< Numbers 14 >

1 Then all ye Congregation lifted vp their voice, and cryed: and the people wept that night,
A daren nan, sai dukan jama’ar suka tā da murya, suka yi kuka da ƙarfi.
2 And all the children of Israel murmured against Moses and Aaron: and the whole assemblie said vnto them, Would God we had died in the land of Egypt, or in this wildernesse: would God we were dead.
Dukan Isra’ilawa suka yi gunaguni a kan Musa da Haruna, dukan taron kuwa suka ce musu, “Da ma mun mutu a Masar! Ko kuma a wannan hamada ma!
3 Wherefore nowe hath the Lord brought vs into this lande to fall vpon the sworde? our wiues, and our children shall be a pray: were it not better for vs to returne into Egypt?
Don me Ubangiji yana kawo mu wannan ƙasa yă bar mu kawai mu mutu da takobi? A kuma kwashe matanmu da’ya’yanmu ganima. Ashe, bai fi mana mu koma Masar ba?”
4 And they said one to another, Let vs make a Captaine and returne into Egypt.
Sai suka ce wa junansu, “Mu naɗa wa kanmu shugaba, mu koma Masar.”
5 Then Moses and Aaron fell on their faces before all the assemblie of the Congregation of the children of Israel.
Sai Musa da Haruna suka fāɗi rubda ciki a gaban jama’ar Isra’ilawa da suka taru a can.
6 And Ioshua the sonne of Nun, and Caleb the sonne of Iephunneh two of them that searched the lande, rent their clothes,
Yoshuwa ɗan Nun da Kaleb ɗan Yefunne waɗanda suke tare da masu leƙo asirin ƙasar, suka yayyage tufafinsu
7 And spake vnto all the assemblie of the childre of Israel, saying, The land which we walked through to search it, is a very good lande.
suka ce wa dukan taron Isra’ilawa, “Ƙasar da muka ratsa, muka kuma leƙi asirinta, tana da kyau sosai.
8 If the Lord loue vs, he will bring vs into this land, and giue it vs, which is a land that floweth with milke and honie.
In Ubangiji ya ji daɗinmu, zai kai mu ƙasan nan, ƙasar da take zub da madara da zuma, yă kuwa ba mu ita.
9 But rebell not ye against the Lord, neither feare ye the people of the land: for they are but bread for vs: their shielde is departed from the, and the Lord is with vs, feare them not.
Sai dai kada ku tayar wa Ubangiji. Kada kuma ku ji tsoron mutane ƙasar, domin za mu gama da su. Kāriyarsu ta gama, amma Ubangiji yana nan tare da mu. Kada ku ji tsoronsu.”
10 And all the multitude saide, Stone them with stones: but the glory of the Lord appeared in the Tabernacle of the Congregation, before all the children of Israel.
Amma taron jama’a suka ce za su jajjefe su da duwatsu. Sai ɗaukakar Ubangiji ta bayyana a Tentin Sujada ga dukan Isra’ilawa.
11 And the Lord said vnto Moses, How long will this people prouoke me, and howe long will it be, yer they beleeue me, for al the signes which I haue shewed among them?
Ubangiji ya ce wa Musa, “Har yaushe mutanen nan za su rena ni? Har yaushe za su ƙi gaskata da ni, duk da yawan mu’ujizan da nake yi a cikinsu?
12 I will smite them with the pestilence and destroy them, and will make thee a greater nation and mightier then they.
Zan buge su duka da annoba, in hallaka su, amma zan mai da kai al’umma mai girma, da kuma ƙarfi fiye da su.”
13 But Moses saide vnto the Lord, When the Egyptians shall heare it, (for thou broughtest this people by thy power from among them)
Sai Musa ya ce wa Ubangiji, “Ai, Masarawa za su ji game da wannan! Da ikonka ka fitar da mutanen nan daga cikinsu.
14 Then they shall say to the inhabitants of this land, (for they haue heard that thou, Lord, art among this people, and that thou, Lord, art seene face to face, and that thy cloude standeth ouer them, and that thou goest before them by day time in a pillar of a cloude, and in a pillar of fire by night)
Za su kuwa gaya wa mutanen wannan ƙasa. Sun riga sun ji cewa kai, ya Ubangiji, kana tare da waɗannan mutane, kuma cewa kai, ya Ubangiji, an gan ka fuska da fuska, cewa girgijenka ya tsaya bisansu, cewa kana tafiya a gabansu cikin ginshiƙin girgije da rana, da ginshiƙin wuta kuma da dare.
