< Micah 6 >

1 Hearken ye nowe what the Lord sayth, Arise thou, and contende before the mountaines, and let the hilles heare thy voyce.
Ku saurari abin da Ubangiji ya ce, “Tashi ku gabatar da ƙararku a gaban duwatsu; bari tuddai su ji abin da kuke so ku faɗa.
2 Heare ye, O mountaynes, the Lordes quarel, and ye mightie foundations of the earth: for the Lord hath a quarell against his people, and he will pleade with Israel.
“Ku saurara, ya ku duwatsu game da tuhumar da Ubangiji yake muku, ku ji, ku daɗaɗɗun tushin duniya. Gama Ubangiji yana da ƙara a kan mutanensa; yana tuhumar Isra’ila.
3 O my people, what haue I done vnto thee? or wherin haue I grieued thee? testifie against me.
“Ya ku mutanena, me na yi muku? Ta yaya na nawaita muku? Ku amsa mini.
4 Surely I brought thee vp out of the land of Egypt, and redeemed thee out of the house of seruants, and I haue sent before thee, Moses, Aaron, and Miriam.
Na fito da ku daga ƙasar Masar na kuma’yantar da ku daga ƙasar bauta. Na aika da Musa yă jagorance ku, haka ma Haruna da Miriyam.
5 O my people, remember nowe what Balak King of Moab had deuised, and what Balaam the sonne of Beor answered him, from Shittim vnto Gilgal, that ye may knowe the righteousnes of the Lord.
Ya ku mutanena, ku tuna abin da Balak sarkin Mowab ya ƙulla da kuma amsar da Bala’am ɗan Beyor ya bayar. Ku tuna da tafiyarku daga Shittim zuwa Gilgal, don ku san ayyukan adalcin Ubangiji.”
6 Wherewith shall I come before the Lord, and bowe my selfe before the hie God? Shall I come before him with burnt offrings, and with calues of a yeere olde?
Da me zan zo a gaban Ubangiji in rusuna a gaban Maɗaukaki Allah? Shin, zan zo ne a gabansa da hadaya ta ƙonawa, da ɗan maraƙi bana ɗaya?
7 Will the Lord be pleased with thousands of rams, or with ten thousand riuers of oyle? shall I giue my first borne for my transgression, euen the fruite of my bodie, for the sinne of my soule?
Ubangiji zai ji daɗin hadayar raguna dubbai da kuma rafuffukan mai dubbai goma? Zan ba da ɗan farina ne don laifina, ko’ya’yan jikina domin zunubin raina?
8 He hath shewed thee, O man, what is good, and what the Lord requireth of thee: surely to doe iustly, and to loue mercie, and to humble thy selfe, to walke with thy God.
Ya nuna maka, ya mutum, abin da yake mai kyau. Me Ubangiji yake bukata daga gare ka kuwa shi ne ka yi gaskiya ka so aikata jinƙai ka kuma yi tafiya da tawali’u a gaban Allah.
9 The Lordes voyce cryeth vnto the citie, and the man of wisedome shall see thy name: Heare the rodde, and who hath appoynted it.
Ku saurara! Ubangiji yana kira ga birni, a ji tsoron sunana kuwa hikima ce, “Ku kasa kunne ga sandan nan da kuma wannan wanda ya naɗa.
10 Are yet the treasures of wickednes in the house of the wicked, and the scant measure, that is abominable?
Har yanzu zan manta, ya muguwar gida da dukiyarki da kika samu a muguwar hanya zan kuma manta da bugaggen mudun awo wanda ake zargi?
11 Shall I iustifie the wicked balances, and the bag of deceitfull weightes?
Zan kuɓutar da mutumin da yake da ma’auni na rashin gaskiya, da kuma buhun ma’aunan ƙarya?
12 For the rich men thereof are full of crueltie, and the inhabitants thereof haue spoken lyes, and their tongue is deceitfull in their mouth.
Attajiranta masu fitina ne; mutanenta kuma maƙaryata ne harsunansu kuwa suna yaudara.
13 Therefore also will I make thee sicke in smiting thee, and in making thee desolate, because of thy sinnes.
Saboda haka, zan hallaka ku in lalace ku saboda zunubanku.
14 Thou shalt eate and not be satisfied, and thy casting downe shall be in the mids of thee, and thou shalt take holde, but shalt not deliuer: and that which thou deliuerest, will I giue vp to the sworde.
Za ku ci amma ba za ku ƙoshi ba, cikinku zai zama babu kome Za ku tattara amma ba za ku yi ajiyar kome ba, gama abin da kuka yi ajiya zan ba wa takobi.
15 Thou shalt sowe, but not reape: thou shalt treade the oliues, but thou shalt not anoint thee with oyle, and make sweete wine, but shalt not drinke wine.
Za ku yi shuki amma ba za ku girba ba; za ku matse zaitun amma ba za ku yi amfani da mai wa kanku ba, za ku tattaka’ya’yan inabi amma ba za ku sha ruwan inabin ba.
16 For the statutes of Omri are kept, and all the maner of the house of Ahab, and ye walke in their counsels, that I should make thee waste, and the inhabitants thereof an hissing: therefore ye shall beare the reproche of my people.
Kuna kiyaye ƙa’idodin Omri da dukan ayyukan gidan Ahab kun kuma bi al’adunsu. Saboda haka, zan maishe ku kufai in mai da ku abin dariya a cikin mutane, za ku sha reni a wurin al’ummai.”

< Micah 6 >