< Malachi 2 >

1 And now, O ye Priests, this commandement is for you.
“Yanzu fa wannan gargaɗi dominku ne, ku firistoci.
2 If yee will not heare it, nor consider it in your heart, to giue glory vnto my Name, sayth the Lord of hostes, I will euen sende a curse vpon you, and will curse your blessings: yea, I haue cursed them alreadie, because yee doe not consider it in your heart.
In ba ku saurara ba, in kuma ba ku sa zuciyarku ga girmama sunana ba, zan aukar muku da la’ana, zan kuma la’antar da albarkunku. I, na riga na la’anta su, domin ba ku sa zuciyarku ga girmama ni ba, in ji Ubangiji Maɗaukaki.
3 Behold, I wil corrupt your seede, and cast dongue vpon your faces, euen the dongue of your solemne feastes, and you shall be like vnto it.
“Saboda ku zan tsawata wa zuriyarku; zan watsa kashin dabbobin hadayunku a fuskokinku, a kuma kwashe ku tare da shi.
4 And yee shall know, that I haue sent this commandement vnto you, that my couenant, which I made with Leui, might stand, sayeth the Lord of hostes.
Za ku kuwa san cewa ni ne na aika muku da wannan gargaɗi domin alkawarina da Lawi yă ci gaba,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
5 My couenant was with him of life and peace, and I gaue him feare, and he feared mee, and was afraid before my Name.
“Alkawarina da shi, alkawari ne na rai da salama, wanda na ba shi; domin yă girmama ni, ya kuwa girmama ni, ya kuma ji tsoron sunana ƙwarai.
6 The lawe of trueth was in his mouth, and there was no iniquitie founde in his lippes: hee walked with me in peace and equitie, and did turne many away from iniquitie.
Umarnin gaskiya yana a bakinsa, ba a kuma sami wani ƙarya a leɓunansa ba. Ya yi tafiya tare da ni cikin salama da adalci, ya kuwa juyo da mutane masu yawa daga zunubi.
7 For the Priestes lippes shoulde preserue knowledge, and they shoulde seeke the Lawe at his mouth: for he is the messenger of the Lord of hostes.
“Gama ya kamata leɓunan firist su kiyaye ilimi, ya kamata kuma mutane su nemi umarni daga bakinsa, domin shi ne manzon Ubangiji Maɗaukaki.
8 But yee are gone out of the way: yee haue caused many to fall by the Lawe: yee haue broken the couenant of Leui, sayeth the Lord of hostes.
Amma sai kuka kauce hanya, ta wurin koyarwarku kuma kuka sa mutane da yawa suka yi tuntuɓe; kun keta alkawarin da na yi da Lawi,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
9 Therefore haue I also made you to be despised, and vile before all the people, because yee kept not my wayes, but haue beene partiall in the Lawe.
“Saboda haka na sa a rena ku, a kuma wulaƙanta ku a gaban dukan mutane, domin ba ku bi hanyoyina ba amma kuka nuna sonkai a al’amuran shari’a.”
10 Haue we not all one father? hath not one God made vs? why doe we transgresse euery one against his brother, and breake the couenant of our fathers?
Ashe, ba Mahaifi guda dukanmu muke da shi ba? Ba Allah ɗaya ne ya halicce mu ba? Don me muka keta alkawarin kakanninmu ta wurin cin amanar juna?
11 Iudah hath transgressed, and an abomination is committed in Israel and in Ierusalem: for Iudah hath defiled the holinesse of the Lord, which hee loued, and hath maried the daughter of a strange God.
Yahuda ya ci amana. An yi abin kunya a Isra’ila da kuma a Urushalima. Yahuda ya ƙazantar da wuri mai tsarkin da Ubangiji yake ƙauna, ta wurin auren’yar wani baƙon allah.
12 The Lord will cut off the man that doeth this: both the master and the seruaunt out of the Tabernacle of Iaacob, and him that offereth an offering vnto the Lord of hostes.
Game da mutumin da ya aikata wannan, ko wane ne shi, bari Ubangiji yă yanke shi daga tentunan Yaƙub, ko da ma ya kawo hadayu ga Ubangiji Maɗaukaki.
13 And this haue ye done againe, and couered the altar of the Lord with teares, with weeping and with mourning: because the offering is no more regarded, neither receiued acceptably at your handes.
Ga kuma wani abin da kuke yi. Kukan cika bagaden Ubangiji da hawaye. Kukan yi kuka kuna ihu gama Ubangiji ba ya mai da hankali ga hadayunku ko yă karɓe su da farin ciki.
14 Yet yee say, Wherein? Because the Lord hath beene witnesse betweene thee and the wife of thy youth, against whome thou hast transgressed: yet is shee thy companion, and the wife of thy couenant.
Kukan ce, “Don me ba ya karɓan hadayunmu?” Ai, domin Ubangiji ya zama shaida tsakaninka da matar ƙuruciyarka, gama ka keta amanar da ka yi mata, ko da yake ita abokiyar zamanka ce, matar aurenka ta alkawari.
15 And did not hee make one? yet had hee abundance of spirit: and wherefore one? because he sought a godly seede: therefore keepe your selues in your spirit, and let none trespasse against the wife of his youth.
Ashe, Ubangiji bai maishe su ɗaya ba? Cikin jiki da ruhu, su nasa ne. Me ya sa suke ɗaya? Domin yana neman’ya’ya masu tsoron Allah. Saboda haka sai ka lura da kanka, kada kuma ka ci amanar matar ƙuruciyarka.
16 If thou hatest her, put her away, sayeth the Lord God of Israel, yet he couereth the iniurie vnder his garment, saieth the Lord of hosts: therefore keepe your selues in your spirite, and transgresse not.
“Na ƙi kisan aure,” in ji Ubangiji, Allah na Isra’ila. “Na kuma ƙi mutumin da ya rufe kansa da tashin hankali kamar riga,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. Saboda haka sai ka lura da kanka, kada kuma ka ci amana.
17 Yee haue wearied the Lord with your woordes: yet yee say, Wherein haue we wearied him? When ye say, Euery one that doeth euill, is good in the sight of the Lord, and he deliteth in them. Or where is the God of iudgement?
Kun sa Ubangiji Maɗaukaki ya gaji da maganganunku. Sai kuka ce, “Yaya muka sa ya gaji?” Kun yi haka ta wurin cewa, “Duk waɗanda suke aikata mugunta, mutanen kirki ne a gaban Ubangiji, yana kuwa jin daɗinsu,” kuna kuma cewa, “Ina Allah mai adalci yake?”

< Malachi 2 >