< Luke 7 >

1 When hee had ended all his sayings in the audience of the people, he entred into Capernaum.
Bayan da Yesu ya gama fadar dukan abubuwan da zai fadi a jin kunnen dukan mutanen, sai ya shiga Kafarnahum.
2 And a certaine Ceturions seruant was sicke and readie to die, which was deare vnto him.
Bawan wani jarumi, wanda yake kauna, ba shi da lafiya har ma ya kusa mutuwa.
3 And when he heard of Iesus, hee sent vnto him the Elders of the Iewes, beseeching him that he would come, and heale his seruant.
Amma da ya ji labarin Yesu, jarumin ya aiki wadansu dattawan Yahudawa, ya ce a roki Yesu ya zo ya ceci bawansa daga mutuwa.
4 So they came to Iesus, and besought him instantly, saying that hee was worthy that hee should doe this for him:
Sa'adda su ka zo kusa da Yesu, su ka roke shi da gaske, cewa, “Wannan ya isa ka yi masa haka,
5 For he loueth, said they, our nation, and he hath built vs a Synagogue.
saboda shi mai kaunar kasar mu ne, kuma shi ne ya gina mana majami'a.
6 Then Iesus went with them: but when he was now not farre from the house, the Centurion sent friendes to him, saying vnto him, Lord, trouble not thy selfe: for I am not worthy that thou shouldest enter vnder my roofe:
Sai Yesu ya tafi tare da su. Amma sa'adda ya zo kusa da gidan mutumin, jarumin ya aiki abokansa su ka ce da shi, “Ubangiji kada ka damu domin ni ban isa ka zo gida na ba.
7 Wherefore I thought not my selfe worthy to come vnto thee: but say the word, and my seruant shalbe whole:
Shi ya sa na ga ban isa in zo wurinka ba, ka yi magana kadai bawa na kuwa zai warke.
8 For I likewise am a man set vnder authoritie, and haue vnder mee souldiers, and I say vnto one, Goe, and he goeth: and to another, Come, and hee commeth: and to my seruant, Doe this, and he doeth it.
Gama ni ma mutum ne mai iko, ina da sojoji karkashina. Ina iya cewa da wannan, 'Ka je' sai ya tafi, in kuma ce da wani 'ka zo' sai ya zo, in kuma ce da bawa na, 'Yi kaza,' sai ya yi.”
9 When Iesus heard these things, he marueiled at him, and turned him, and said to the people, that followed him, I say vnto you, I haue not found so great faith, no not in Israel.
Sa'adda Yesu ya ji haka, ya yi mamakin mutumin, ya juya wajen taron da su ke biye da shi, ya ce, “Na gaya maku, ko a cikin Isra'ila ban sami wani mai bangaskiya irin wannan ba”
10 And when they that were sent, turned backe to the house, they founde the seruant that was sicke, whole.
Daga nan wadanda a ka aika, suka dawo gida suka tarar da bawan cikin koshin lafiya.
11 And it came to passe the day after, that he went into a citie called Nain, and many of his disciples went with him, and a great multitude.
Wani lokaci bayan wannan, ya zama Yesu yana tafiya wani gari da ake kira Na'im. Almajiransa su na tare da shi, da kuma taron mutane masu yawa.
12 Nowe when hee came neere to the gate of the citie, behold, there was a dead man caried out, who was the onely begotten sonne of his mother, which was a widowe, and much people of the citie was with her.
Sa'adda ya kusa da kofar garin, sai ga wani matacce ana dauke da shi. Kuma shi kadai ne da a wurin mahaifiyarsa. Ita kuwa gwauruwa ce, mutane da dama daga cikin gari suna tare da ita.
13 And when the Lord sawe her, he had compassion on her, and said vnto her, Weepe not.
Da ganin ta, sai Ubangiji ya cika da tausayi a game da ita ya ce da ita, “Kada ki yi kuka.”
14 And he went and touched the coffin (and they that bare him, stoode still) and he said, Yong man, I say vnto thee, Arise.
Sai ya zo ya taba makarar, sai masu dauke da shi su ka tsaya. Ya ce 'Saurayi na ce ma ka ka tashi.”
15 And he that was dead, sate vp, and began to speake, and he deliuered him to his mother.
Sai mataccen ya tashi ya fara yin magana. Sai Yesu ya ba mahaifiyar danta.
16 Then there came a feare on them all, and they glorified God, saying, A great Prophet is risen among vs, and God hath visited his people.
Sai tsoro ya kama su duka. Su ka kama yabon Allah, su na cewa, “An ta da wani annabi mai girma a cikinmu” kuma “Allah ya dubi mutanensa.”
17 And this rumour of him went foorth throughout all Iudea, and throughout all the region round about.
Wannan labari na Yesu, ya ba zu a cikin dukan Yahudiya da yankuna da su ke kewaye.
18 And the disciples of Iohn shewed him of all these things.
Almajiran Yahaya suka gaya masa dukan wadannan abubuwa.
