< Numbers 8 >

1 And the Lord spake vnto Moses, saying,
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 Speake vnto Aaron, and say vnto him, When thou lightest the lampes, the seuen lampes shall giue light towarde the forefront of the Candlesticke.
“Yi magana da Haruna, ka ce masa, ‘Sa’ad da za ka shisshirya fitilun nan bakwai, ka shirya su yadda za su fuskanci gaba domin haskensu yă haskaka ta gaba.’”
3 And Aaron did so, lighting the lampes thereof towarde ye forefront of the Candlesticke, as the Lord had commanded Moses.
Haka kuwa Haruna ya yi; ya shisshirya fitilun yadda za su fuskanci gaba a kan wurin ajiye fitilan, kamar dai yadda Ubangiji ya umarci Musa.
4 And this was the worke of the Candlesticke, euen of golde beaten out with the hammer, both the shafte, and the flowres thereof was beaten out with the hammer: according to the paterne, which the Lord had shewed Moses, so made he the Candlesticke.
Ga yadda aka yi wurin ajiye fitilan. An ƙera shi da zinariya daga gindinsa har zuwa sama inda ya buɗu. Aka ƙera wurin ajiye fitilan yadda Ubangiji ya nuna wa Musa.
5 And the Lord spake vnto Moses, saying,
Ubangiji ya ce wa Musa,
6 Take the Leuites from among the children of Israel, and purifie them.
“Keɓe Lawiyawa daga sauran Isra’ilawa, ka tsarkake su.
7 And thus shalt thou doe vnto them, when thou purifiest them, Sprinckle water of purification vpon them, and let them shaue all their flesh, and wash their clothes: so they shalbe cleane.
Ga yadda za ka tsarkake su, ka yayyafa musu ruwan tsarkakewa; ka sa su aske jikunansu duka su kuma wanke tufafinsu, ta haka za su tsarkake kansu.
8 Then they shall take a yong bullocke with his meate offring of fine floure, mingled with oyle, and another yong bullocke shalt thou take for a sinne offring.
Ka sa su ɗauki ɗan bijimi tare da lallausan garin hadaya, kwaɓaɓɓe da mai; sa’an nan, kai kuma ka ɗauki ɗan bijimi na biyu na hadaya don zunubi.
9 Then thou shalt bring the Leuites before the Tabernacle of the Congregation, and asseble all the Congregation of the children of Israel.
Ka kawo Lawiyawa a gaban Tentin Sujada, ka kuma kira taron Isra’ilawa duka.
10 Thou shalt bring the Leuites also before the Lord, and the children of Israel shall put their handes vpon the Leuites.
Za ka kawo Lawiyawa a gaban Ubangiji, Isra’ilawa kuma za su ɗibiya musu hannuwansu.
11 And Aaron shall offer the Leuites before the Lord, as a shake offring of ye childre of Israel, that they may execute the seruice of the Lord.
Haruna zai miƙa Lawiyawa a gaban Ubangiji a matsayin hadaya ta kaɗawa daga Isra’ilawa, saboda a shirya su domin aikin Ubangiji.
12 And the Leuites shall put their handes vpon the heades of the bullockes, and make thou the one a sinne offring, and the other a burnt offring vnto the Lord, that thou mayest make an atonement for the Leuites.
“Bayan Lawiyawa sun ɗibiya hannuwansu a kan bijiman, sai ka yi amfani da ɗaya a matsayin hadaya don zunubi ga Ubangiji, ɗayan kuma domin hadaya ta ƙonawa, don yin kafara saboda Lawiyawa.
13 And thou shalt set the Leuites before Aaron and before his sonnes, and offer the as a shake offring to the Lord.
Ka kuma sa Lawiyawa su tsaya a gaban Haruna da’ya’yansa, sai ka miƙa su kamar hadaya ta kaɗawa ga Ubangiji.
14 Thus thou shalt separate the Leuites from among the children of Israel, and the Leuites shall be mine.
Da haka za ka keɓe Lawiyawa daga sauran Isra’ilawa, Lawiyawa za su zama nawa.