15 That thou wilt kill this people as one man: so the heathen which haue heard the fame of thee, shall thus say,
In ka kashe dukan mutanen nan gaba ɗaya, al’ummai da suka ji wannan labari game da kai za su ce,
16 Because the Lord was not able to bring this people into the lande, which he sware vnto them, therefore hath he slaine them in the wildernesse.
‘Ubangiji ya kāsa kai waɗannan mutane a ƙasar da ya yi alkawari da rantsuwa ne, shi ya sa ya kashe su a hamada.’
17 And now, I beseech thee, let the power of my Lord be great, according as thou hast spoken, saying,
“Yanzu bari Ubangiji yă nuna ikonsa, kamar dai yadda ka furta.
18 The Lord is slowe to anger, and of great mercie, and forgiuing iniquitie, and sinne, but not making the wicked innocent, and visiting the wickednes of the fathers vpon the children, in the thirde and fourth generation:
‘Ubangiji mai jinkiri fushi ne, mai yawan ƙauna, mai gafarta zunubi da tawaye. Duk da haka ba ya ƙyale mai laifi, babu horo. Yana horin’ya’ya saboda zunubin iyayensu har tsara ta uku, da ta huɗu.’
19 Be mercifull, I beseech thee, vnto the iniquitie of this people, according to thy great mercie, and as thou hast forgiuen this people from Egypt, euen vntill nowe.
Bisa ga ƙaunarka mai girma, ka gafarta zunubin mutanen nan, kamar dai yadda ka gafarta musu daga lokacin da suka bar Masar har zuwa yanzu.”
20 And the Lord said, I haue forgiuen it, according to thy request.
Ubangiji ya amsa ya ce, “Na gafarta musu, yadda ka roƙa.
21 Notwithstanding, as I liue, all the earth shall be filled with the glory of the Lord.
Duk da haka, muddin ina raye, kuma muddin ɗaukakar Ubangiji ta cika dukan duniya,
22 For all those men which haue seene my glory, and my miracles which I did in Egypt, and in the wildernes, and haue tempted me this ten times, and haue not obeyed my voyce,
ko ɗaya daga cikinsu da suka ga ɗaukakata da mu’ujizai da na yi a Masar, da kuma a cikin hamada, da suka ƙi yin mini biyayya, suka kuma gwada ni har sau goma,
23 Certainely they shall not see the lande, whereof I sware vnto their fathers: neither shall any that prouoke me, see it.
ba ko ɗayansu da zai gan ƙasar da na yi alkawari da rantsuwa zan ba wa kakanninsu. Ba ko ɗaya da ya rena ni, da zai taɓa ganinta.
24 But my seruant Caleb, because he had another spirite, and hath followed me stil, euen him will I bring into the lande, whither he went, and his seede shall inherite it.
Amma domin Kaleb bawana ya kasance da ruhu dabam, ya kuma bi ni da zuciya ɗaya, zan kai shi cikin ƙasar da ya je, zuriyarsa kuwa za su gāje ta.
25 Nowe the Amalekites and the Canaanites remaine in the valley: wherefore turne backe to morowe, and get you into the wildernesse, by the way of the red Sea.
Da yake Amalekawa da Kan’aniyawa suna zama a kwarin, gobe sai ka koma baya, ka nufi wajen hamada ta hanyar Jan Teku.”
26 After, the Lord spake vnto Moses and to Aaron, saying,
Ubangiji ya ce wa Musa da Haruna,
27 How long shall I suffer this wicked multitude to murmure against me? I haue heard the murmurings of the children of Israel, which they murmure against me.
“Har yaushe wannan muguwar al’umma za tă yi gunaguni a kaina? Na ji koke-koken waɗannan Isra’ilawa masu gunaguni.
28 Tell them, As I liue (saith the Lord) I wil surely do vnto you, euen as ye haue spoken in mine eares.
Saboda haka ka gaya musu cewa, ‘Muddin ina raye, in ji Ubangiji, zan yi muku daidai da abin da na ji kuke faɗa.
29 Your carkeises shall fall in this wildernes, and all you that were counted through all your nombers, from twentie yeere olde and aboue, which haue murmured against me,
A cikin wannan hamadan, jikunanku za su fāɗi, kowanne a cikinku mai shekara ashirin ko fiye, wanda aka ƙirga shi cikin ƙidaya, wanda kuma ya yi gunaguni a kaina, da zai shiga wannan ƙasa.
30 Ye shall not doubtles come into the land, for the which I lifted vp mine hande, to make you dwell therein, saue Caleb the sonne of Iephunneh, and Ioshua the sonne of Nun.
Ba ko ɗaya daga cikinku da zai shiga ƙasar da na ɗaga hannu na rantse, za tă zama gidanku, sai dai Kaleb ɗan Yefunne da Yoshuwa ɗan Nun.
