< Lamentations 2 >

1 How hath the Lord darkened the daughter of Zion in his wrath! and hath cast downe from heauen vnto the earth the beautie of Israel, and remembred not his footestoole in the day of his wrath!
Yadda Ubangiji ya rufe Diyar Sihiyona da gizagizan fushi! Ya jefar da darajar Isra’ila daga sama zuwa ƙasa; bai tuna da wurin ɗora ƙafafunsa ba a ranar fushinsa.
2 The Lord hath destroyed al the habitations of Iaakob, and not spared: he hath throwen downe in his wrath ye strong holds of the daughter of Iudah: he hath cast the downe to ye ground: he hath polluted the kingdome and the princes thereof.
Ubangiji ya hallakar da wurin zaman Yaƙub ba tausayi; A cikin fushinsa kuma zai rurrushe kagaran Diyar Yahuda. Ya ƙasƙantar da mulki da masu mulki.
3 Hee hath cut off in his fierce wrath all the horne of Israel: he hath drawen backe his right hand from before the enemie, and there was kindled in Iaakob like a flame of fire, which deuoured rounde about.
A cikin zafin fushi ya fasa kowane ƙaho na Isra’ila. Ya janye hannun damansa sa’ad da maƙiyi ya zo. Ya yi ƙuna a cikin Yaƙub kamar wuta mai ƙone duk abin da yake kusa da ita.
4 He hath bent his bowe like an enemie: his right hand was stretched vp as an aduersarie, and slewe al that was pleasant to the eye in the tabernacle of the daughter of Zion: he powred out his wrath like fire.
Kamar abokin gāba, ya ɗana bakansa; hannun damansa na shirye. Kamar maƙiyi, ya kashe duk wanda idonsa ya ji daɗin gani; ya zuba fushinsa kamar wuta a kan tenti na Diyar Sihiyona.
5 The Lord was as an enemie: he hath deuoured Israel, and consumed all his palaces: hee hath destroyed his strong holdes, and hath increased in the daughter of Iudah lamentation and mourning.
Ubangiji kamar maƙiyi ne; ya hallaka Isra’ila. Ya hallaka wurarenta duka ya kuma hallaka kagaranta. Ya ƙara yawan makoki da baƙin ciki wa Diyar Yahuda.
6 For hee hath destroyed his Tabernacle, as a garden, hee hath destroyed his Congregation: the Lord hath caused the feastes and Sabbathes to bee forgotten in Zion, and hath despised in the indignation of his wrath the King and the Priest.
Ya rushe haikalinsa kamar lambu; ya hallaka wurin yi masa sujada. Ubangiji ya sa Sihiyona ta manta da bukukkuwanta da kuma ranakunta na Asabbaci; a cikin zafin fushinsa ya watsar da sarki da firist.
7 The Lord hath forsaken his altar: he hath abhorred his Sanctuarie: he hath giue into the hand of the enemie the walles of her palaces: they haue made a noyse in the House of the Lord, as in the day of solemnitie.
Ubangiji ya ƙi bagadensa ya kuma yi wofi da haikalinsa. Ya ba maƙiyinta fadodinta; suka yi sowa a cikin gidan Ubangiji kamar a ranar da ake yin biki.
8 The Lord hath determined to destroy the wall of the daughter of Zion: hee stretched out a lyne: hee hath not withdrawen his hande from destroying: therefore hee made the rampart and the wall to lament: they were destroyed together.
Ubangiji ya ƙuduri niyya yă rushe bangon da yake kewaye da Diyar Sihiyona. Ya auna da igiyar awo bai fasa hallaka ta ba. Ya sa katanga da katanga duk suka lalace.
9 Her gates are sunke to the grounde: he hath destroyed and broken her barres: her King and her princes are among the Gentiles: the Lawe is no more, neither can her Prophets receiue any vision from the Lord.
Ƙofofinta sun nutse a cikin ƙasa; ya kakkarya ƙarafanta. Sarakunanta da’ya’yan sarakunanta duk an kai su bauta cikin waɗansu ƙasashe, babu sauran doka, annabawa kuma ba su samun wahayi daga wurin Ubangiji.
10 The Elders of the daughter of Zion sit vpon the grounde, and keepe silence: they haue cast vp dust vpon their heades: they haue girded them selues with sackecloth: the virgines of Ierusalem hang downe their heades to the ground.
Dattawan Diyar Sihiyona sun zauna shiru a ƙasa; suka kuma sa rigar buhu.’Yan matan Urushalima suka sunkuyar da kawunansu ƙasa.
11 Mine eyes doe saile with teares: my bowels swell: my liuer is powred vpon the earth, for the destruction of the daughter of my people, because the children and sucklings swoone in the streetes of the citie.
Idanuna sun dushe don yawan kuka, raina na cike da baƙin ciki; zuciyata ta karaya domin mutanena sun hallaka, domin yara da jarirai suna suma a kan hanyoyi a cikin birni.
