< Micah 4 >

1 But in the last dayes it shall come to passe, that the mountaine of the House of the Lord shall be prepared in the toppe of the mountaines, and it shall bee exalted aboue the hilles, and people shall flowe vnto it.
A kwanakin ƙarshe za a kafa dutsen haikalin Ubangiji yă zama babba a cikin duwatsu. Za a ɗaga shi sama da tuddai, mutane kuma za su riƙa ɗunguma zuwa gare shi.
2 Yea, many nations shall come and say, Come, and let vs goe vp to the Mountaine of the Lord, and to the House of the God of Iaakob, and hee will teache vs his wayes, and we wil walke in his pathes: for the Lawe shall goe forth of Zion, and the worde of the Lord from Ierusalem.
Al’ummai da yawa za su zo su ce, “Ku zo, bari mu haura zuwa dutsen Ubangiji, zuwa gidan Allah na Yaƙub. Zai koya mana hanyoyinsa, don mu yi tafiya cikin hanyoyinsa.” Doka za tă fita daga Sihiyona, maganar Ubangiji kuma daga Urushalima.
3 And he shall iudge among many people, and rebuke mightie nations a farre off, and they shall breake their swordes into mattockes, and their speares into sithes: nation shall not lift vp a sword against nation, neither shall they learne to fight any more.
Zai shari’anta tsakanin mutane yă kuma sulhunta tsakanin manyan al’ummai nesa da kuma kusa. Har su mai da takubansu su zama garemani, māsunsu kuma su zama wuƙaƙen askin itace. Al’umma ba za tă ɗauki takobi gāba da wata al’umma ba, ko a yi horarwa don yaƙi.
4 But they shall sit euery man vnder his vine, and vnder his figge tree, and none shall make them afraid: for the mouth of the Lord of hostes hath spoken it.
Kowa zai zauna a tushen kuringar inabinsa da tushen ɓaurensa, kuma ba wanda zai tsoratar da su, gama Ubangiji Maɗaukaki ne ya faɗa.
5 For all people will walke euery one in the name of his God, and we will walke in the Name of the Lord our God, for euer and euer.
Dukan al’ummai za su iya tafiya a cikin sunan allolinsu; mu dai za mu yi tafiya a cikin sunan Ubangiji Allahnmu har abada abadin.
6 At the same day, saith the Lord, will I gather her that halteth, and I will gather her that is cast out, and her that I haue afflicted.
“A wannan rana,” in ji Ubangiji, “zan tattara guragu; zan kuma tara masu zaman bauta, da waɗanda na sa suka damu.
7 And I will make her that halted, a remnant, and her that was cast farre off, a mightie nation: and the Lord shall reigne ouer them in Mount Zion, from hence forth euen for euer.
Zan mai da guragu su zama raguwa, waɗanda aka kora, su zama al’umma mai ƙarfi. Ubangiji zai yi mulkinsu a Dutsen Sihiyona daga wannan rana da kuma har abada.
8 And thou, O towre of the flock, the strong holde of the daughter Zion, vnto thee shall it come, euen the first dominion, and kingdome shall come to the daughter Ierusalem.
Game da ke, ya hasumiyar tsaron garke, Ya mafaka Diyar Sihiyona, za a maido miki da mulkinki na dā, sarauta kuma za tă zo wa Diyar Urushalima.”
9 Nowe why doest thou crie out with lamentation? is there no King in thee? is thy counseller perished? for sorowe hath taken thee, as a woman in trauaile.
Don me yanzu kike kuka da ƙarfi, ba ki da sarki ne? Masu shawararki sun hallaka ne, da zafi ya cika ki kamar mace mai naƙuda?
10 Sorow and mourne, O daughter Zion, like a woman in trauaile: for nowe shalt thou goe foorth of the citie, and dwel in the field, and shalt goe into Babel, but there shalt thou be deliuered: there the Lord shall redeeme thee from the hand of thine enemies.
Ki yi birgima cikin zafin azaba, ya Diyar Sihiyona, kamar macen da take naƙuda, don yanzu dole ki bar birni ki kafa sansani a filin Allah. Za ki tafi Babilon; a can za a kuɓutar da ki. A can ne Ubangiji zai fanshe ki daga hannun maƙiyanki.
11 Nowe also many nations are gathered against thee, saying, Zion shalbe condemned and our eye shall looke vpon Zion.
Amma yanzu al’ummai da yawa suna gāba da ke. Suna cewa, “Bari a ƙazantar da ita, bari mu zuba wa Sihiyona ido.”
12 But they knowe not the thoughtes of the Lord: they vnderstand not his counsell, for he shall gather them as the sheaues in the barne.
Amma ba su san tunanin Ubangiji ba; ba su fahimci shirinsa ba, shi da ya tattara su kamar dammuna a masussuka.
13 Arise, and thresh, O daughter Zion: for I will make thine horne yron, and I will make thine hooues brasse, and thou shalt breake in pieces many people: and I will consecrate their riches vnto the Lord, and their substance vnto the ruler of the whole worlde.
“Ki tashi ki yi sussuka, ya Diyar Sihiyona, gama zan ba ki ƙahonin ƙarfe; zan ba ki kofatan tagulla domin ki ragargaje al’ummai masu yawa.” Za ki ba Ubangiji dukan dukiyarsu da suka tara ta hanyar zamba, wadatarsu kuma ga Ubangiji dukan duniya.

< Micah 4 >