< Nahum 2 >

1 The destroyer is come before thy face: keepe the munition: looke to the way: make thy loynes strong: increase thy strength mightily.
Mai hari yana matsowa a kanki, Ninebe. Ki tsare mafaka, ki yi gadin hanya ki sha ɗamara ki tattaro dukan ƙarfinki!
2 For the Lord hath turned away the glorie of Iaakob, as the glorie of Israel: for the emptiers haue emptied them out, and marred their vine branches.
Ubangiji zai maido da darajar Yaƙub, kamar ta Isra’ila, ko da yake masu washewa sun washe su suka kuma lalatar da inabinsu.
3 The shield of his mightie men is made red: the valiant men are in skarlet: the charets shalbe as in the fire and flames in the day of his preparation, and the firre trees shall tremble.
Garkuwoyin sojojinsa ja wur ne; jarumawansa suna sanye da kaya masu ruwan jan garura. Ƙarafan kekunan yaƙi suna walƙiya a ranar da aka shirya su; ana kaɗa māsu da bantsoro.
4 The charets shall rage in the streetes: they shall runne to and from in the hie wayes: they shall seeme like lampes: they shall shoote like the lightning.
Kekunan yaƙi sun zabura a tituna, suna kai da kawowa a dandali. Suna walƙiya kamar tocila suna sheƙawa a guje kamar walƙiya.
5 He shall remember his strong men: they shall stumble as they goe: they shall make haste to the walles thereof, and the defence shall bee prepared.
Ninebe ta tattara rundunarta, duk da haka sun yi ta tuntuɓe a kan hanyarsu. Sun ruga zuwa katangan birnin, sun sanya garkuwar kāriya a inda ya kamata.
6 The gates of the riuers shalbe opened, and the palace shall melt.
An buɗe ƙofofin rafuffukan sai wurin ya rurrushe.
7 And Huzzab the Queene shalbe led away captiue, and her maides shall leade her as with the voyce of doues, smiting vpon their breastes.
An umarta cewa birnin za tă tafi bauta, za a kuma yi gaba da su. Bayi’yan mata suna kuka kamar tattabaru suna buga ƙirjinsu.
8 But Nineueh is of olde like a poole of water: yet they shall flee away. Stande, stande, shall they crie: but none shall looke backe.
Ninebe tana kama da tafki, wanda ruwanta yana yoyo. Suna kuka suna cewa, “Ku tsaya! Ku tsaya,” amma ba wanda ya waiga.
9 Spoyle ye the siluer, spoyle the golde: for there is none ende of the store, and glorie of all the pleasant vessels.
A washe azurfa; a washe zinariya; dukiyarsu ba ta da iyaka, arzikinsu kuma ba ya ƙarewa.
10 She is emptie and voyde and waste, and the heart melteth, and the knees smite together, and sorowe is in all loynes, and the faces of the all gather blackenesse.
Ta zama wofi, an washe ta, an tuɓe ta! Zukata sun narke, gwiwoyi suna kaɗuwa, jikuna suna rawa, fuskoki duk sun kwantsare!
11 Where is the dwelling of the lyons, and the pasture of the lyons whelpes? where the lyon, and the lionesse walked, and the lyons whelpe, and none made them afrayde.
Ina kogon zakokin nan yake yanzu, inda suka ciyar da’ya’yansu, inda zaki da zakanya sukan shiga, da’ya’yansu, ba mai damunsu
12 The lyon did teare in pieces ynough for his whelpes, and woryed for his lyonesse, and filled his holes with praye, and his dennes with, spoyle.
Zaki ya kashe abin da ya ishe’ya’yansa ya kuma murɗe wuyan dabbobi ya cika wurin zamansa da abin da ya kama ya cika kogwanninsa da abin da ya kashe.
13 Beholde, I come vnto thee, sayeth the Lord of hostes, and I will burne her charets in the smoke, and the sworde shall deuoure thy yong lyons, and I will cut off thy spoyle from the earth, and the voyce of thy messengers shall no more be heard.
“Ina gāba da ke,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Zan ƙone kekunan yaƙinki, takobi kuma zai fafare’ya’yan zakokinki. Ba kuma zan bar miki namun jejin da za ki kashe a duniya ba. Ba kuwa za a ƙara jin muryar’yan saƙonki ba.”

< Nahum 2 >