< Luke 1 >

1 Forasmuch as many haue taken in hand to set foorth the storie of those things, whereof we are fully persuaded,
Mutane da yawa sun ɗau niyyar rubuta labarin abubuwan da aka cika a cikinmu,
2 As they haue deliuered them vnto vs, which from the beginning saw them their selues, and were ministers of ye word,
kamar yadda muka karɓe su daga waɗanda tun farko shaidu ne da kuma masu hidimar bishara.
3 It seemed good also to me (most noble Theophilus) assoone as I had searched out perfectly all things from the beginning, to write vnto thee thereof from point to point,
Saboda haka, da yake ni da kaina na binciko kome a hankali daga farko, na ga ya yi kyau in rubuta maka labarin dalla-dalla, ya mafifici Tiyofilus,
4 That thou mightest acknowledge the certaintie of those things, whereof thou hast bene instructed.
don ka san tabbacin abubuwan da aka koyar da kai.
5 In the time of Herod King of Iudea, there was a certaine Priest named Zacharias, of the course of Abia: and his wife was of the daughters of Aaron, and her name was Elisabet.
A lokacin da Hiridus ne yake sarautar Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na sashin firistoci gidan Abiya. Matarsa Elizabet ma’yar zuriyar Haruna ce.
6 Both were iust before God, and walked in all the commandements and ordinances of the Lord, without reproofe.
Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna kuma bin umarnan Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi.
7 And they had no childe, because that Elisabet was barren: and both were well stricken in age.
Sai dai ba su da’ya’ya, domin Elizabet bakararriya ce; kuma dukansu biyu sun tsufa.
8 And it came to passe, as he executed the Priestes office before God, as his course came in order,
Wata rana da lokacin aikin firistoci na sashen Zakariya na yin hidima ya kewayo, yana kuma cikin hidimarsa ta firist a gaban Allah,
9 According to the custome of the Priests office, his lot was to burne incense, when he went into the Temple of the Lord.
sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare.
10 And the whole multitude of the people were without in prayer, while the incense was burning.
Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.
11 Then appeared vnto him an Angel of the Lord standing at the right side of the altar of incense.
Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare.
12 And when Zacharias sawe him, he was troubled, and feare fell vpon him.
Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi.
13 But the Angel saide vnto him, Feare not, Zacharias: for thy prayer is heard, and thy wise Elisabet shall beare thee a sonne, and thou shalt call his name Iohn.
Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna.
14 And thou shalt haue ioy and gladnes, and many shall reioyce at his birth.
Zai zama abin murna da farin ciki a gare ka, mutane da yawa kuwa za su yi murna don haihuwarsa,
15 For he shalbe great in the sight of the Lord, and shall neither drinke wine, nor strong drinke: and he shalbe filled with the holy Ghost, euen from his mothers wombe.
gama zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba kuwa zai taɓa shan ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun haihuwa.
16 And many of the children of Israel shall he turne to their Lord God.
Shi ne zai juye mutanen Isra’ila da yawa zuwa wurin Ubangiji Allahnsu.
17 For he shall goe before him in the spirite and power of Elias, to turne the hearts of the fathers to the children, and the disobedient to the wisedome of the iust men, to make ready a people prepared for the Lord.
Zai sha gaban Ubangiji, a ruhu da kuma iko irin na Iliya, domin yă juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, marasa biyayya kuma ga zama masu biyayya don yă kintsa mutane su zama shiryayyu domin Ubangiji.”
18 Then Zacharias said vnto ye Angel, Whereby shall I knowe this? for I am an olde man, and my wife is of a great age.
Sai Zakariya ya tambayi mala’ikan ya ce, “Yaya zan tabbatar da wannan? Ga ni tsoho, matana kuma ta kwana biyu.”
19 And the Angell answered, and sayde vnto him, I am Gabriel that stand in the presence of God, and am sent to speake vnto thee, and to shew thee these good tidings.
Mala’ikan ya ce, “Ni ne Jibra’ilu. Ina tsaya a gaban Allah, an kuma aiko ni in yi maka magana, in kuma faɗa maka wannan labari mai daɗi.
20 And beholde, thou shalt be domme, and not be able to speake, vntill the day that these things be done, because thou beleeuedst not my words, which shalbe fulfilled in their season.
