< Joshua 16 >

1 And the lot fell to the children of Ioseph from Iorden by Iericho vnto the water of Iericho Eastward, and to the wildernes that goeth vp from Iericho by the mount Beth-el:
Rabon da aka ba wa Yusuf ya fara tun daga Urdun kusa da Yeriko, gabas da ruwan Yeriko, sai ya miƙe zuwa jeji, ya haura har zuwa cikin ƙasar tudu na Betel.
2 And goeth out from Beth-el to Luz, and runneth along vnto the borders of Archiataroth,
Ya ci gaba daga Betel (wato, Luz), ya zarce zuwa sashen Arkitawa na Atarot,
3 And goeth down Westward to the coast of Iaphleti, vnto the coast of Beth-horon the nether, and to Gezer: and the endes thereof are at the Sea.
ya sauka zuwa yammancin bakin iyakar Yalfetiyawa har zuwa yankin Bet-Horon wanda yake cikin kwari. Ya zarce kuma zuwa Gezer, ya gangara ya yi ƙarshe a Bahar Rum.
4 So the children of Ioseph, Manasseh and Ephraim tooke their inheritance.
Wannan ne yankin da aka ba wa Manasse da Efraim zuriyar Yusuf gādonsu.
5 Also the borders of the children of Ephraim according to their families, euen the borders of their inheritance on the Eastside were Atroth-addar, vnto Beth-horon the vpper.
Yankin Efraim ke nan bisa ga iyalansu. Iyakar ƙasarsu ta gādo ta kama daga Atarot Addar a gabas zuwa Bet-Horon,
6 And this border goeth out to the Sea vnto Michmethah on the Northside, and this border returneth Eastward vnto Taanathshiloh, and passeth it on the Eastside vnto Ianohah,
ta wuce zuwa Bahar Rum. Daga Mikmetat a arewa kuwa iyakar ta karkata gabas zuwa Ta’anat Shilo, ta wuce zuwa Yanowa a gabas.
7 And goeth downe from Ianohah to Ataroth, and Naarath, and commeth to Iericho, and goeth out at Iorden.
Sai ta gangara daga Yanowa zuwa Atarot da Na’ara, ta bi ta Yeriko, ta kuma fito ta Urdun.
8 And this border goeth from Tappuah Westward vnto the riuer Kanah, and the endes thereof are at the Sea: this is the inheritance of the tribe of the children of Ephraim by their families.
Daga Taffuwa kuma iyakar ta bi yamma zuwa kwazazzaban Kana, ta ƙarasa a Bahar Rum. Wannan shi ne gādon mutanen Efraim bisa ga iyalansu.
9 And the separate cities for the children of Ephraim were among the inheritance of the children of Manasseh: all the cities with their villages.
Gādon ya kuma haɗa da dukan garuruwa da ƙauyuka waɗanda aka keɓe wa mutanen Efraim daga cikin gādon mutanen Manasse.
10 And they cast not out the Canaanite that dwelt in Gezer, but the Canaanite dwelt among the Ephraimites vnto this day, and serued vnder tribute.
Ba su kori Kan’aniyawan da suke zama a Gezer ba, don haka Kan’aniyawa suna zama tare da mutanen Efraim har wa yau; amma Kan’aniyawa suka zama masu yin aikin dole.

< Joshua 16 >