< Luke 4 >

1 And Iesus full of the holy Ghost returned from Iordan, and was led by that Spirit into the wildernes,
Sai Yesu, cike da Ruhu Mai Tsarki, ya dawo daga kogin Urdun, sai Ruhu Mai Tsarki ya bishe shi zuwa cikin jeji
2 And was there fourtie dayes tempted of the deuil, and in those dayes he did eate nothing: but when they were ended, he afterward was hungry.
kwana arba'in, shaidan kuma ya jarabce shi. A kwanakin nan, bai ci abinci ba, kuma yunwa ta kama shi bayan karshen lokacin.
3 Then the deuil saide vnto him, If thou be the Sonne of God, commaund this stone that it be made bread.
Shaidan ya ce masa, “Idan kai Dan Allah ne, ka umarci wannan dutse ya zama gurasa.”
4 But Iesus answered him, saying, It is written, That man shall not liue by bread only, but by euery word of God.
Yesu ya amsa masa, “A rubuce yake, 'Ba da gurasa kadai Mutum zai rayu ba.'”
5 Then the deuill tooke him vp into an high mountaine, and shewed him all the kingdomes of the world, in the twinkeling of an eye.
Sai shaidan ya kai shi zuwa wani tudu mai tsawo, ya kuma nuna masa dukan mulkokin duniyan nan a dan lokaci.
6 And the deuill saide vnto him, All this power will I giue thee, and the glory of those kingdomes: for that is deliuered to mee: and to whomsoeuer I will, I giue it.
Shaidan ya ce masa, “Zan ba ka iko ka yi mulkin dukan wadannan, da dukan daukakarsu. Zan yi haka domin an ba ni su duka in yi mulkinsu, kuma ina da yanci in ba dukan wanda na ga dama.
7 If thou therefore wilt worship mee, they shalbe all thine.
Saboda da haka, idan ka rusuna ka yi mani sujada, dukansu za su zama naka.”
8 But Iesus answered him, and saide, Hence from mee, Satan: for it is written, Thou shalt worship the Lord thy God, and him alone thou shalt serue.
Amma Yesu ya amsa ya ce masa, “A rubuce yake, 'Dole ne Ubangiji Allahnka za ka yi wa sujada, shi kadai kuma za ka bauta wa.”
9 Then hee brought him to Hierusalem, and set him on a pinacle of the Temple, and said vnto him, If thou be the Sonne of God, cast thy selfe downe from hence,
Sai shaidan ya kai Yesu Urushalima, ya tsayadda shi a bisan kololuwar haikali, kuma ya ce masa, “Idan kai Dan Allah ne, ka jefas da kanka kasa daga nan.
10 For it is written, That hee will giue his Angels charge ouer thee to keepe thee:
Domin a rubuce yake, 'Zai ba mala'ikunsa umarni su kiyaye ka, su kuma tsare ka,'
11 And with their handes they shall lift thee vp, least at any time thou shouldest dash thy foote against a stone.
kuma, 'Za su daga ka sama a hannunsu, don kada ka yi tuntube a kan dutse.”
12 And Iesus answered, and said vnto him, It is said, Thou shalt not tempt the Lord thy God.
Yesu ya amsa masa cewa, “An fadi, 'Kada ka gwada Ubangiji Allahnka.'”
13 And when the deuil had ended all the tentation, he departed from him for a litle season.
Da shaidan ya gama yi wa Yesu gwaji, sai ya kyale shi sai wani lokaci.
14 And Iesus returned by the power of the spirite into Galile: and there went a fame of him throughout all the region round about.
Sai Yesu ya koma Galili cike da ikon Ruhu, kuma labarinsa ya bazu cikin dukan wuraren dake wannan yankin.
15 For he taught in their Synagogues, and was honoured of all men.
Ya yi ta koyarwa a cikin majami'unsu, sai kowa na ta yabon sa.
16 And hee came to Nazareth where hee had bene brought vp, and (as his custome was) went into the Synagogue on the Sabbath day, and stoode vp to reade.