Yanzu za ka zama bebe, ba za ka ƙara iya magana ba sai ranar da wannan magana ta cika, saboda ba ka gaskata da kalmomina waɗanda za su zama gaskiya a daidai lokacinsu ba.”
21 Now the people waited for Zacharias, and marueiled that he taried so long in the Temple.
Ana cikin haka, mutane suna jiran Zakariya, suna kuma mamaki me ya sa ya daɗe haka a cikin haikali.
22 And when hee came out, hee coulde not speake vnto them: then they perceiued that hee had seene a vision in the Temple: For he made signes vnto them, and remained domme.
Da ya fito, bai iya yin musu magana ba. Sai suka gane, ya ga wahayi ne a haikali, domin ya dinga yin musu alamu, amma ya kāsa yin magana.
23 And it came to passe, when the daies of his office were fulfilled, that he departed to his owne house.
Da lokacin hidimarsa ya cika, sai ya koma gida.
24 And after those daies, his wife Elisabet conceiued, and hid her selfe fiue moneths, saying,
Bayan wannan, matarsa Elizabet ta yi ciki, ta kuma riƙa ɓuya har wata biyar.
25 Thus hath the Lord dealt with me, in the daies wherein he looked on me, to take from me my rebuke among men.
Sai ta ce, “Ubangiji ne ya yi mini wannan. A waɗannan kwanaki ya nuna tagomashinsa ya kuma kawar mini da kunya a cikin mutane.”
26 And in the sixth moneth, the Angell Gabriel was sent from God vnto a citie of Galile, named Nazareth,
A wata na shida, sai Allah ya aiki mala’ika Jibra’ilu zuwa Nazaret, wani gari a Galili,
27 To a virgin affianced to a man whose name was Ioseph, of the house of Dauid, and the virgins name was Marie.
gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu.
28 And the Angel went in vnto her, and said, Haile thou that art freely beloued: the Lord is with thee: blessed art thou among women.
Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”
29 And when she saw him, she was troubled at his saying, and thought what maner of salutation that should be.
Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka?
30 Then the Angel saide vnto her, Feare not, Marie: for thou hast found fauour with God.
Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.
31 For loe, thou shalt conceiue in thy wobe, and beare a sonne, and shalt call his name Iesus.
Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu.
32 He shall be great, and shall be called the Sonne of the most High, and the Lord God shall giue vnto him the throne of his father Dauid.
Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda,
33 And hee shall reigne ouer the house of Iacob for euer, and of his kingdome shall bee none ende. (aiōn g165)
zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.” (aiōn g165)
34 Then sayde Marie vnto the Angel, How shall this be, seeing I knowe not man?
Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”
35 And the Angel answered, and said vnto her, The holy Ghost shall come vpon thee, and the power of the most High shall ouershadowe thee: therefore also that holy thing which shall bee borne of thee, shall be called the Sonne of God.
Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.
36 And behold, thy cousin Elisabet, she hath also conceiued a sonne in her olde age: and this is her sixt moneth, which was called barren.
’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida.
37 For with God shall nothing be vnpossible.
Gama ba abin da zai gagari Allah.”
38 Then Marie said, Behold the seruant of the Lord: be it vnto me according to thy woorde. So the Angel departed from her.
Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.
39 And Marie arose in those daies, and went into ye hil countrey with hast to a citie of Iuda,
A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya,
40 And entred into the house of Zacharias, and saluted Elisabet.
inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet.
41 And it came to passe, as Elisabet heard the salutation of Marie, the babe sprang in her bellie, and Elisabet was filled with the holy Ghost.
Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki.
42 And she cried with a loud voice, and saide, Blessed art thou among women, because the fruit of thy wombe is blessed.
Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa!
43 And whence commeth this to mee, that the mother of my Lord should come to me?
Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina?
44 For loe, assoone as the voice of thy salutation sounded in mine eares, the babe sprang in my bellie for ioye,
Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna.