15 And afterwarde shall the Leuites goe in, to serue in the Tabernacle of the Congregation, and thou shalt purifie them and offer them, as a shake offering.
“Bayan ka tsarkake Lawiyawa, ka kuma miƙa su kamar hadaya ta kaɗawa, sai su zo su yi aikinsu a Tentin Sujada.
16 For they are freely giuen vnto me from among the children of Israel, for such as open any wombe: for all the first borne of the children of Israel haue I taken them vnto me.
Gama dukansu an ba ni su daga cikin Isra’ilawa a maimakon dukan waɗanda suka fara buɗe mahaifa, wato, dukan’ya’yan farin Isra’ilawa. Na karɓi Lawiyawa su zama nawa.
17 For all the first borne of the children of Israel are mine, both of man and of beast: since the day that I smote euery first borne in the land of Egypt, I sanctified them for my selfe.
Kowane ɗan farin haihuwa, ko mutum, ko dabba a Isra’ila, nawa ne. Sa’ad da na kashe’ya’yan fari a Masar, na keɓe’ya’yan fari na Isra’ilawa wa kaina.
18 And I haue taken the Leuites for all the first borne of the children of Israel,
Na kuma ɗauki Lawiyawa a maimakon dukan’ya’yan fari maza a Isra’ila.
19 And haue giuen the Leuites as a gift vnto Aaron, and to his sonnes from among the children of Israel, to do the seruice of the children of Israel in the Tabernacle of the Congregation, and to make an atonement for the children of Israel, that there be no plague among the children of Israel, when the children of Israel come neere vnto the Sanctuarie.
Cikin dukan Isra’ilawa, na ba da Lawiyawa kyauta ga Haruna da’ya’yansa, su yi hidima a Tentin Sujada a madadin Isra’ilawa, su kuma yi kafara dominsu saboda kada annoba ta bugi Isra’ilawa sa’ad da suka je kusa da wuri mai tsarki.”
20 Then Moses and Aaron and all the Cogregation of the children of Israel did with the Leuites, according vnto all that the Lord had commanded Moses concerning the Leuites: so did the children of Israel vnto them.
Musa, Haruna da kuma dukan taron Isra’ilawa, suka yi da Lawiyawa yadda Ubangiji ya umarci Musa.
21 So the Leuites were purified, and washed their clothes, and Aaron offred them as a shake offring before the Lord, and Aaron made an atonement for them, to purifie them.
Lawiyawa suka tsarkake kansu, suka kuma wanke tufafinsu. Sai Haruna ya miƙa su kamar hadaya ta kaɗawa a gaban Ubangiji, ya kuma yi kafara saboda su don yă tsarkake su.
22 And after that, went the Leuites in to doe their seruice in the Tabernacle of the Congregation, before Aaron and before his sonnes: as the Lord had commanded Moses concerning the Leuites, so they did vnto them.
Bayan haka, sai Lawiyawa suka zo don su yi aikinsu a Tentin Sujada, a ƙarƙashin Haruna da’ya’yansa. Suka yi da Lawiyawa kamar dai yadda Ubangiji ya umarci Musa.
23 And the Lord spake vnto Moses, saying,
Ubangiji ya ce wa Musa,
24 This also belongeth to the Leuites: from fiue and twentie yeere olde and vpwarde, they shall goe in, to execute their office in the seruice of the Tabernacle of the Congregation.
“Wannan ya shafi Lawiyawa ne, wato, mazan da suka kai shekara ashirin da biyar, ko fiye, za su zo su yi aiki a Tentin Sujada,
25 And after the age of fiftie yeere, they shall cease from executing the office, and shall serue no more:
amma in suka kai shekaru hamsin da haihuwa, dole su huta daga wannan aiki na yau da kullum, su kuma daina aiki.
26 But they shall minister with their brethre in the Tabernacle of the Congregation, to keepe things committed to their charge, but they shall doe no seruice: thus shalt thou doe vnto the Leuites touching their charges.
Za su iya taimakon’yan’uwansu cikin tafiyar da ayyuka a Tentin Sujada, amma su kansu ba za su yi aikin ba. Haka fa za ka ba wa Lawiyawa aikinsu.”

< Numbers 8 >