< Numbers 20 >

1 Then the children of Israel came with ye whole Congregation to the desert of Zin in the first moneth, and the people abode at Cadesh: where Miriam died, and was buried there.
A watan fari, dukan jama’ar Isra’ilawa suka iso Hamadan Zin. Suka sauka a Kadesh. A nan ne Miriyam ta mutu, aka kuma bizne ta.
2 But there was no water for the Congregation, and they assembled them selues against Moses and against Aaron.
Sai aka rasa ruwa da jama’a za su sha, mutane suka taru, suka tayar wa Musa da Haruna.
3 And the people chode with Moses, and spake, saying, Would God we had perished, when our brethren died before the Lord.
Suka yi gunaguni wa Musa suka ce, “Da ma mun mutu sa’ad da’yan’uwanmu suka mutu a gaban Ubangiji!
4 Why haue ye thus brought the Congregation of the Lord vnto his wildernesse, that both we, and our cattell should die there?
Don me ka kawo jama’ar Ubangiji a wannan hamada, don mu da dabbobinmu mu mutu a nan ke nan?
5 Wherefore nowe haue yee made vs to come vp from Egypt, to bring vs into this miserable place, which is no place of seede, nor figges, nor vines, nor pomegranates? neither is there any water to drinke.
Don me ka fitar da mu daga Masar zuwa wannan banzan wuri, inda babu hatsi ko ɓaure, inabi ko rumman. Kuma babu ruwan da za a sha?”
6 Then Moses and Aaron went from the assemblie vnto the doore of the Tabernacle of the Congregation, and fell vpon their faces: and the glory of the Lord appeared vnto them.
Sai Musa da Haruna suka tashi daga taron, suka tafi ƙofar Tentin Sujada, suka fāɗi rubda ciki, sai ɗaukakar Ubangiji ta bayyana musu.
7 And the Lord spake vnto Moses, saying,
Ubangiji ya ce wa Musa,
8 Take the rod, and gather thou and thy brother Aaron the Congregation together, and speake yee vnto the rocke before their eyes, and it shall giue foorth his water, and thou shalt bring them water out of the rocke: so thou shalt giue the Congregation, and their beastes drinke.
“Ka ɗauki sandanka, kai da Haruna, ɗan’uwanka, ku tara jama’a, ku yi magana da dutsen a gabansu ya ba da ruwan da yake cikinsa. Za ka sa ruwa ya ɓuɓɓugo musu daga dutsen. Ta haka za ka ba taron jama’a da garkunansu ruwan sha.”
9 Then Moses tooke the rod from before the Lord, as he had commanded him.
Sai Musa ya je ya ɗauki sandan kamar yadda Ubangiji ya umarce shi.
10 And Moses and Aaron gathered the Congregation together before the rocke, and Moses sayd vnto them, Heare nowe, ye rebels: shall we bring you water out of this rocke?
Shi da Haruna, suka tara jama’a a gaban dutsen, Musa ya ce musu, “Ku saurara, ku’yan tawaye, dole mu kawo muku ruwa daga wannan dutse?”
11 Then Moses lift vp his hande, and with his rod he smote the rocke twise, and the water came out aboundantly: so the Congregation, and their beastes dranke.
Sai Musa ya ɗaga hannu, ya bugi dutsen sau biyu da sandansa. Ruwa kuwa ya yi ta kwararowa, jama’a da dabbobinsu suka sha.
12 Againe the Lord spake vnto Moses, and to Aaron, Because ye beleeued me not, to sanctifie mee in the presence of the children of Israel, therefore ye shall not bring this Congregation into the land which I haue giuen them.
Amma Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna. “Tun da yake ba ku gaskata ni ba, ba ku kuwa ɗaukaka ni a idon Isra’ilawa ba, to, ba za ku kai taron jama’an nan a ƙasar da na ba su ba.”
13 This is the water of Meribah, because the children of Israel stroue with the Lord, and hee was sanctified in them.
Waɗannan su ne ruwan Meriba, inda Isra’ilawa suka yi wa Ubangiji gunaguni, inda kuma ya nuna kansa mai tsarki a cikinsu.
14 Then Moses sent messengers from Kadesh vnto the king of Edom, saying, Thus sayth thy brother Israel, Thou knowest all the trauaile that we haue had,
Musa ya aiki manzanni daga Kadesh zuwa wurin sarkin Edom cewa, “Ga abin da ɗan’uwanka Isra’ila ya ce ka san duk irin wahalolin da ya same mu.
15 How our fathers went downe into Egypt, and we dwelt in Egypt a long time, where the Egyptians handled vs euill and our fathers.
