< Numbers 27 >

1 Then came the daughters of Zelophehad, the sonne of Hepher, the sonne of Gilead, the sonne of Machir, the sonne of Manasseh, of the familie of Manasseh, the sonne of Ioseph (and the names of his daughters were these, Mahlah, Noah and Hoglah, and Milcah, and Tirzah)
’Ya’yan nan mata na Zelofehad, ɗan Hefer, ɗan Gileyad, ɗan Makir, ɗan Manasse, suna cikin kabilan Manasse ɗan Yusuf, suka tafi ƙofar shiga Tentin Sujada. Sunayensu kuwa su ne Mala, Nowa, Hogla, Milka da kuma Tirza.
2 And stoode before Moses, and before Eleazar the Priest, and before the Princes, and all the assemblie, at the doore of the Tabernacle of the Congregation, saying,
Da suka tafi ƙofar shiga Tentin Sujada, sai suka tsaya a gaban Musa, Eleyazar firist, shugabannin da sauran taro, suka ce,
3 Our father dyed in the wildernes, and he was not among the assemblie of them that were assembled against the Lord in the companie of Korah, but died in his sinne, and had no sonnes.
“Mahaifinmu ya mutu a hamada. Ba ya cikin mabiyan Kora waɗanda suka taru suka tayar wa Ubangiji, amma ya mutu ne saboda zunubinsa, bai kuma bar’ya’ya maza ba.
4 Wherefore should the name of our father be taken away from among his familie, because he hath no sonne? giue vs a possession among the brethren of our father.
Me ya sa sunan mahaifinmu zai ɓace a kabilarsa don kawai ba shi da ɗa? Ka ba mu gādo cikin’yan’uwan mahaifinmu.”
5 Then Moses brought their cause before the Lord.
Saboda haka Musa ya kawo maganarsu a gaban Ubangiji.
6 And the Lord spake vnto Moses, saying,
Ubangiji kuwa ya ce wa masa,
7 The daughters of Zelophehad speake right: thou shalt giue them a possession to inherite among their fathers brethren, and shalt turne the inheritance of their father vnto them.
“Abin da’ya’yan nan mata na Zelofehad suke faɗi gaskiya ne. Dole ka ba su mallaka a matsayin gādo cikin’yan’uwan mahaifinsu, ka kuma mayar musu da gādon mahaifinsu.
8 Also thou shalt speake vnto the children of Israel, saying, If a man die and haue no sonne, then ye shall turne his inheritaunce vnto his daughter.
“Ka faɗa wa Isra’ilawa cewa, ‘In wani ya mutu ba shi da ɗa, a ba da gādonsa ga’yarsa.
9 And if he haue no daughter, ye shall giue his inheritance vnto his brethren.
In ba shi da diya, sai a ba wa’yan’uwansa gādonsa.
10 And if he haue no brethren, ye shall giue his inheritance vnto his fathers brethren.
In ba shi da’yan’uwa, a ba da gādonsa ga’yan’uwan mahaifinsa.
11 And if his father haue no brethren, ye shall giue his inheritance vnto his next kinsman of his familie, and he shall possesse it: and this shall be vnto the children of Israel a law of iudgement, as the Lord hath commanded Moses.
In mahaifinsa ba shi da’yan’uwa, a ba da gādonsa ga danginsa na kusa, a kabilarsa don yă mallaka. Wannan ya zama ƙa’ida wa Isra’ilawa, yadda Ubangiji ya umarci Musa.’”
12 Againe the Lord said vnto Moses, Go vp into this mount of Abarim, and behold ye lande which I haue giuen vnto the children of Israel.
Sa’an nan Ubangiji ya ce wa Musa, “Hau bisa wannan dutse a Abarim. Ka ga ƙasar da na ba wa Isra’ilawa.
13 And when thou hast seene it, thou shalt be gathered vnto thy people also, as Aaron thy brother was gathered.
Bayan ka gani, kai ma za ka bi ƙafafun mutanenka, kamar yadda ɗan’uwanka Haruna ya yi,
14 For ye were disobedient vnto my worde in the desert of Zin, in the strife of the assemblie, to sanctifie me in the waters before their eyes. That is the water of Meribah in Kadesh in the wildernesse of Zin.
gama sa’ad da jama’a suka yi tayarwa saboda rashin ruwa a Hamadan Zin, ku biyu, ba ku kiyaye umarnina don ku ɗaukaka ni matsayin mai tsarki, a gabansu ba.” (Waɗannan su ne ruwaye na Meriba da Kadesh, a Hamadan Zin.)
15 Then Moses spake vnto the Lord, saying,
Musa ya ce wa Ubangiji,
16 Let the Lord God of the spirits of all flesh appoint a man ouer the Congregation,
“Bari Ubangiji, Allah na ruhohin’yan adam, yă naɗa wani a kan wannan jama’a
17 Who may goe out and in before them, and leade them out and in, that the Congregation of the Lord be not as sheepe, which haue not a shepheard.
yă shiga, yă kuma fita a gabansu, wanda zai bishe su zuwa waje, yă kuma dawo da su ciki, don kada mutanen Ubangiji su zama kamar tumakin da ba su da makiyayi.”
18 And the Lord said vnto Moses, Take thee Ioshua the sonne of Nun, in whom is the Spirite, and put thine handes vpon him,
Sai Ubangiji ya ce wa Musa, “Ka ɗauki Yoshuwa ɗan Nun, mutumin da ruhun shugabanci yake a cikinsa, ka ɗibiya masa hannunka.
19 And set him before Eleazar the Priest, and before all the Congregation, and giue him a charge in their sight.
Ka sa yă tsaya a gaban Eleyazar firist, da gaban dukan jama’a, sa’an nan ka keɓe shi a gabansu.
20 And giue him of thy glory, that all the Congregation of ye children of Israel may obey.
Ka danƙa masa ikonka don dukan jama’a Isra’ilawa su yi masa biyayya.
21 And he shall stande before Eleazar the Priest, who shall aske counsell for him by the iudgement of Vrim before the Lord: at his worde they shall goe out, and at his worde they shall come in, both he, and all the children of Israel with him and all the Congregation.
Zai tsaya a gaban Eleyazar firist, wanda zai nemi masa shawara ta wurin Urim a gaban Ubangiji. Da umarninsa, da shi da dukan jama’ar Isra’ilawa za su fita, da umarninsa kuma za su shiga.”
22 So Moses did as the Lord had commanded him, and he tooke Ioshua, and set him before Eleazar the Priest, and before all the Congregation.
Musa ya yi yadda Ubangiji ya umarce shi. Ya ɗauki Yoshuwa, ya sa ya tsaya a gaban Eleyazar firist, da kuma gaban dukan jama’a.
23 Then he put his handes vpon him, and gaue him a charge, as the Lord had spoken by the hand of Moses.
Sai ya ɗibiya masa hannuwansa, ya keɓe shi, yadda Ubangiji ya umarta ta wurin Musa.

< Numbers 27 >