31 But your children, (which ye said shoulde be a pray) them will I bring in, and they shall knowe the lande which ye haue refused:
Amma game da’ya’yanku da kuka ce za a kwashe ganima, zan kawo su cikin ƙasar, su ji daɗin ƙasar wadda kuka ƙi.
32 But euen your carkeises shall fall in this wildernes,
Amma ku, jikunanku za su fāɗi a wannan hamada.
33 And your children shall wander in the wildernesse, fourtie yeeres, and shall beare your whoredomes, vntill your carkeises be wasted in the wildernesse.
’Ya’yanku za su zama makiyaya a nan, shekaru arba’in suna shan wahala domin rashin amincinku, har sai mutum na ƙarshe a cikinku ya kwanta a hamada.
34 After the number of the dayes, in the which ye searched out the lande, euen fourtie dayes, euery day for a yeere, shall ye beare your iniquity, for fourtie yeeres, and ye shall feele my breach of promise.
Shekaru arba’in, shekara ɗaya a madadi kwana ɗaya cikin kwanakin arba’in da kuka ɗauka kuka leƙi asirin ƙasa, za ku sha wahala saboda zunubanku, ku kuma san abin da ake nufi da sa ni in yi gāba da ku.’
35 I the Lord haue said, Certainely I will doe so to all this wicked company, that are gathered together against me: for in this wildernesse they shall be consumed, and there they shall die.
Ni, Ubangiji na faɗa, zan kuwa aikata waɗannan abubuwa a kan dukan muguwar jama’an nan da suka haɗa kai, suka tayar mini. Za su sadu da ƙarshensu a wannan hamada; a nan za su mutu.”
36 And the men which Moses had sent to search the land (which, when they came againe, made all the people to murmure against him, and brought vp a slander vpon the lande)
Saboda haka mutanen da Musa ya aika, su leƙo asirin ƙasar, waɗanda suka komo, suka sa taron jama’a su yi gunaguni a kansa saboda sun kawo rahoto mai banrazana a kan ƙasar,
37 Euen those men that did bring vp that vile slander vpon the land, shall die by a plague before the Lord.
waɗannan mutanen da suka kawo rahoto mai banrazana a kan ƙasar, annoba ta buge su, suka kuwa mutu a gaban Ubangiji.
38 But Ioshua the sonne of Nun, and Caleb the sonne of Iephunneh, of those men that went to search the land, shall liue.
Daga cikin mutanen da suka leƙo asirin ƙasar, Yoshuwa ɗan Nun, da Kaleb ɗan Yefunne ne, kaɗai suka rayu.
39 Then Moses tolde these sayings vnto all the children of Israel, and the people sorowed greatly.
Da Musa ya gaya wa dukan Isra’ilawa wannan labari, sai suka yi baƙin ciki ƙwarai.
40 And they rose vp earely in the morning, and gate them vp into the toppe of the mountaine, saying, Loe, we be readie, to goe vp to the place which the Lord hath promised: for wee haue sinned.
Kashegari da sassafe suka haura ta wajen ƙasa mai tudu suka ce, “Mun yi zunubi, za mu tafi inda Ubangiji ya yi alkawari.”
41 But Moses said, Wherefore transgresse yee thus the commandement of the Lord? it will not so come well to passe.
Amma Musa ya ce, “Don me kuke rashin biyayya da umarnin Ubangiji? Wannan ba zai yiwu ba!
42 Goe not vp (for the Lord is not among you) lest ye be ouerthrowe before your enemies.
Kada ku haura, domin Ubangiji, ba ya tare da ku. Magabtanku za su ci nasara a kanku,
43 For the Amalekites and the Canaanites are there before you, and ye shall fall by the sworde: for in as much as ye are turned away from the Lord, the Lord also will not be with you.
gama Amalekawa da Kan’aniyawa za su kara da ku a can. Domin kun juya daga Ubangiji, ba zai kasance da ku ba, za a kuma karkashe ku da takobi.”
44 Yet they presumed obstinately to goe vp to the top of the mountaine: but the Arke of the couenant of the Lord, and Moses departed not out of the campe.
Duk da haka, suka yi tsammani ba zai zama haka ba, sai suka haura ta wajen ƙasa mai tudu, Musa da akwatin alkawarin Ubangiji dai ba su gusa daga sansanin ba.
45 Then the Amalekites and the Canaanites, which dwelt in that mountaine, came downe and smote them, and consumed them vnto Hormah.
Sai Amalekawa da Kan’aniyawa mazaunan ƙasar tudu, suka gangaro suka auka musu, suka bubbuge su suka kokkore su har Horma.

< Numbers 14 >