45 And blessed is shee that beleeued: for those things shall be perfourmed, which were tolde her from the Lord.
Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”
46 Then Marie sayde, My soule magnifieth the Lord,
Sai Maryamu ta ce, “Raina yana ɗaukaka Ubangiji
47 And my spirite reioyceth in God my Sauiour.
ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,
48 For hee hath looked on the poore degree of his seruaunt: for beholde, from henceforth shall all ages call me blessed,
gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa. Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,
49 Because hee that is mightie, hath done for me great things, and holy is his Name.
gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa, sunansa labudda Mai Tsarki ne.
50 And his mercie is from generation to generation on them that feare him.
Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa, daga zamani zuwa zamani.
51 Hee hath shewed strength with his arme: hee hath scattered the proude in the imagination of their hearts.
Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa; ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.
52 Hee hath put downe the mighty from their seates, and exalted them of lowe degree.
Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.
53 Hee hath filled the hungrie with good things, and sent away the rich emptie.
Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa amma ya sallami mawadata hannu wofi.
54 Hee hath vpholden Israel his seruaunt to be mindefull of his mercie
Ya taimaki bawansa Isra’ila, yana tunawa yă nuna jinƙai
55 (As hee hath spoken to our fathers, to wit, to Abraham, and his seede) for euer. (aiōn g165)
ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.” (aiōn g165)
56 And Marie abode with her about three moneths: after, shee returned to her owne house.
Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.
57 Nowe Elisabets time was fulfilled, that shee should be deliuered, and shee brought foorth a sonne.
Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa.
58 And her neighbours, and cousins heard tell howe the Lord had shewed his great mercie vpon her, and they reioyced with her.
Maƙwabtanta da’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.
59 And it was so that on the eight day they came to circumcise the babe, and called him Zacharias after the name of his father.
A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,
60 But his mother answered, and saide, Not so, but he shalbe called Iohn.
amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”
61 And they saide vnto her, There is none of thy kindred, that is named with this name.
Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”
62 Then they made signes to his father, howe he would haue him called.
Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.
63 So hee asked for writing tables, and wrote, saying, His name is Iohn, and they marueiled all.
Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
64 And his mouth was opened immediately, and his tongue, and he spake and praised God.
Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.
65 Then feare came on all them that dwelt neere vnto them, and all these woordes were noised abroade throughout all the hill countrey of Iudea.
Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.
66 And al they that heard them, laid them vp in their hearts, saying, What maner childe shall this be! and the hand of the Lord was with him.
Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.
67 Then his father Zacharias was filled with the holy Ghost, and prophesied, saying,
Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,
68 Blessed be the Lord God of Israel, because he hath visited and redeemed his people,
“Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.
69 And hath raised vp the horne of saluation vnto vs, in the house of his seruant Dauid,
Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda
70 As he spake by ye mouth of his holy Prophets, which were since the world began, saying, (aiōn g165)
(yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki), (aiōn g165)
71 That he would sende vs deliuerance from our enemies, and from the hands of all that hate vs,
cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu
72 That he might shewe mercie towards our fathers, and remember his holy couenant,
don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
73 And the othe which he sware to our father Abraham.
rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,
74 Which was, that he would graunt vnto vs, that we being deliuered out of the handes of our enemies, should serue him without feare,
don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,
75 All the daies of our life, in holinesse and righteousnesse before him.
cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.
76 And thou, babe, shalt be called the Prophet of the most High: for thou shalt goe before the face of the Lord, to prepare his waies,
“Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki; gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,
77 And to giue knowledge of saluation vnto his people, by the remission of their sinnes,
don ka sanar da mutanensa ceto, ta wurin gafarar zunubansu,
78 Through ye tender mercy of our God, wherby the day spring from an hie hath visited vs,
saboda jinƙai na Allahnmu mai ƙauna, hasken nan na ceto zai ɓullo mana daga sama,
79 To giue light to them that sit in darknes, and in the shadow of death, and to guide our feete into the way of peace.
don yă haskaka a kan waɗanda suke zama cikin duhu, da kuma cikin inuwar mutuwa, don yă bi da ƙafafunmu a hanyar salama.”
80 And the childe grewe, and waxed strong in spirit, and was in the wildernesse, til the day came that he should shewe him selfe vnto Israel.
Yaron kuwa ya yi girma ya kuma ƙarfafa a ruhu; ya zauna a hamada sai lokacin da ya fito a fili ga mutanen Isra’ila.

< Luke 1 >