< Luke 16 >

1 And he sayde also vnto his disciples, There was a certaine riche man, which had a stewarde, and he was accused vnto him, that he wasted his goods.
Yesu ya ce wa almajiransa, “An yi wani mai arziki wanda aka yi wa manajansa zargin yin banza da dukiyarsa.
2 And hee called him, and saide vnto him, Howe is it that I heare this of thee? Giue an accounts of thy stewardship: for thou maiest be no longer steward.
Sai ya kira manajan, ya tambaye shi, ‘Me nake ji haka a kanka? Ka kawo lissafin aikinka, domin ba za ka iya cin gaba da aikinka ba.’
3 Then the stewarde saide within himselfe, What shall I doe? for my master taketh away from me the stewardship. I cannot digge, and to begge I am ashamed.
“Sai manajan ya ce cikin tunaninsa, ‘Maigidana zai kore ni daga aiki, me zan yi? Ba ni da ƙarfin noma, kuma ina jin kunyan yin bara.
4 I knowe what I will doe, that when I am put out of the stewardship, they may receiue mee into their houses.
Na san abin da zan yi, don mutane su karɓe ni a gidajensu, bayan an kore ni daga aiki a nan.’
5 Then called he vnto him euery one of his masters detters, and said vnto the first, Howe much owest thou vnto my master?
“Sai ya kira kowane ɗaya da maigidansa yake bin bashi. Ya tambayi na farkon ya ce, ‘Nawa ne maigidana yake bin ka?’
6 And he said, An hudreth measures of oyle. And he saide to him, Take thy writing, and sitte downe quickely, and write fiftie.
“Ya amsa ya ce, ‘Garwar mai na zaitun guda ɗari tara.’ “Manajan ya ce, ‘Ga takardarka, ka zauna maza ka mai da shi ɗari huɗu.’
7 Then said he to another, How much owest thou? And hee sayde, An hundreth measures of wheate. Then he saide to him, Take thy writing, and write foure score.
“Ya kuma tambayi na biyun, ‘Kai fa, nawa ne ake bin ka?’ “Sai ya amsa ya ce, ‘Buhunan alkama dubu.’ “Ya ce, ‘Ga takardarka, ka mai da shi ɗari takwas.’
8 And the Lord commended the vniust stewarde, because he had done wisely. Wherefore the children of this worlde are in their generation wiser then the children of light. (aiōn g165)
“Maigidan kuwa ya yabi manajan nan marar gaskiya saboda wayonsa. Gama’yan duniyan nan suna da wayon yin hulɗa da junansu fiye da’yan haske. (aiōn g165)
9 And I say vnto you, Make you friends with the riches of iniquitie, that when ye shall want, they may receiue you into euerlasting habitations. (aiōnios g166)
Ina gaya muku, ku yi amfani da dukiya na wannan duniya, domin ku sami wa kanku abokai. Saboda bayan dukiyar ta ƙare, za a karɓe ku a wuraren zama da sun dawwama. (aiōnios g166)
10 He that is faithfull in the least, hee is also faithful in much: and he that is vniust in the least, is vniust also in much.
“Duk wanda ana amincewa da shi cikin ƙaramin abu, ana kuma amincewa da shi cikin babba. Kuma duk marar gaskiya cikin ƙaramin abu, zai zama marar gaskiya cikin babba.
11 If then ye haue not ben faithful in the wicked riches, who wil trust you in the true treasure?
In fa ku ba amintattu ne cikin tafiyar da dukiya ta wannan duniya ba, wa zai amince muku da dukiya ta gaskiya?
12 And if ye haue not bene faithfull in another mans goods, who shall giue you that which is yours?
In fa ku ba amintattu ne cikin tafiyar da dukiyar wani ba, wa zai ba ku dukiya naku, na kanku?
13 No seruaunt can serue two masters: for either he shall hate the one, and loue the other: or els he shall leane to the one, and despise the other. Yee can not serue God and riches.
“Babu wani bawa mai iya bauta wa iyayengiji biyu ba. Ko dai ya ƙi ɗaya, ya so ɗayan, ko kuwa ya dāge ga yi wa ɗaya bauta, sa’an nan ya rena ɗayan. Ba za ku iya ku bauta wa Allah tare da bauta wa Mammon (wato, Kuɗi) a lokaci ɗaya ba.”
14 All these thinges heard the Pharises also which were couetous, and they scoffed at him.
Da Farisiyawa masu son kuɗi suka ji wannan duka, sai suka yi wa Yesu tsaki.
15 Then he sayde vnto them, Yee are they, which iustifie your selues before men: but God knoweth your heartes: for that which is highly esteemed among men, is abomination in the sight of God.
Ya ce musu, “Ku ne masu mai da kanku marasa laifi a gaban mutane, amma Allah ya san zuciyarku. Abu mai daraja a gaban mutane, abin ƙyama ne a gaban Allah.
