< Proverbs 2 >

1 My sonne, if thou wilt receiue my wordes, and hide my commandements within thee,
Ɗana, in ka yarda da kalmomina ka kuma ajiye umarnaina a cikinka,
2 And cause thine eares to hearken vnto wisdome, and encline thine heart to vnderstanding,
kana kasa kunne ga abin da yake na hikima, kana kuma yin ƙoƙari ka fahimce shi,
3 (For if thou callest after knowledge, and cryest for vnderstanding:
in kuma ka kira ga tsinkaya ka kuma kira da ƙarfi don ganewa,
4 If thou seekest her as siluer, and searchest for her as for treasures,
in ka neme shi yadda ake neman azurfa ka kuma neme shi kamar yadda ake neman ɓoyayyiyar dukiya,
5 Then shalt thou vnderstand the feare of the Lord, and finde the knowledge of God.
to, za ka gane tsoron Ubangiji ka kuma sami sanin Allah.
6 For the Lord giueth wisdome, out of his mouth commeth knowledge and vnderstanding.
Gama Ubangiji yana ba da hikima, daga bakinsa kuma, sani da ganewa sukan fito.
7 He preserueth the state of the righteous: he is a shielde to them that walke vprightly,
Yana riƙe da nasara a ma’aji don masu yin gaskiya, shi ne mafaka ga waɗanda tafiyarsu ba ta da laifi,
8 That they may keepe the wayes of iudgement: and he preserueth the way of his Saintes)
gama yana tsare abin da masu adalci suke bukata yana kuma tsare hanyar amintattunsa.
9 Then shalt thou vnderstand righteousnes, and iudgement, and equitie, and euery good path.
Sa’an nan za ku fahimci abin da yake daidai da abin da yake na adalci da abin da yake gaskiya, da kowace hanya mai kyau.
10 When wisdome entreth into thine heart, and knowledge deliteth thy soule,
Gama hikima za tă shiga cikin zuciyarka, sani kuma zai faranta maka rai.
11 Then shall counsell preserue thee, and vnderstanding shall keepe thee,
Tsinkaya za tă tsare ka, ganewa kuma za tă yi maka jagora.
12 And deliuer thee from the euill way, and from the man that speaketh froward things,
Hikima za tă cece ka daga hanyoyin mugayen mutane, daga kalmomin mutane masu ɓatanci,
13 And from them that leaue the wayes of righteousnes to walke in the wayes of darkenes:
waɗanda suke barin miƙaƙƙun hanyoyi don su yi tafiya a hanyoyi masu duhu,
14 Which reioyce in doing euill, and delite in the frowardnesse of the wicked,
waɗanda suke jin daɗin yin abin da ba shi da kyau suna kuma farin ciki a mugayen ɓatanci,
15 Whose wayes are crooked and they are lewde in their paths.
waɗanda hanyoyinsu karkatattu ne waɗanda kuma suke cuku-cuku a hanyoyinsu.
16 And it shall deliuer thee from the strange woman, euen from the stranger, which flattereth with her wordes.
Zai kiyaye ku kuma daga mazinaciya, daga mace mai lalata, mai ƙoƙarin kama ka da daɗin bakinta,
17 Which forsaketh the guide of her youth, and forgetteth the couenant of her God.
wadda ta bar mijin ƙuruciyarta ta kuma ƙyale alkawarin da ta yi a gaban Allah.
18 Surely her house tendeth to death, and her paths vnto the dead.
Gama gidanta yana kai ga mutuwa hanyarta kuma ga ruhohin matattu.
19 All they that goe vnto her, returne not againe, neither take they holde of the wayes of life.
Duk wanda ya ziyarce ta ba ya ƙara komowa ba zai ƙara komowa ga hanyar rai.
20 Therefore walke thou in the way of good men, and keepe the wayes of the righteous.
Don haka dole ku yi tafiya a hanyoyin mutanen kirki ku kuma yi ta bi hanyoyin adalai.
21 For the iust shall dwell in the land, and the vpright men shall remaine in it.
Gama masu aikata gaskiya za su zauna a cikin ƙasar, marasa laifi kuma za su kasance a cikinta;
22 But the wicked shalbe cut off from ye earth, and the transgressours shalbe rooted out of it.
amma za a fid da mugaye daga ƙasar, za a tumɓuke marasa aminci kuma daga gare ta.

< Proverbs 2 >