< Luke 5 >

1 Then it came to passe, as the people preassed vpon him to heare the word of God, that he stoode by the lake of Gennesaret,
Wata rana, Yesu yana tsaye a bakin Tafkin Gennesaret, mutane kuma suna ta matsawa kewaye da shi, domin su ji maganar Allah,
2 And sawe two shippes stand by the lakes side, but the fishermen were gone out of them, and were washing their nettes.
sai ya hangi jiragen ruwa biyu a bakin tafkin, waɗanda masu kamun kifi suka bari suna wankin abin kamun kifinsu.
3 And he entred into one of the ships, which was Simons, and required him that he would thrust off a litle from the land: and he sate downe, and taught the people out of the ship.
Sai ya shiga ɗaya jirgin ruwan da yake na Siman, ya kuma roƙe shi yă tura shi kaɗan daga gaci. Sai ya zauna a jirgin ruwan, ya koyar da mutane daga ciki.
4 Now when he had left speaking, he sayd vnto Simon, Lanch out into the deepe, and let downe your nettes to make a draught.
Da ya gama magana, sai ya ce wa Siman, “Ka tuƙa jirgin zuwa inda akwai zurfi, ka saukar da abin kamun kifinka ka kama kifi.”
5 Then Simon answered, and sayd vnto him, Master, we haue trauailed sore all night, and haue taken nothing: neuerthelesse at thy worde I will let downe the net.
Siman ya amsa ya ce, “Ranka yă daɗe, duk dare mun yi ta fama ba mu kama kome ba, amma tun da ka ce haka, zan saki abin kamun kifin.”
6 And when they had so done, they enclosed a great multitude of fishes, so that their net brake.
Da suka yi haka, sai suka kama kifi da yawa, har abin kamun kifinsu suka fara tsintsinkewa.
7 And they beckened to their parteners, which were in the other ship, that they shoulde come and helpe them, who came then, and filled both the ships, that they did sinke.
Sai suka kira abokansu a ɗaya jirgin, su zo su taimake su, suka kuwa zo. Suka cika jiragen biyu da kifi cif, har jiragen suka fara nutsewa.
8 Now when Simon Peter saw it, he fel down at Iesus knees, saying, Lord, go from me: for I am a sinfull man.
Da Siman Bitrus ya ga wannan, sai ya fāɗi a gaban Yesu ya ce, “Rabu da ni, Ubangiji. Ni mai zunubi ne!”
9 For he was vtterly astonied, and all that were with him, for the draught of fishes which they tooke.
Gama mamaki ya kama shi da abokansa duka, saboda yawan kifin da suka kama.
10 And so was also Iames and Iohn the sonnes of Zebedeus, which were companions with Simon. Then Iesus sayde vnto Simon, Feare not: from henceforth thou shalt catch men.
Yaƙub da Yohanna,’ya’yan Zebedi, abokan aikin Siman su ma suka yi mamaki. Sai Yesu ya ce wa Siman, “Kada ka ji tsoro, daga yanzu za ka riƙa kama mutane ne.”
11 And when they had brought the ships to land, they forsooke all, and followed him.
Sai suka jawo jiragen ruwansu zuwa gaci, suka bar kome da kome, suka bi shi.
12 Nowe it came to passe, as he was in a certaine citie, beholde, there was a man full of leprosie, and when he sawe Iesus, he fell on his face, and besought him, saying, Lord, if thou wilt, thou canst make me cleane.
Yayinda Yesu yake ɗaya daga cikin garuruwan nan, sai ga wani mutum wanda kuturta ta ci ƙarfinsa. Da ganin Yesu, sai ya fāɗi da fuskarsa a ƙasa, ya roƙe shi ya ce, “Ubangiji, in ka yarda, kana iya ka tsabtacce ni.”
13 So he stretched forth his hand, and touched him, saying, I will, be thou cleane. And immediately the leprosie departed from him.