Wata rana ya zo Nazarat, birnin da aka rene shi. Kamar yadda ya saba yi, ya shiga cikin majami'a a nan ranar Asabaci, ya kuma tashi tsaye domin ya karanta Nassi.
17 And there was deliuered vnto him the booke of the Prophet Esaias: and when hee had opened the booke, hee founde the place, where it was written,
An mika masa littafin anabi Ishaya, ya bude littafin ya kuma ga inda an rubuta,
18 The Spirit of the Lord is vpon mee, because he hath anoynted me, that I should preach the Gospel to the poore: he hath sent mee, that I should heale the broken hearted, that I should preach deliuerance to the captiues, and recouering of sight to the blinde, that I should set at libertie them that are bruised:
“Ruhun Ubangiji yana kai na, domin ya shafe ni in yi wa'azin Bishara ga matalauta. Ya aike ni in yi shelar yanci ga daurarru, da kuma budewar idanu ga makafi, in 'yantar da wadanda su ke cikin kunci,
19 And that I should preache the acceptable yeere of the Lord.
in kuma yi shelar shekarar tagomashi na Ubangiji.”
20 And hee closed the booke, and gaue it againe to the minister, and sate downe: and the eyes of all that were in the Synagogue were fastened on him.
Sai ya rufe littafin, ya mai da shi ga ma'aikacin majami'ar, sai ya zauna. Dukan wadanda suke cikin majami'ar suka zura Idanuwansu a kansa.
21 Then he began to say vnto them, This day is the Scripture fulfilled in your eares.
Sai ya fara masu magana, “Yau wannan Nassi ya cika a kunuwanku.”
22 And all bare him witnes, and wondered at the gracious wordes, which proceeded out of his mouth, and said, Is not this Iosephs sonne?
Dukan wadanda ke wurin sun shaida abin da ya fadi kuma dukansu sun yi ta mamakin kalmomin alheri da suke fitowa daga bakinsa. Suna cewa, “Wannan ai dan Yusufu ne kawai, ko ba haka ba?”
23 Then he said vnto them, Ye will surely say vnto mee this prouerbe, Physician, heale thy selfe: whatsoeuer we haue heard done in Capernaum, doe it here likewise in thine owne countrey.
Yesu ya ce masu, “Lallai za ku fada mani wannan karin magana, 'Likita, ka warkar da kanka. Duk abin da mun ji wai ka yi a Kafarnahum, ka yi shi a nan garinka ma.'”
24 And he saide, Verely I say vnto you, No Prophet is accepted in his owne countrey.
Ya sake cewa, “Hakika na fada maku, annabi baya samun karbuwa a garinsa.
25 But I tell you of a trueth, many widowes were in Israel in the dayes of Elias, when heauen was shut three yeres and sixe moneths, when great famine was throughout all the land:
Amma na gaya maku gaskiya akwai gwauraye da yawa cikin Isra'ila a zamanin Iliya, lokacin da an rufe sammai shekaru uku da rabi babu ruwa, lokacin da anyi gagarumar yunwa a duk fadin kasar.
26 But vnto none of them was Elias sent, saue into Sarepta, a citie of Sidon, vnto a certaine widowe.
Amma ba a aiki Iliya zuwa wurin waninsu ba, sai wurin gwauruwa da ke a Zarifat can kusa da Sidon.
27 Also many lepers were in Israel, in the time of Eliseus the Prophet: yet none of them was made cleane, sauing Naaman the Syrian.
Akwai kutare da yawa kuma a Isa'ila a zamanin anabi Elisha, amma babu wanda aka warkar sai dai Na'aman mutumin Suriya kadai.
28 Then all that were in the Synagogue, when they heard it, were filled with wrath,
Dukan mutanen da ke cikin majami'a suka fusata kwarai sa'adda suka ji wadannan zantattuka.
29 And rose vp, and thrust him out of the citie, and led him vnto the edge of the hil, whereon their citie was built, to cast him downe headlong.
Suka tashi suka tura shi zuwa wajen birnin, suka kai shi bakin dutsen da aka gina garinsu a kai dominsu jefar da shi kasa.