19 So Iohn called vnto him two certaine men of his disciples, and sent them to Iesus, saying, Art thou hee that should come, or shall we waite for another?
Sai Yahaya ya kira biyu daga cikin almajiransa, ya aike su wurin Ubangiji, suka ce da shi, “Kai ne mai zuwan nan, ko akwai wani wanda za mu saurari zuwansa?”
20 And when the men were come vnto him, they said, Iohn Baptist hath sent vs vnto thee, saying, Art thou hee that should come, or shall we waite for another?
Sa'adda suka zo kusa da Yesu, sai mutanen suka ce, “Yahaya Mai Baftisma, ya aiko mu, mu tambaya, “Kai ne mai zuwan nan, ko akwai wani wanda za mu saurari zuwansa?”
21 And at that time, he cured many of their sickenesses, and plagues, and of euill spirites, and vnto many blinde men he gaue sight freely.
A cikin wannan lokaci, ya warkar da mutane da yawa daga cututtuka da matsaloli da miyagun ruhohi. Makafi da yawa sun sami ganin gari.
22 And Iesus answered, and saide vnto them, Goe your wayes and shewe Iohn, what things ye haue seene and heard: that the blinde see, the halt goe, the lepers are cleansed, the deafe heare, the dead are raised, and the poore receiue the Gospel.
Yesu, ya amsa ya ce masu, “Bayan kun tafi, ku ba Yohanna rahoton abin da ku ka ji da abin da ku ka gani. Makafi suna ganin gari, guragu suna tafiya, ana kuma tsarkake kutare. Kurame suna ji, ana tayar da matattu, ana gaya wa matalauta labari mai dadi.
23 And blessed is hee, that shall not be offended in me.
Mai albarka ne mutumin da ya tsaya a kan ba da gaskiya gare ni saboda ayukan da na ke yi.”
24 And when the messengers of Iohn were departed, hee began to speake vnto the people, of Iohn, What went ye out into the wildernes to see? A reede shaken with the winde?
Bayan da mutanen da Yahaya ya aiko suka tafi, Yesu ya fara yi wa taron magana game da Yahaya. “Me ku ka tafi ku gani a cikin hamada, ciyawa wadda iska ta ke girgizawa?
25 But what went ye out to see? A man clothed in soft rayment? beholde, they which are gorgeously apparelled, and liue delicately, are in Kings courtes.
Amma me ku ka tafi domin ku gani, mutum mai saye da tufafi masu taushi? Duba mutanen da su ke saye da tufafi masu daraja, kuma suna rayuwa cikin jin dadi suna fadar sarakuna.
26 But what went ye foorth to see? A Prophet? yea, I say to you, and greater then a Prophet.
Amma me ku ka tafi domin ku gani, annabi ne? I, ina gaya ma ku, ya ma fi annabi.
27 This is he of whom it is written, Beholde, I sende my messenger before thy face, which shall prepare thy way before thee.
Wannan shine wanda aka rubuta a kansa, “Duba, ina aika manzo na a gabanka, wanda za ya shirya maka hanya a gabanka.
28 For I say vnto you, there is no greater Prophet then Iohn, among them that are begotten of women: neuerthelesse, hee that is the least in the kingdome of God, is greater then he.
Ina gaya maku, a cikin wadanda mata suka haifa, ba wanda ya fi Yahaya girma. Duk da haka, wanda ya fi kankanta a mulkin Allah, ya fi shi girma.
29 Then all the people that heard, and the Publicanes iustified God, being baptized with the baptisme of Iohn.
Sa'anda dukan mutane suka ji haka, har da ma su karbar haraji, suka shaida Allah mai adalci ne. Su na cikin wadanda Yahaya ya yi wa baftisma.
30 But the Pharises and the expounders of the Law despised the counsell of God against themselues, and were not baptized of him.
Amma Farisawa da wadanda su ke kwararru a cikin shari'ar Yahudawa, wadanda ba shi ne ya yi masu baftisma ba, suka yi watsi da hikimar Allah don kansu.
31 And the Lord saide, Whereunto shall I liken the men of this generation? and what thing are they like vnto?
Sa'annan Yesu ya ce, “Da me zan kamanta mutanen wannan zamani? Da me suka yi kama?
32 They are like vnto litle children sitting in the market place, and crying one to another, and saying, We haue piped vnto you, and ye haue not daunced: we haue mourned to you, and ye haue not wept.
Suna kama da yaran da suke wasa a kasuwa, wadanda suke magana da junansu suna cewa, “Mun yi maku busa, ba ku yi rawa ba. Mun yi makoki, ba ku yi kuka ba.”
33 For Iohn Baptist came, neither eating bread, nor drinking wine: and ye say, He hath the deuil.
Haka, Yahaya ya zo, bai ci gurasa ba, bai sha ruwan inabi ba, amma ku ka ce, 'Aljani ne yake mulkinsa.