Yesu ya miƙa hannunsa ya taɓa mutumin ya ce, “Na yarda, ka zama da tsabta!” Nan da nan, sai kuturtar ta rabu da shi.
14 And he commanded him that hee should tell it no man: but Go, sayth he, and shew thy selfe to the Priest, and offer for thy clensing, as Moses hath commanded, for a witnes vnto them.
Sai Yesu ya umarce shi ya ce, “Kada ka gaya wa kowa, amma ka tafi ka nuna kanka ga firist, ka kuma miƙa hadayu da Musa ya umarta, saboda tsarkakewarka ta zama shaida a gare su.”
15 But so much more went there a fame abroad of him, and great multitudes came together to heare, and to be healed of him of their infirmities.
Duk da haka, labarinsa ya ƙara bazuwa sosai, har taron mutane suka dinga zuwa don jinsa, da kuma neman warkarwa daga cututtukansu.
16 But he kept himselfe apart in the wildernes, and prayed.
Amma Yesu sau da yawa, yakan keɓe kansa zuwa wuraren da ba kowa, yă yi addu’a.
17 And it came to passe, on a certaine day, as he was teaching, that the Pharises and doctours of the Law sate by, which were come out of euery towne of Galile, and Iudea, and Hierusalem, and the power of the Lord was in him to heale them.
Wata rana, da yake cikin koyarwa, waɗansu Farisiyawa da malaman dokoki waɗanda suka zo daga kowane ƙauye a Galili, Yahudiya da Urushalima kuwa suna zaune. Ikon Ubangiji yana nan don yă warkar da masu ciwo.
18 Then beholde, men brought a man lying in a bed, which was taken with a palsie, and they sought meanes to bring him in, and to lay him before him.
Sai ga waɗansu mutane suka kawo wani shanyayye a kan tabarma. Suka yi ƙoƙari su shigar da shi cikin gidan, domin su kwantar da shi a gaban Yesu.
19 And when they could not finde by what way they might bring him in, because of the preasse, they went vp on the house, and let him downe through the tyling, bed and all, in the middes before Iesus.
Da suka ga babu hanyar da za su bi saboda taron, sai suka haura rufin, suka saukar da shi a kan tabarmarsa, ta bakin ramin da suka huda a rufin, suka ajiye shi a tsakiyar taron, a gaban Yesu.
20 And when he sawe their faith, he sayd vnto him, Man, thy sinnes are forgiuen thee.
Da Yesu ya ga bangaskiyarsu, sai ya ce, “Saurayi, an gafarta maka zunubanka.”
21 Then the Scribes and the Pharises began to reason, saying, Who is this that speaketh blasphemies? who can forgiue sinnes, but God onely?
Farisiyawa da malaman dokoki suka fara yin tunani a zukatansu, “Wane ne wannan mutum da yake saɓo haka? Wa zai iya gafarta zunubai, in ba Allah kaɗai ba?”
22 But when Iesus perceiued their reasoning, he answered, and sayd vnto them, What reason ye in your hearts?
Yesu ya san abin da suke tunani, sai ya yi tambaya ya ce, “Don me kuke tunanin waɗannan abubuwa a zukatanku?
23 Whether is easier to say, Thy sinnes are forgiuen thee, or to say, Rise and walke?
Wanne ya fi sauƙi, a ce, ‘An gafarta maka zunubanka,’ ko kuma a ce, ‘Tashi, ka yi tafiya’?
24 But that ye may know that that Sonne of man hath authoritie to forgiue sinnes in earth, (he sayd vnto the sicke of the palsie) I say to thee, Arise: take vp thy bed, and goe to thine house.
Amma domin ku san cewa Ɗan Mutum yana da iko a duniya ya gafarta zunubai.” Sai ya ce wa shanyayyen, “Na ce maka, tashi, ɗauki tabarmarka ka tafi gida.”
25 And immediatly he rose vp before them, and tooke vp his bed whereon he lay, and departed to his owne house, praysing God.
