< Judges 8 >

1 Then the men of Ephraim sayde vnto him, Why hast thou serued vs thus that thou calledst vs not, when thou wentest to fight with the Midianites? and they chode with him sharply.
To, mutanen Efraim suka ce wa Gideyon, “Me ya sa ka yi mana haka? Me ya sa ba ka kira mu lokacin da ka tafi yaƙi da Midiyawa ba?” Suka zarge shi sosai.
2 To whom he said, What haue I now done in comparison of you? is not the gleaning of grapes of Ephraim better, then the vintage of Abiezer?
Amma ya ce musu, “Me na yi da za a iya kwatanta da abin da kuka yi? Ashe, kalar inabin da Efraim ta yi bai fi dukan girbin inabin da Abiyezer suka yi ba?
3 God hath deliuered into your handes the princes of Midian, Oreb and Zeeb: and what was I able to do in comparison of you? and when he had thus spoken, then their spirits abated toward him.
Allah ya ba da Oreb da Zeyib, shugabannin Midiyawa a hannuwanku. Me na yi da ya fi naku? Da ya faɗi haka sai hankalinsu ya kwanta.”
4 And Gideon came to Iorden to passe ouer, hee, and the three hundreth men that were with him, weary, yet pursuing them.
Gideyon da mutanensa ɗari uku, sun gaji, duk da haka suka yi ta fafarar, suka zo Urdun suka haye shi.
5 And he said vnto the men of Succoth, Giue, I pray you, morsels of bread vnto the people that follow me (for they be wearie) that I may follow after Zebah, and Zalmunna Kings of Midian.
Ya ce wa mutanen Sukkot, “Ku ba wa mutanena burodi; sun gaji, har yanzu ina fafarar Zeba da Zalmunna, sarakunan Midiyawa.”
6 And the princes of Succoth sayde, Are the handes of Zebah and Zalmunna nowe in thine hads, that we should giue bread vnto thine army?
Amma shugabannin Sukkot suka ce, “Ka kama Zeba da Zalmunna ko ne? Don me za mu ba wa mayaƙanka burodi?”
7 Gideon then sayde, Therefore when the Lord hath deliuered Zebah and Zalmunna into mine hand, I will teare your flesh with thornes of the wildernes and with breers.
Sai Gideyon ya ce, “Haka ko? To, sa’ad da Ubangiji ya ba da Zeba da Zalmunna a hannuna, zan tsattsaga jikinku da ƙayayyuwan jeji.”
8 And he went vp thence to Penuel, and spake vnto them likewise, and the men of Penuel answered him, as the men of Succoth answered.
Daga nan ya wuce zuwa Fenuwel ya yi irin roƙon nan, amma suka amsa yadda mutanen Sukkot suka yi.
9 And he sayd also vnto the men of Penuel, When I come againe in peace, I will breake downe this towre.
Saboda haka sai ya ce wa mutanen Fenuwel, “Sa’ad da na dawo da nasara zan rushe wannan hasumiya.”
10 Now Zebah and Zalmunna were in Karkor, and their hostes with them, about fifteene thousande, all that were left of all the hostes of them of the East: for there was slaine an hundreth and twentie thousand men, that drew swordes.
To, Zeba da Zalmunna suna a Karkor da mayaƙa wajen dubu goma sha biyar, abin da ya rage ke nan na mayaƙan gabashi; mayaƙa masu takobi dubu ɗari da ashirin ne suka mutu.
11 And Gideon went through them that dwelt in Tabernacles on the East side of Nobah and Iogbehah, and smote the hoste: for the hoste was carelesse.
Gideyon ya haura ta hanyar makiyaya, gabas da Noba, da kuma Yogbeha, ya fāɗa wa mayaƙan ta yadda ba su zata ba.
12 And when Zebah and Zalmunna fled, hee followed after them, and tooke the two kings of Midian, Zebah and Zalmunna, and discomfited all the hoste.
Zeba da Zalmunna, sarakunan biyu na Midiyawa suka tsere, amma ya bi su ya kama, ya fatattaki dukan mayaƙansu.
13 So Gideon the sonne of Ioash returned from battel, the sunne being yet hie,
Sa’an nan Gideyon ɗan Yowash ya komo daga yaƙi ta Hanyar Heres.
14 And tooke a seruant of the me of Succoth, and inquired of him: and he wrote to him the princes of Succoth and the Elders thereof, euen seuentie and seuen men.
Ya kama wani saurayin Sukkot ya tambaye shi, saurayin kuwa ya rubuta masa dukan sunayen shugabanni saba’in da bakwai na Sukkot, da dattawan garin.
15 And he came vnto the men of Succoth, and sayd, Behold Zebah and Zalmunna, by whome ye vpbrayded me, saying, Are the hands of Zebah and Zalmunna already in thine hands, that we should giue bread vnto thy weary men?
Sa’an nan Gideyon ya zo ya ce wa mutanen Sukkot, “To, ga Zeba da Zalmunna, waɗanda kuka yi mini ba’a kuna cewa, ‘Ka kama Zeba da Zalmunna ko ne? Me zai sa mu ba mutanenka da suka gaji burodi?’”
16 Then he tooke the Elders of the citie, and thornes of the wildernes and breers, and did teare the men of Succoth with them.
Ya kwashe dattawan garin ya koya wa mutanen Sukkot hankali ta wurin hukunta su da ƙayayyuwan hamada.
17 Also he brake downe the towre of Penuel, and slew the men of the citie.
Ya rushe hasumiyar Fenuwel ya kuma karkashe mutanen garin.
18 Then saide he vnto Zebah and Zalmunna, What maner of men were they, whom ye slew at Tabor? and they answered, As thou art, so were they: euery one was like the children of a King.