30 But he passed through the middes of them, and went his way,
Amma ya ratsa tsakaninsu ya yi gabansa.
31 And came downe into Capernaum a citie of Galile, and there taught them on the Sabbath dayes.
Sannan ya gangara zuwa Kafarnahum, wani birni a Galili. Wata Asabaci yana koya wa mutane a cikin majami'a.
32 And they were astonied at his doctrine: for his worde was with authoritie.
Sun yi mamaki kwarai da koyarwan sa, domin maganarsa na da iko.
33 And in the Synagogue there was a man which had a spirit of an vncleane deuill, which cryed with a loude voyce,
A wannan lokacin akwai wani mutum a cikin majami'a mai kazamin ruhu, sai ya yi kara da babbar murya,
34 Saying, Oh, what haue we to doe with thee, thou Iesus of Nazareth? art thou come to destroy vs? I know who thou art, euen the holy one of God.
“Ina ruwan mu da kai, Yesu Banazarat? Ka zo domin ka hallaka mu ne? Na san ko kai wanene! Kai ne Mai Tsarki na Allah!”
35 And Iesus rebuked him, saying, Holde thy peace, and come out of him. Then the deuill throwing him in the middes of them, came out of him, and hurt him nothing at all.
Yesu ya tsauta wa aljanin yana cewa, “Yi shiru ka fita daga cikinsa!” Da aljanin ya jefar da mutumin kasa a tsakiyarsu, ya fita daga cikinsa ba tare da yi masa rauni ba.
36 So feare came on them all, and they spake among themselues, saying, What thing is this: for with authoritie and power he commaundeth the foule spirits, and they come out?
Dukan mutanen suka yi mamaki, kuma suna ta zancen wannan abu a tsakaninsu. Sun ce, “Wanda irin maganganu kenan? Ya umarce kazaman ruhohin da karfi da iko kuma sun fita.”
37 And ye fame of him spred abroad throughout all the places of the countrey round about.
Saboda da haka, an fara yada labarinsa zuwa dukan kewayen yankin.
38 And he rose vp, and came out of the Synagogue, and entred into Simons house. And Simons wiues mother was taken with a great feuer, and they required him for her.
Sai Yesu ya bar majami'ar ya shiga gidan Siman. A wannan lokacin, surukar Siman tana fama da zazzabi mai zafi, sai suka roke shi dominta.
39 Then he stoode ouer her, and rebuked the feuer, and it left her, and immediatly she arose, and ministred vnto them.
Sai ya tsaya a kanta, ya tsautawa zazzabin, kuma ya rabu da ita. Nan take, ta tashi ta fara yi masu hidima.
40 Now at the sunne setting, all they that had sicke folkes of diuers diseases, brought them vnto him, and he layd his hands on euery one of them, and healed them.
Da faduwar rana, mutane suka kawo wa Yesu dukan wadanda suke ciwo da cuttuttuka dabam dabam. Ya dora masu hannuwansa ya warkar da su.
41 And deuils also came out of many, crying, and saying, Thou art that Christ that Sonne of God: but he rebuked them, and suffered them not to say that they knewe him to be that Christ.
Aljanu kuma sun fita daga wadasunsu da dama, suna kuka cewa, “Kai ne Dan Allah!” Yesu ya tsauta wa aljannun ya kuma hana su magana, domin sun sani cewa shine Almasihu.
42 And when it was day, he departed, and went foorth into a desart place, and the people sought him, and came to him, and kept him that he should not depart from them.
Da safiya ta yi, ya kebe kansa zuwa wani wurin da babu kowa. Jama'a da dama suna neman sa suka zo inda yake. Sun yi kokari su hana shi barin su.
43 But he sayd vnto them, Surely I must also preach the kingdome of God to other cities: for therefore am I sent.
Amma ya ce masu, “Dole in yi bisharar Allah a wasu birane da dama, domin dalilin da aka aiko ni nan kenan.”
44 And hee preached in the Synagogues of Galile.
Sai ya ci gaba da wa'azi cikin majami'u dukan fadin Yahudiya.

< Luke 4 >