Nan da nan, ya tashi tsaye a gabansu, ya ɗauki tabarmar da yake kwance a kai, ya tafi gida, yana yabon Allah.
26 And they were all amased, and praysed God, and were filled with feare, saying, Doutlesse we haue seene strange things to day.
Kowa ya yi mamaki, ya kuma yabi Allah. Suka cika da tsoro, suna cewa, “Mun ga abubuwan banmamaki yau.”
27 And after that, he went foorth and sawe a Publicane named Leui, sitting at the receite of custome, and sayd vnto him, Follow me.
Bayan wannan, sai Yesu ya fita, ya ga wani mai karɓar haraji, mai suna Lawi, yana zaune a wurin da ake karɓar haraji. Yesu ya ce masa, “Bi ni.”
28 And he left all, rose vp, and folowed him.
Sai Lawi ya tashi, ya bar kome da kome, ya bi shi.
29 Then Leui made him a great feast in his owne house, where there was a great company of Publicanes, and of other that sate at table with them.
Sai Lawi ya shirya wa Yesu wani babban liyafa a gidansa. Wani babban taron na masu karɓar haraji, tare da waɗansu suna cin abinci tare da su.
30 But they that were Scribes and Pharises among them, murmured against his disciples, saying, Why eate ye and drinke ye with Publicanes and sinners?
Amma Farisiyawa da malaman dokokin da suke a ƙungiyarsu, suka yi wa almajiransa gunaguni, suna cewa, “Don me kuke ci, kuke sha tare da masu karɓar haraji da masu zunubi?”
31 Then Iesus answered, and sayd vnto them, They that are whole, neede not the Physician, but they that are sicke.
Yesu ya amsa musu ya ce, “Ai, masu lafiya ba sa bukatar likita, sai dai marasa lafiya.
32 I came not to call the righteous, but sinners to repentance.
Ban zo don in kira masu adalci ba, sai dai masu zunubi zuwa ga tuba.”
33 Then they said vnto him, Why do the disciples of Iohn fast often, and pray, and the disciples of the Pharises also, but thine eate and drinke?
Suka ce masa, “Almajiran Yohanna sukan yi azumi da addu’a, haka ma almajiran Farisiyawa, amma naka sai ci da sha.”
34 And he said vnto them, Can ye make the children of the wedding chamber to fast, as long as the bridegrome is with them?
Yesu ya amsa ya ce, “Za ku iya sa abokan ango yin azumi yayinda yake tare da su?
35 But the dayes will come, euen when the bridegrome shalbe taken away from them: then shall they fast in those dayes.
Amma lokaci yana zuwa, da za a ɗauke ango daga gare su. A waɗancan kwanakin ne za su yi azumi.”
36 Againe he spake also vnto them a parable, No man putteth a piece of a newe garment into an olde vesture: for then the newe renteth it, and the piece taken out of the newe, agreeth not with the olde.
Sai ya faɗa musu wannan misali ya ce, “Ba wanda yakan yage ƙyalle daga sabuwar riga ya yi wa tsohuwar riga faci. In ya yi haka, zai yage sabuwar rigar, kuma facin daga sabuwar ba zai dace da tsohuwar rigar ba.
37 Also no man powreth newe wine into olde vessels: for then ye new wine wil breake the vessels, and it will runne out, and the vessels will perish:
Kuma ba wanda yakan zuba sabon ruwan inabi a cikin tsofaffin salkuna. In ya yi haka, sabon ruwan inabi zai farfashe salkunan, ruwan inabin yă zube, salkunan kuma su lalace.
38 But newe wine must be powred into newe vessels: so both are preserued.
A’a, sai dai a zuba sabon ruwan inabi a sababbin salkuna.
39 Also no man that drinketh olde wine, straightway desireth newe: for he sayth, The olde is more profitable.
Kuma ba wanda yakan so shan sabon ruwan inabi bayan ya sha tsohon, don yakan ce, ‘Ai, tsohon ya fi kyau.’”

< Luke 5 >