Sa’an nan ya ce wa Zeba da Zalmunna, “Waɗanne irin mutane ne kuka karkashe a Tabor.” Suka ce, “Mutane kamar ka ne kowane kamar ɗan sarki.”
19 And he said, They were my brethren, euen my mothers children: as the Lord liueth, if ye had saued their liues, I would not slay you.
Gideyon ya ce, “Waɗannan’yan’uwana ne,’ya’yan mahaifiyata. Muddin Ubangiji yana a raye, da a ce kun bar su da rai, da ba zan kashe ku ba.”
20 Then he sayde vnto Iether his first borne sonne, Vp, and slay them: but the boy drew not his sword: for he feared, because he was yet yong.
Da ya juya wajen Yeter, ɗan farinsa, sai ya ce, “Ka kashe su!” Amma Yeter bai zāre takobinsa ba, domin shi yaro ne kawai kuma yana tsoro.
21 Then Zebah and Zalmunna sayd, Rise thou, and fall vpon vs: for as the man is, so is his strength. And Gideon arose and slew Zebah and Zalmunna, and tooke away the ornamentes, that were on their camels neckes.
Zeba da Zalmunna suka ce masa, “Zo, ka yi da kanka. ‘Yadda mutum yake haka ƙarfinsa.’” Ta haka Gideyon ya matso gaba ya kashe su, ya ɗauki kayan ado daga wuyar raƙumansu.
22 Then the men of Israel sayd vnto Gideon, Reigne thou ouer vs, both thou, and thy sonne, and thy sonnes sonne: for thou hast deliuered vs out of the hand of Midian.
Isra’ilawa suka ce wa Gideyon, “Ka yi mulkinmu, kai, ɗanka da jikanka, domin ka cece mu daga hannun Midiyawa.”
23 And Gideon sayde vnto them, I will not reigne ouer you, neither shall my childe reigne ouer you, but the Lord shall reigne ouer you.
Amma Gideyon ya ce musu, “Ni, ko ɗana, ba za mu yi mulkinku ba. Ubangiji ne zai yi mulkinku.”
24 Againe Gideon sayd vnto them, I would desire a request of you, that you would giue mee euery man the earings of his pray (for they had golden earings because they were Ismaelites)
Kuma ya ce, “Ina da roƙo guda ɗaya, cewa kowannenku ya ba ni’yan kunne daga rabon ganima.” (Al’adar mutanen Ishmayel ce su sa’yan kunnen zinariya.)
25 And they answered, Wee will giue them. And they spred a garment, and did cast therein euery man the earings of his pray.
Suka ce, “Za mu yi farin cikin ba ka su.” Saboda haka suka shimfiɗa mayafi, kowanne ya sa ɗan kunne ɗaya daga ganimar.
26 And the weight of the golden earings that he required, was a thousande and seuen hundreth shekels of golde, beside collers and iewels, and purple rayment that was on the kings of Midian, and beside the cheynes that were about their camels neckes.
Nauyin’yan kunnen zinariyar ya kai shekel ɗari goma sha bakwai, ban da kayan ado, abin wuya da tufafin shunayya waɗanda sarakuna Midiyawa suke sawa ko sarƙoƙin da suke wuyar raƙumansu.
27 And Gideon made an Ephod thereof, and put it in Ophrah his citie: and all Israel went a whoring there after it, which was the destruction of Gideon and his house.
Gideyon ya efod da zinariyar, wanda ya ajiye a Ofra, garinsa. Dukan Isra’ila suka shiga yin karuwanci ta wurin yin sujada a can, ya kuwa zama wa Gideyon da dukan iyalinsa tarko.
28 Thus was Midian brought lowe before the children of Israel, so that they lift vp their heads no more: and the countrey was in quietnes fourtie yeeres in the dayes of Gideon.
Da haka Isra’ilawa suka mallaki Midiyawa ba su kuma sāke tā da kai ba. A zamanin Gideyon ƙasar ta sami zaman lafiya har shekara arba’in.
29 Then Ierubbaal the sonne of Ioash went, and dwelt in his owne house.
Yerub-Ba’al ɗan Yowash ya koma gida don yă zauna.
30 And Gideon had seuentie sonnes begotten of his body: for he had many wiues.
Yana da’ya’ya saba’in maza da ya haifa, gama yana da mata da yawa.
31 And his concubine that was in Shechem, bare him a sonne also, whose name he called Abimelech.
Yana kuma da ƙwarƙwara wadda take Shekem, ita ma ta haifa masa ɗa wanda ya ba shi suna Abimelek.
32 So Gideon the sonne of Ioash dyed in a good age, and was buried in the sepulchre of Ioash his father in Ophrah, of the father of ye Ezrites.
Gideyon ɗan Yowash ya rasu da kyakkyawan tsufa aka kuma binne shi a kabarin Yowash mahaifinsa a Ofra na mutanen Abiyezer.
33 But when Gideon was dead, the children of Israel turned away and went a whoring after Baalim, and made Baal-berith their God.
Ba a daɗe da rasuwar Gideyon ba, sai Isra’ila ta sāke shiga karuwanci suna bauta wa Ba’al. Suka kafa Ba’al-Berit yă zama musu allahnsu ba kuma
34 And the children of Israel remembred not the Lord their God, which had deliuered the out of the hands of all their enemies on euery side.
tuna da Ubangiji Allahnsu, wanda ya cece su daga hannuwan abokan gābansu a kowane gefe ba.
35 Neither shewed they mercy on the house of Ierubbaal, or Gideon, according to al the goodnesse which he had shewed vnto Israel.
Suka kāsa nuna alheri ga gidan Yerub-Ba’al (wato, Gideyon) saboda abubuwa masu alherin da ya yi musu.

< Judges 8 >