< Proverbs 24 >

1 Be not thou enuious against euill men, neither desire to be with them.
Kada ka yi ƙyashin mugaye, kada ka yi sha’awar ƙungiyarsu;
2 For their heart imagineth destruction, and their lippes speake mischiefe.
gama leɓunansu suna maganar tā-da-na-zaune-tsaye ne.
3 Through wisdome is an house builded, and with vnderstanding it is established.
Ta wurin hikima ce ake gina gida, kuma ta wurin fahimi ake kafa ta;
4 And by knowledge shall the chambers bee filled with all precious, and pleasant riches.
ta wurin sani ɗakunanta sukan cika da kyawawan kayayyaki masu daraja.
5 A wise man is strong: for a man of vnderstanding encreaseth his strength.
Mutum mai hikima yana da iko sosai, kuma mutum mai sani yakan ƙaru da ƙarfi;
6 For with counsel thou shalt enterprise thy warre, and in the multitude of them that can giue counsell, is health.
don yin yaƙi kana bukatar bishewa, kuma don ka yi nasara kana bukatar mashawarta masu yawa.
7 Wisdome is hie to a foole: therefore he can not open his mouth in the gate.
Hikima ta yi wa wawa nisa ƙwarai a cikin taro a ƙofar gari ba shi da ta cewa.
8 Hee that imagineth to doe euill, men shall call him an autour of wickednes.
Duk mai ƙulla mugunta za a ɗauka shi mai kuta hargitsi ne.
9 The wicked thought of a foole is sinne, and the scorner is an abomination vnto men.
Makircin wawa zunubi ne, mutane kuma sukan yi ƙyamar mai ba’a.
10 If thou bee faint in the day of aduersitie, thy strength is small.
In ba ka da ƙarfi a lokacin wahala, ka tabbatar kai marar ƙarfi ne sosai!
11 Deliuer them that are drawen to death: wilt thou not preserue them that are led to be slaine?
Ka kuɓutar da waɗanda ake ja zuwa inda za a kashe su; ka riƙe waɗanda suke tangaɗi zuwa wajen yanka.
12 If thou say, Beholde, we knew not of it: he that pondereth the heartes, doeth not hee vnderstand it? and hee that keepeth thy soule, knoweth he it not? will not he also recompense euery man according to his workes?
In kuka ce, “Ai, ba mu san wani abu a kai wannan ba,” shi da yake awon ba shi da zuciyar ganewa ne? Shi da yake tsare ranka bai sani ba ne? Ba zai sāka wa kowane mutum bisa ga abin da ya aikata ba?
13 My sonne, eate hony, for it is good, and the hony combe, for it is sweete vnto thy mouth.
Ka sha zuma, ɗana, ka sha zuma gama tana da kyau; zuma daga kaki yana da zaƙi a harshenka.
14 So shall the knowledge of wisdome be vnto thy soule, if thou finde it, and there shall be an ende, and thine hope shall not be cut off.
Ka kuma san cewa hikima tana da zaƙi ga rai; in ka same ta, akwai sa zuciya ta nan gaba dominka, kuma sa zuciyarka ba za tă zama a banza ba.
15 Laye no waite, O wicked man, against the house of the righteous, and spoyle not his resting place.
Kada ka kwanta kana fako kamar ɗan iska don ƙwace gidan adali, kada ka ƙwace masa wurin zama;
16 For a iust man falleth seuen times, and riseth againe: but the wicked fall into mischiefe.
gama ko da adali ya fāɗi sau bakwai, yakan tashi kuma, amma bala’i kan kwantar da mugaye.
17 Bee thou not glad when thine enemie falleth, and let not thine heart reioyce when hee stumbleth,
Kada ka yi dariya sa’ad da abokin gāba ya fāɗi; sa’ad da ya yi tuntuɓe, kada ka yi farin ciki,
18 Least the Lord see it, and it displease him, and he turne his wrath from him.
in ba haka ba in Ubangiji ya gani ba zai amince ba ya kuma juye fushinsa daga gare shi.
19 Fret not thy selfe because of the malicious, neither be enuious at the wicked.
Kada ka ji tsoro saboda masu mugunta ko ka yi ƙyashin mugaye,
20 For there shall bee none ende of plagues to the euill man: the light of the wicked shall bee put out.
gama mugu ba shi da zuciya ta nan gaba, kuma fitilar mugaye za tă mutu.
21 My sonne feare the Lord, and the King, and meddle not with them that are sedicious.
Ka ji tsoron Ubangiji da kuma sarki, ɗana, kuma kada ka haɗa kai da masu tayarwa,
22 For their destruction shall rise suddenly, and who knoweth the ruine of them both?
gama za a tura waɗannan biyu zuwa hallaka nan da nan, kuma wa ya sani irin bala’in da za su iya kawowa?
23 ALSO THESE THINGS PERTEINE TO THE WISE, It is not good to haue respect of any person in iudgement.
Waɗannan ma maganganun masu hikima ne, Nunan sonkai a shari’a ba shi da kyau.
24 He that saith to the wicked, Thou art righteous, him shall the people curse, and the multitude shall abhorre him.
Duk wanda ya ce wa mai laifi, “Ba ka da laifi”, mutane za su la’ance shi al’umma kuma za tă ce ba a san shi ba.
25 But to them that rebuke him, shall be pleasure, and vpon them shall come the blessing of goodnesse.
Amma zai zama da lafiya ga duk waɗanda suka hukunta masu laifi, kuma babban albarka zai zo a kansu.
26 They shall kisse the lippes of him that answereth vpright wordes.
Amsa da take ta gaskiya tana kamar sumba a leɓuna.
27 Prepare thy worke without, and make readie thy thinges in the fielde, and after, builde thine house.
Ka gama aikinka ka kuma shirya gonakinka; bayan haka, ka gina gidanka.
28 Be not a witnes against thy neighbour without cause: for wilt thou deceiue with thy lippes?
Kada ka ba da shaida a kan maƙwabcinka ba tare da isashen dalili ba, ko ka yi amfani da leɓunanka ka yi ruɗu.
29 Say not, I wil doe to him, as he hath done to mee, I will recompence euery man according to his worke.
Kada ka ce, “Zan yi masa kamar yadda ya yi mini; zan rama abin da wannan mutum ya yi mini.”
30 I passed by the fielde of the slouthfull, and by the vineyarde of the man destitute of vnderstanding.
Na wuce cikin gonar rago, na wuce cikin gonar inabin mutumin da ba shi da azanci;
31 And lo, it was al growen ouer with thornes, and nettles had couered the face thereof, and the stone wall thereof was broken downe.
ƙayayyuwa sun yi girma ko’ina, ciyayi sun rufe ƙasar, katangar duwatsu duk ta rushe.
32 Then I behelde, and I considered it well: I looked vpon it, and receiued instruction.
Na yi tunani a zuciyata na kuwa koyi darasi daga abin da na gani.
33 Yet a litle sleepe, a litle slumber, a litle folding of the handes to sleepe.
Ɗan barci, ɗan gyangyaɗi, ɗan naɗin hannuwa don a huta,
34 So thy pouertie commeth as one that traueileth by the way, and thy necessitie like an armed man.
sai talauci ya shigo maka kamar’yan fashi rashi kuma ya zo maka kamar mai hari.

< Proverbs 24 >