12 They haue sayd to their mothers, Where is bread and drinke? when they swooned as the wounded in the streetes of the citie, and whe they gaue vp the ghost in their mothers bosome.
Suna ce wa uwayensu, “Ina burodi da ruwan inabi?” Yayinda suke suma kamar mutanen da aka ji masu ciwo a cikin birni, sa’ad da suke mutuwa a hannuwan uwayensu.
13 What thing shall I take to witnesse for thee? what thing shall I compare to thee, O daughter Ierusalem? what shall I liken to thee, that I may comfort thee, O virgine daughter Zion? for thy breach is great like ye sea: who can heale thee?
Me zan ce miki? Da me zan kwatanta ki, ke Diyar Urushalima? Da me zan misalta ki, yadda zan iya yi miki ta’aziyya, Ke Budurwa Diyar Sihiyona? Ciwonki yana da zurfi kamar teku. Wane ne zai iya warkar da ke?
14 Thy Prophets haue looked out vayne, and foolish things for thee, and they haue not discouered thine iniquitie, to turne away thy captiuitie, but haue looked out for thee false prophesies, and causes of banishment.
Wahayin annabawanki ƙarya ne kuma marasa amfani; ba su tona zunubanki ba yadda za su iya ceto ki daga bauta ba. Sun yi miki annabcin ƙarya marar amfani.
15 All that passe by the way, clap their hands at thee: they hisse and wagge their head vpon the daughter Ierusalem, saying, Is this the citie that men call, The perfection of beautie, and the ioye of the whole earth?
Duk masu wucewa suna yi miki tafi na reni; suna yi wa Diyar Urushalima tsaki suna kaɗa kai suna cewa, “Wannan ne birnin da aka ce kyakkyawa ne, mai farantawa dukan duniya rai?”
16 All thine enemies haue opened their mouth against thee: they hisse and gnashe the teeth, saying, Let vs deuoure it: certainely this is the day that we looked for: we haue founde and seene it.
Maƙiyanki duka suna ta surutu game da ke; suna tsaki suna cizon haƙora suna cewa, “Mun hallaka ta. Wannan ce ranar da muke jira; yau mun gan ta.”
17 The Lord hath done that which he had purposed: he hath fulfilled his worde that he had determined of old time: he hath throwen downe, and not spared: hee hath caused thine enemie to reioyce ouer thee, and set vp the horne of thine aduersaries.
Ubangiji ya yi abin da ya shirya; ya cika maganarsa, wadda ya umarta tun daɗewa. Ya jefar da ke ba tausayi, ya bari maƙiya sun yi nasara da ke, ya ɗaukaka ƙahon maƙiyanki.
18 Their heart cryed vnto the Lord, O wall of the daughter Zion, let teares runne downe like a riuer, day and night: take thee no rest, neither let the apple of thine eye cease.
Zuciyar mutane ta yi kuka ga Ubangiji. Ya bangon Diyar Urushalima, bar hawayenki su zuba kamar rafi dare da rana; kada ki huta, kada idanunki su huta.
19 Arise, cry in the night: in the beginning of the watches powre out thine heart like water before the face of the Lord: lift vp thine handes towarde him for the life of thy yong children, that faint for hunger in the corners of all the streetes.
Ki tashi, ki yi kuka cikin dare, dare na yi sai ki fara kuka; kina buɗewa Ubangiji zuciyarki. Ki ɗaga hannuwanki gare shi domin rayukan’ya’yanki, waɗanda suka suma don yunwa a kan kowane titi.
20 Beholde, O Lord, and consider to whome thou hast done thus: shall the women eate their fruite, and children of a spanne long? shall the Priest and the Prophet be slaine in the Sanctuarie of the Lord?
“Ka duba, ka gani ya Ubangiji. Wane ne ka taɓa yi wa haka? Ko ya kamata uwaye su ci’ya’yansu,’ya’yan da suka yi reno? Ko ya kamata a kashe firistoci da annabawa a cikin haikalin Ubangiji?
21 The yong and the olde lie on the ground in the streetes: my virgins and my yong men are fallen by the sworde: thou hast slaine them in the day of thy wrath: thou hast killed and not spared.
“Matasa da tsofaffi duk suna kwanciya a cikin ƙurar tituna; an karkashe matasa da’yan matana da takobi. Ka kashe su a ranar fushinka; ka kashe su ba tausayi.
22 Thou hast called as in a solemne daye my terrours rounde about, so that in the day of the Lordes wrath none escaped nor remained: those that I haue nourished and brought vp, hath mine enemie consumed.
“Kamar yadda kake yin gayyata a ranar biki, haka kake kawo mini tsoro a kowane gefe. A ranar fushin Ubangiji ba mai tserewa ba wanda zai tsira; maƙiyina ya kashe waɗanda na yi renonsu, na kuma lura da su.”

< Lamentations 2 >