< Joshua 18 >

1 And the whole Congregation of the children of Israel, came together at Shiloh: for they set vp the Tabernacle of the Congregation there, after the land was subiect vnto them.
Isra’ilawa duka suka taru a Shilo suka kafa tenti inda za su dinga taruwa. Yanzu ƙasar tana ƙarƙashin mulkinsu,
2 Nowe there remained among the children of Israel seuen tribes, to whom they had not deuided their inheritance.
amma akwai sauran kabilu bakwai na Isra’ila waɗanda ba su samu rabon gādonsu ba tukuna.
3 Therefore Ioshua said vnto the children of Israel, Howe long are ye so slacke to enter and possesse the land which the Lord God of your fathers hath giuen you?
Saboda haka Yoshuwa ya ce wa Isra’ilawa, “Har yaushe za ku yi jinkirin shiga, ku mallaki ƙasar da Ubangiji Allah na iyayenku ya ba ku?
4 Giue from among you for euery tribe three men, that I may sende them, and that they may rise, and walke through the land, and distribute it according to their inheritance, and returne to me.
Ku ba da mutum uku daga kowace kabila, ni kuwa in aike su, su zagaya dukan ƙasar su rubuta bayani game da ita, bisa ga yadda za a raba ta gādo ga kowace kabila, sa’an nan su dawo wurina.
5 And that they may deuide it vnto them into seuen parts, (Iudah shall abide in his coast at the South, and the house of Ioseph shall stand in their coastes at the North)
Za ku raba ƙasar kashi bakwai. Mutanen Yahuda za su ci gaba da kasancewa a wurin da suke a kudu, sai kuma mutanen Yusuf a wurin da suke a arewa.
6 Ye shall describe the land therefore into seuen partes, and shall bring them hither to me, and I will cast lottes for you here before the Lord our God.
Bayan kun auna ƙasar, ku raba ta kashi bakwai, sai ku kawo mini taswirar ƙasar. Ni kuma in yi muku ƙuri’a a gaban Ubangiji Allahnmu.
7 But the Leuites shall haue no part among you: for the Priesthood of the Lord is their inheritance: also Gad and Reuben and halfe the tribe of Manasseh haue receiued their inheritance beyond Iorden Eastward, which Moses the seruant of the Lord gaue them.
Lawiyawa ba su da rabo a cikinku, domin aikin firistocin da suke yi wa Ubangiji shi ne gādonsu. Gad, Ruben da rabin kabilar Manasse kuwa sun riga sun samu gādonsu a gabashin gefen Urdun, Musa bawan Ubangiji ya ba su.”
8 Then the men arose, and went their way: and Ioshua charged them that went to describe the land, saying, Depart, and goe through the land, and describe it, and returne to me, that I may here cast lottes for you before the Lord in Shiloh.
Da mutanen za su kama hanya su je su zāna yadda ƙasar take, Yoshuwa ya umarce su cewa, “Ku je ku ga yadda ƙasar take. Sa’an nan ku dawo wurina, zan yi muku ƙuri’a a nan Shilo a gaban Ubangiji.”
9 So the men departed, and passed through the lande, and described it by cities into seuen partes in a booke, and returned to Ioshua into the campe at Shiloh.
Mutanen kuwa suka tafi suka bi ta cikin ƙasar, suka bayyana yadda take a rubuce, gari-gari, kashi bakwai, suka koma wurin Yoshuwa a Shilo.
10 Then Ioshua cast lottes for them in Shiloh before the Lord, and there Ioshua deuided the land vnto the children of Israel, according to their portions:
Sai Yoshuwa ya yi musu ƙuri’a a gaban Ubangiji, a nan ne ya raba wa Isra’ilawa ƙasar bisa ga yadda aka raba su kabila-kabila.
11 And the lot of the tribe of the children of Beniamin came foorth according to their families, and the cost of their lot lay betweene the children of Iudah, and the children of Ioseph.
Ƙuri’ar kabilar Benyamin bisa ga iyalansu. Rabonsu ya kama daga ƙasar da take tsakanin kabilar Yahuda da ta Yusuf.
12 And their coast on the Northside was from Iorden, and the border went vp to the side of Iericho on the Northpart, and went vp through the mountaines Westward, and the endes thereof are in the wildernesse of Beth-auen:
Daga gefen arewa, iyakarsu ta kama ne daga Urdun, ta wuce arewa a gangaren Yeriko, ta nufi yamma cikin ƙasar kan tudu, ta fito a jejin Bet-Awen.