16 The Lawe and the Prophets endured vntill Iohn: and since that time the kingdome of God is preached, and euery man preasseth into it.
“An yi shelar Doka da Annabawa har zuwa lokacin Yohanna. Tun daga lokacin nan, bisharar mulkin Allah ne ake wa’azinta, kowa kuma yana ƙoƙarin kutsa kai ya shiga.
17 Nowe it is more easie that heauen and earth shoulde passe away, then that one title of the Lawe should fall.
Gama ta fi sauƙi sama da ƙasa su shuɗe, da a ce ɗigo guda ɗaya na rubutun, ya fita ya fāɗi daga cikin Doka.
18 Whosoeuer putteth away his wife, and marieth another, committeth adulterie: and whosoeuer marieth her that is put away from her husband, committeth adulterie.
“Duk wanda ya saki matarsa ya auri wata mace, zina ne yake yi. Kuma mutumin da ya auri macen da aka sake, zina ne yake yi.
19 There was a certaine riche man, which was clothed in purple and fine linnen, and fared well and delicately euery day.
“An yi wani mutum mai arziki wanda yakan sa tufafi masu ruwan shunayya, da kuma na lallausan lilin, yana kuma cikin rayuwar jin daɗi kullum.
20 Also there was a certaine begger named Lazarus, which was laide at his gate full of sores,
A ƙofar gidansa kuma akan ajiye wani mai bara, mai suna Lazarus, wanda jikinsa duk gyambuna ne.
21 And desired to bee refreshed with the crommes that fell from the riche mans table: yea, and the dogges came and licked his sores.
Shi kuwa yakan yi marmarin cin abin da yakan fāɗi daga tebur na mai arzikin nan. Har karnuka ma sukan zo su lashe gyambunansa.
22 And it was so that the begger died, and was caried by the Angels into Abrahams bosome. The rich man also died, and was buried.
“Ana nan, sai mai baran ya mutu, kuma mala’iku suka ɗauke shi zuwa gefen Ibrahim. Mai arzikin ma ya mutu, aka kuma binne shi.
23 And being in hell in torments, he lift vp his eyes, and sawe Abraham a farre off, and Lazarus in his bosome. (Hadēs g86)
A cikin jahannama ta wuta, inda yana shan azaba, ya ɗaga kai ya hangi Ibrahim can nesa, da kuma Lazarus a gefensa. (Hadēs g86)
24 Then he cried, and saide, Father Abraham, haue mercie on mee, and sende Lazarus that hee may dippe the tip of his finger in water, and coole my tongue: for I am tormented in this flame.
Sai ya yi masa kira ya ce, ‘Baba, Ibrahim, ka ji tausayina, ka aiki Lazarus ya sa ɗan yatsarsa a ruwa, ya ɗiga mini a harshe saboda in ji sanyi, domin ina shan azaba cikin wannan wuta.’
25 But Abraham saide, Sonne, remember that thou in thy life time receiuedst thy pleasures, and likewise Lazarus paines: now therefore is he comforted, and thou art tormented.
“Amma Ibrahim ya ce, ‘Ka tuna fa ɗana, a lokacin da kake duniya, ka sami abubuwa masu kyau naka, Lazarus kuwa ya sami munanan abubuwa. Amma yanzu ya sami ta’aziyya a nan, kai kuwa kana shan azaba.
26 Besides all this, betweene you and vs there is a great gulfe set, so that they which would goe from hence to you, can not: neither can they come from thence to vs.
Ban da wannan duka ma, tsakaninmu da kai, akwai wani babban rami da aka yi, yadda waɗanda suke son ƙetarewa daga nan zuwa wurinku, ba za su iya ba, kuma ba mai iya ƙetarewa daga wurinku zuwa wurinmu.’
27 Then he said, I pray thee therfore, father, that thou wouldest sende him to my fathers house,
“Ya amsa ya ce, ‘To, ina roƙonka, ya uba, ka aiki Lazarus zuwa gidan mahaifina,
28 (For I haue fiue brethren) that he may testifie vnto them, least they also come into this place of torment.
gama ina da’yan’uwana biyar maza. Bari yă ba su gargaɗi, don kada su ma su zo wurin nan mai azaba.’
29 Abraham said vnto him, They haue Moses and the Prophets: let them heare them.
“Ibrahim ya amsa ya ce, ‘Suna da Musa da Annabawa, ai, sai su saurare su.’
30 And he sayde, Nay, father Abraham: but if one came vnto them from the dead, they will amend their liues.
“Sai ya ce, ‘A’a, ya uba, Ibrahim, in dai wani ya tashi daga matattu ya je wurinsu, za su tuba.’
31 Then he saide vnto him, If they heare not Moses and the Prophets, neither will they be persuaded, though one rise from the dead againe.
“Amma ya ce masa, ‘In ba su saurari Musa da Annabawa ba, kai, ko da wani ya tashi daga matattu ma, ba za su saurare shi ba.’”

< Luke 16 >