34 The Sonne of man is come, and eateth and drinketh: and ye say, Beholde, a man which is a glutton, and a drinker of wine, a friend of Publicanes and sinners:
Dan Mutum, ya zo, yana ci, yana sha, amma, kuka ki shi, kuna cewa dubi mutum mai hadama, mai shan ruwan inabi da yawa, abokin masu karbar haraji da masu zunubi!
35 But wisdome is iustified of all her children.
Amma hikimar Allah tana shaidar dukan 'yayanta.”
36 And one of the Pharises desired him that hee would eate with him: and hee went into the Pharises house, and sate downe at table.
Wata rana wani Bafarise, ya roki Yesu ya je ya ci abinci tare da shi. Bayan da Yesu ya shiga gidan Bafarisen, ya zauna a teburi domin ya ci abinci.
37 And beholde, a woman in the citie, which was a sinner, when she knewe that Iesus sate at table in the Pharises house, shee brought a boxe of oyntment.
Sai ga wata mace mai zunubi, ta fito daga cikin birni. Sa'anda ta ji labari Yesu yana gidan Bafarisen, domin ya ci abinci. Ta dauki tandun mai na alabastar mai kamshi.
38 And shee stoode at his feete behinde him weeping, and began to wash his feete with teares, and did wipe them with the heares of her head, and kissed his feete, and anoynted them with the oyntment.
Ta tsaya kusa da Yesu tana kuka. Ta fara jika kafafunsa da hawayenta, tana shafe kafafunsa da gashin kanta. Tana yi wa kafafunsa sumba, tana shafe su da turare.
39 Nowe when the Pharise which bade him, saw it, he spake within himselfe, saying, If this man were a Prophet, hee woulde surely haue knowen who, and what maner of woman this is which toucheth him: for she is a sinner.
Sa'anda Bafarisen da ya gaiyaci Yesu, ya ga haka, sai ya yi tunani a cikin ransa, da cewa, “In da wannan mutum annabi ne, da ya gane ko wacce irin mace ce, wannan da take taba shi, ita mai zunubi ce.”
40 And Iesus answered, and saide vnto him, Simon, I haue somewhat to say vnto thee. And he said, Master, say on.
Yesu ya amsa ya ce masa, “Siman, ina so in gaya maka wani abu.” Ya ce, “malam sai ka fadi!”
41 There was a certaine lender which had two detters: the one ought fiue hundreth pence, and the other fiftie:
Yesu ya ce, “wani mutum mai ba da bashi yana bin wadansu mutane su biyu kudi, yana bin dayan sule dari, dayan kuma yana bin sa sule hamsin.
42 When they had nothing to pay, he forgaue them both: Which of them therefore, tell mee, will loue him most?
Da yake ba su da kudin da za su iya biyan sa, sai ya yafe masu, su duka biyu. A cikin su biyu, wanne ne zai fi nuna kauna ga wannan mutum?”
43 Simon answered, and said, I suppose that he, to whom he forgaue most. And he said vnto him, Thou hast truely iudged.
Siman ya amsa ya ce, “Ina tsammani wanda ya yafe wa kudi da yawa.” Yesu ya amsa ya ce masa, “Ka shari'anta dai dai.”
44 Then he turned to the woman, and said vnto Simon, Seest thou this woman? I entred into thine house, and thou gauest mee no water to my feete: but she hath washed my feete with teares, and wiped them with the heares of her head.
Yesu ya juya wajen matar, ya ce da Siman, “Ka ga matan nan. Na shiga gidanka. Ba ka ba ni ruwa domin kafafuna ba, amma ita ta ba ni, da hawayenta ta wanke kafafuna, ta kuma shafe su da gashin kanta.
45 Thou gauest me no kisse: but she, since the time I came in, hath not ceased to kisse my feete.
Kai ba ka yi ma ni sumba ba, amma ita ta yi, tun sa'adda na shigo nan ba ta dena sumbatar kafafuna ba.
46 Mine head with oyle thou didest not anoint: but she hath anoynted my feete with oyntment.
Kai ba ka shafe kai na da mai ba, amma ita ta shafe kafafuna da turare.
47 Wherefore I say vnto thee, many sinnes are forgiuen her: for she loued much. To whom a litle is forgiuen, he doeth loue a litle.
Saboda haka, ita wadda ta ke da zunubi da yawa ta bayar da mai yawa, ta kuma nuna kauna mai yawa. Amma shi wanda aka gafarta wa kadan, ya kuma nuna kauna kadan.”
48 And he saide vnto her, Thy sinnes are forgiuen thee.
Daga nan sai ya ce mata, “An gafarta zunubanki.”
49 And they that sate at table with him, began to say within themselues, Who is this that euen forgiueth sinnes?
Wadanda su ke a nan zaune tare da shi suka fara magana da junansu, “Wanene wannan wanda har yake gafarta zunubai?
50 And he said to the woman, Thy faith hath saued thee: goe in peace.
Sai Yesu ya ce da matar, “Bangaskiyarki ta cece ki. Ki tafi da salama.”

< Luke 7 >