13 And this border goeth along from thence to Luz, euen to the Southside of Luz (the same is Beth-el) and this border descendeth to Atroth-addar, neere the mount, that lyeth on the Southside of Beth-horon the nether.
Daga can ta ƙetare zuwa gangaren Luz a kudu (wato, Betel), ta wuce zuwa Atarot Adda a tudun arewa na kwarin Bet-Horon.
14 So the border turneth, and compasseth the corner of the Sea Southward, from the mount that lyeth before Beth-horon Southward: and the endes thereof are at Kiriath-baal (which is Kiriath-iearim) a citie of the children of Iudah: this is the Westquarter.
Daga tudun da yake fuskantar Bet-Horon a kudu, iyakar ta juya kudu ta gefen yamma ta ɓullo a Kiriyat Ba’al (wato, Kiriyat Yeyarim), birnin Yahuda. Wannan ita ce iyakar a wajen yamma.
15 And the Southquarter is from the ende of Kiriath-iearim, and this border goeth out Westward, and commeth to the fountaine of waters of Nephtoah.
A gefen kudu kuwa, iyakar ta fara daga ƙauyukan Kiriyat Yeyarim wajen yamma sai ta miƙe zuwa maɓuɓɓugar ruwan Neftowa.
16 And this border descendeth at the ende of the mountaine, that lyeth before the valley of Ben-hinnom, which is in the valley of the gyants Northward, and descendeth into the valley of Hinnom by the side of Iebusi Southwarde, and goeth downe to En-rogel,
Iyakar ta gangara zuwa gefen dutsen da yake fuskantar Kwarin Ben Hinnom, wanda yake arewa da Kwarin Refayim. Ta ci gaba ta gangara ta Kwarin Hinnom ta yi kudu kusa da birnin Yebusiyawa har zuwa En Rogel.
17 And compasseth from the North, and goeth foorth to En-shemesh, and stretcheth to Geliloth, which is toward the going vp vnto Adummim, and goeth downe to the stone of Bohan the sonne of Reuben.
Sai ta nausa ta yi wajen arewa, zuwa En Shemesh, ta ci gaba zuwa Gelilot, wanda yake fuskantar hawan Adummim. Daga can ta gangara zuwa Dutsen Bohan, ɗan Ruben.
18 So it goeth along to the side ouer against the plaine Northward, and goeth downe into the plaine.
Sai ta wuce ta yi arewancin gangaren Bet-Araba, ta wuce har zuwa cikin Araba.
19 After, this border goeth along to the side of Beth-hoglah Northward: and the endes thereof, that is, of the border, reach to the point of the salt Sea Northward, and to the ende of Iorden Southward: this is the Southcoast.
Sa’an nan ta wuce zuwa arewancin gangaren Bet-Hogla ta kuma ɓulla a arewancin gaɓar Tekun Gishiri, a bakin Urdun a kudu. Wannan ita ce iyakar a wajen kudu.
20 Also Iorden is the border of it on the Eastside: this is the inheritance of the children of Beniamin by the coastes thereof rounde about according to their families.
Urdun shi ne iyaka a wajen gabas. Waɗannan su ne iyakokin yankin ƙasar da iyalan kabilar Benyamin suka gāda.
21 Nowe the cities of the tribe of the children of Beniamin according to their families, are Iericho, and Beth-hoglah, and the valley of Keziz,
Waɗannan su ne garuruwan da kabilar Benyamin suke da su na gādo. Yeriko, Bet-Hogla, Emek Keziz,
22 And Beth-arabah, and Zemaraim, and Beth-el,
Bet-Araba, Zemarayim, Betel,
23 And Auim, and Parah, and Ophrah,
Awwim, Fara, Ofra,
24 And Chephar, Ammonai, and Ophni, and Gaba: twelue cities with their villages.
Kefar Ammoni, Ofni da Geba, garuruwa goma sha biyu ke nan da ƙauyukansu.
25 Gibeon, and Ramah, and Beeroth,
Akwai kuma Gibeyon, Rama, Beyerot,
26 And Mizpeh, and Chephirah, and Mozah,
Mizfa Kefira, Moza,
27 And Rekem, and Irpeel, and Taralah,
Rekem, Irfeyel, Tarala,
28 And Zela, Eleph, and Iebusi, (which is Ierusalem) Gibeath, and Kiriath: fourteene cities with their villages: this is the inheritance of the children of Beniamin according to their families.
Zela, Hayelef, birnin Yebusiyawa (wato, Urushalima), Gibeya da Kiriyat, garuruwa goma sha huɗu ke nan da ƙauyukansu. Wannan shi ne rabon gādon kabilar Benyamin bisa ga iyalansu.

< Joshua 18 >