 O Lord God the strength of my saluation, thou hast couered mine head in the day of battel.
Ya Ubangiji Mai Iko Duka, mai fansana mai ƙarfi, wanda yake garkuwoyin kaina a ranar yaƙi.
8 Let not the wicked haue his desire, O Lord: performe not his wicked thought, least they be proude. (Selah)
Kada ka biya wa mugaye bukatunsu, ya Ubangiji; kada ka bar shirinsu su yi nasara, in ba haka ba za su yi fariya. (Sela)
9 As for the chiefe of them, that compasse me about, let the mischiefe of their owne lippes come vpon them.
Bari kawunan waɗanda suka kewaye ni su rufu da masifun da leɓunansu suka jawo.
10 Let coles fal vpon them: let him cast them into the fire, and into the deepe pits, that they rise not.
Bari garwashin wuta yă zubo a kansu; bari a jefar da su cikin wuta, cikin rami mai zurfi, kada su sāke tashi.
11 For the backbiter shall not be established vpon the earth: euill shall hunt the cruell man to destruction.
Kada masu ɓata suna su taɓa kahu a ƙasar; bari masifa ta farauci mutane masu rikici.
12 I know that the Lord will auenge the afflicted, and iudge the poore.
Na san cewa Ubangiji ya shirya wa matalauta adalci yana kuma yi wa mabukata adalci.
13 Surely the righteous shall prayse thy Name, and the iust shall dwell in thy presence.
Tabbatacce masu adalci za su yabi sunanka masu aikata gaskiya kuma za su zauna a gabanka.

< Psalms 140 >