Kakanninmu sun gangaro zuwa Masar, muka zauna can shekaru da yawa. Masarawa suka wulaƙanta mu, da kuma kakanninmu,
16 But when we cried vnto the Lord, he heard our voyce, and sent an Angel, and hath brought vs out of Egypt, and beholde, wee are in the citie Kadesh, in thine vtmost border.
amma da muka yi kuka a gaban Ubangiji, ya kuwa ji mu, sai ya aiko mala’ika, ya fitar da mu daga Masar. “Yanzu ga mu a Kadesh, garin da yake kan iyakar yankinka.
17 I pray thee that we may passe through thy countrey: we will not goe through the fieldes nor the vineyardes, neither will we drinke of the water of the welles: we will goe by the kings way, and neither turne vnto the right hand nor to the left, vntill we be past thy borders.
Muna roƙonka, ka yarda mana mu bi ta ƙasarka. Ba za mu bi ta wani fili, ko gonar inabi ba, ko mu sha ruwa daga wata rijiya ba. Za mu bi ta babban hanyar sarki, ba kuwa za mu kauce dama, ko hagu ba, har mu wuce yankinka.”
18 And Edom answered him, Thou shalt not passe by mee, least I come out against thee with the sword.
Amma Edom ya amsa ya ce, “Ba za ku bi ta nan ba; in kuka kuskura, za mu fito, mu yaƙe ku da takobi.”
19 Then the children of Israel said vnto him, We will goe vp by the hie way: and if I and my cattell drinke of thy water, I will then pay for it: I will onely (without any harme) goe through on my feete.
Sai Isra’ilawa suka amsa, suka ce, “Za mu bi ta babbar hanya, in mu, ko dabbobinmu suka sha ruwanku, za mu biya. Mu dai muna so mu wuce ne kawai.”
20 Hee answered againe, Thou shalt not goe through. The Edom came out against him with much people, and with a mightie power.
Sai mutanen Edom suka sāke amsa suka ce, “Ba za ku bi nan ba dai.” Sai Edom ya fito da runduna mai ƙarfi da yawa gaske a kan Isra’ila.
21 Thus Edom denyed to giue Israel passage through his countrey: wherefore Israel turned away from him.
Da yake Edom suka ƙi su bar su su ratsa yankinsu, sai Isra’ila suka juya suka janye daga gare su.
22 And when the children of Israel with al the Congregation departed from Kadesh, they came vnto the mount Hor.
Dukan Jama’ar Isra’ilawa suka tashi daga Kadesh, suka zo Dutsen Hor.
23 And the Lord spake vnto Moses and to Aaron in the mount Hor neere the coast of the land of Edom, saying,
A Dutsen Hor, kusa da iyakar Edom, Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna,
24 Aaron shall be gathered vnto his people: for hee shall not enter into the lande, which I haue giuen vnto the children of Israel, because ye disobeyed my commandement at the water of Meribah.
“Haruna zai rasu. Ba zai shiga ƙasar da na ba Isra’ilawa ba, domin ku biyu, kun ƙi ku bi umarnina a ruwan Meriba.
25 Take Aaron and Eleazar his sonne, and bring them vp into the mount Hor,
Ka kawo Haruna da ɗansa Eleyazar, ka kai su a bisan Dutsen Hor.
26 And cause Aaron to put off his garmentes and put them vpon Eleazar his sonne: for Aaron shall be gathered to his fathers, and shall die there.
Ka tuɓe taguwar Haruna ka sa wa ɗansa Eleyazar, gama Haruna zai rasu a can.”
27 And Moses did as the Lord had commanded: and they went vp into the mount Hor, in the sight of all the Congregation.
Musa ya yi yadda Ubangiji ya umarta. Suka hau Dutsen Hor a idon dukan jama’a.
28 And Moses put off Aarons clothes, and put them vpon Eleazar his sonne: so Aaron dyed there in the top of the mount: and Moses and Eleazar came downe from off the mount.
Musa ya tuɓe taguwar Haruna, ya kuma sa wa Eleyazar ɗan Haruna. Nan kuwa Haruna ya mutu a bisa dutsen. Sa’an nan Musa da Eleyazar suka sauka daga dutsen,
29 When al the Congregation sawe that Aaron was dead, al the house of Israel wept for Aaron thirtie dayes.
sa’ad da dukan jama’a kuwa suka ji cewa Haruna ya mutu, sai dukan gidan Isra’ila suka yi makoki dominsa har kwana talatin.

< Numbers 20 >